Ameer Media NG

Ameer Media NG Graphics Designer, Video Editor,Data Services, Data card, Internet Services, Cable TV Subscription

Shugaban Hukumar Kiyaye Afkuwar Zaizayar Ƙasa da Ambaliyar Ruwa ta Kano Dr. Muhammad S. Khalil ya kai ziyara unguwar Gur...
27/10/2023

Shugaban Hukumar Kiyaye Afkuwar Zaizayar Ƙasa da Ambaliyar Ruwa ta Kano Dr. Muhammad S. Khalil ya kai ziyara unguwar Gurin Gawa inda ake fuskantar barazanar Zaizayar ƙasa.

Khalil ya ce, sun kai wannan ziyarar nan bayan ganin hotunan halin da yankin yake ciki a shafin gidan Rediyon Freedom.

Ya sha alwashin ɗaukar matakin da ya dace.

📷 Freedom Radio Nigeria

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu cikin Daren nan ya sauka a Abuja bayan halartar taron Majalisar Dinkin Duniya na farko a...
29/09/2023

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu cikin Daren nan ya sauka a Abuja bayan halartar taron Majalisar Dinkin Duniya na farko a birnin New York.

Rundunar Sojojin Jamhuriyar Nijar Ta Yanke Alakar Soji Da Kasar Benin Yayin da Jamhuriyar Nijar ke kara shiga matsi daga...
13/09/2023

Rundunar Sojojin Jamhuriyar Nijar Ta Yanke Alakar Soji Da Kasar Benin

Yayin da Jamhuriyar Nijar ke kara shiga matsi daga kasashe, ta fara daukar matakai kan wasu kasashe makwabtanta Sojojin Nijar sun sanar da yanke alakar soji tsakaninsu da Jamhuriyar Benin ganin yadda ta shirya taimakawa kungiyar ECOWAS Wannan na zuwa ne bayan juyin mulki a kasar da sojin su ka kifar da Mohamed Bazoum a ranar 26 ga watan Yulin wannan shekara
Sojojin sun sanar da haka ne a talabijin na kasar a daren jiya Talata 12 ga watan Satumba na yanke alakar da makwabciyarta Benin.

✍️ Abdulganiyyu Sh*tu

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufai  ya saki sabon hotonsa, inda ya bayyana cewa, yana more rayuwarsa a binrin “B...
15/08/2023

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya saki sabon hotonsa, inda ya bayyana cewa, yana more rayuwarsa a binrin “Beirut” dake ƙasar Lebanon.

Abdulganiyyu Sh*tu

Yanzu haka manyan Motoci makare da kaya suna tsaye a bakin Boda a karamar hukumar Jibia da ke kan iyakar Najeriya da Nij...
05/08/2023

Yanzu haka manyan Motoci makare da kaya suna tsaye a bakin Boda a karamar hukumar Jibia da ke kan iyakar Najeriya da Nijar. Wau motocin za su shiga Nijar wasu kuma daga Nijar za su shigo Najeriya.

Kowace Mota da irin kayan da ta dauko, na abunda Gwamnati ta yadda a shigo dashi da kuma abunda ta yadda a fitar dashi. Sakamakon rufe Bododin kasar kowace Mota ta tsaya chak babu shiga babu fita.

Abdulganiyyu Sh*tu

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta a Najeriya (INEC) ta shigar da tuhume-tuhume shida a gaban kotu, kan dakataccen kwamishinan...
06/07/2023

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta a Najeriya (INEC) ta shigar da tuhume-tuhume shida a gaban kotu, kan dakataccen kwamishinan zabe na jihar Adamawa, Hudu Yunusa-Ari.

BBC Hausa ta ruwaito cewa Cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar mai dauke da sahanun shugaban sashen wayar da kan al'umma na hukumar, Festus Okoye, ta ce an shigar da ƙarar ne a gaban babbar kotun jiha da ke Yola, a jihar Adamawa.

Gwamnan jihar Anambra, Farfesa Charles Soludo, ya tayar da hankulan jama’a kan wani shiri na kawo cikas ga yakin da gwam...
03/07/2023

Gwamnan jihar Anambra, Farfesa Charles Soludo, ya tayar da hankulan jama’a kan wani shiri na kawo cikas ga yakin da gwamnatinsa ke yi da rashin tsaro a jihar.

Ya zargi sansanin ‘yan adawar da cewa suna bayyana irin nasarorin da rundunar hadin gwiwa ta JTF ta samu a jihar a matsayin wani shiri na tinkarar ‘ya’yan kabilar Igbo ta hanyar kashe ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba.

falasdinawa shida sun mutu bayan farmakin da Isra'ila ta kai a sansanin 'yan gudun hijira na JeninAmjad Aref al-Jaas, ma...
20/06/2023

falasdinawa shida sun mutu bayan farmakin da Isra'ila ta kai a sansanin 'yan gudun hijira na Jenin

Amjad Aref al-Jaas, mai shekaru 48, shi ne Bafalasdine na shida da ya mutu sakamakon wani gagarumin farmaki da Isra'ila ta kai kan Jenin a ranar Litinin.

Jami’ar Tarayya Oye-Ekiti ta baiwa Professor Isa Ali Pantami  lambar yabo ta “Special Meritorious Service Award” wajen b...
17/04/2023

Jami’ar Tarayya Oye-Ekiti ta baiwa Professor Isa Ali Pantami lambar yabo ta “Special Meritorious Service Award” wajen bunkasa tattalin arzikin dijital. An ba da kyautar ne a lokacin bikin yaye dalibai na ƙarshe (convocation) na Jami'ar

A  ranar Alhamis 13 ga watan Afrilu Sheikh Ja'afar Mahmud Adam ke cika shekara 16 da rasuwa. An harbe fitaccen malamin a...
13/04/2023

A ranar Alhamis 13 ga watan Afrilu Sheikh Ja'afar Mahmud Adam ke cika shekara 16 da rasuwa.

An harbe fitaccen malamin addinin Musuluncin ne yayin da yake jagorantar sallar Asuba a masallaci a Kano ranar Juma'a, 13 ga watan Afrilun 2007.

BBC Hausa

11/04/2023

Address

No 23 University Of Jos Consultancy Plaza Bauchi Road Jos
Jos
8091100

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ameer Media NG posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category