30/07/2026
RAHOTON ZIYARAR BABBAN LIMAMIN MASALLACIN SULTAN BELLO KADUNA ZUWA GA SHEIKH ADAM MUHAMMAD GADAR SOGAI JOS
A ranar Lahadi da ta gabata, Hubusi Center da ke cikin garin Jos ya karɓi baƙo mai daraja, Babban Limamin Masallacin Sultan Bello da ke Kaduna, Dr. Muhammad Sulaiman Abu Sulaiman, wanda ya kai ziyarar girmamawa ga fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Adam Muhammad Gadar Sogai Jos.
Ziyarar ta gudana cikin yanayi na mutunta juna, ƙauna da haɗin kan malamai, inda aka tattauna muhimman batutuwan da s**a shafi ci gaban Da'awar Musulunci, haɗin kan al'umma, da kuma muhimmancin ƙarfafa zumunci tsakanin malamai da cibiyoyin ilimi.
A yayin ganawar, Dr. Muhammad Sulaiman Abu Sulaiman ya bayyana jin daɗinsa da irin ayyukan da Sheikh Adam Muhammad Gadar Sogai yake gudanarwa wajen koyar da Al-Qur'ani da Sunnah tare da tarbiyyantar da al'umma. Ya yi addu'ar Allah Madaukakin Sarki Ya ƙara masa lafiya, hikima da ƙarfin ci gaba da hidimar addini.
Shi ma Sheikh Adam Muhammad Gadar Sogai ya yi maraba da babban baƙon nasa, inda ya nuna godiyarsa bisa wannan ziyara ta alkhairi. Ya bayyana cewa irin wannan mu'amala tsakanin malamai tana ƙara haɗin kai, soyayya da fahimtar juna, tare da ƙarfafa aikin yaɗa addinin Musulunci.
An kammala ziyarar da addu'o'i na neman zaman lafiya ga ƙasa, haɗin kan al'ummar Musulmi, da kuma roƙon Allah Ya ci gaba da kare malamai, Ya albarkaci iliminsu da ayyukansu, Ya sanya wannan ziyara ta kasance sanadin ƙarin alheri ga al'ummar Musulmi baki ɗaya.
Allah Ya karɓi wannan ziyara da alheri, Ya ƙara haɗin kai tsakanin malamai, Ya kuma ba su ikon ci gaba da jagorantar al'umma bisa Al-Qur'ani da Sunnah da fahimtar magabata managarta .
Ameen summa Ameen
Rahoto:
Suraaj Abu khairiyyah Muhammad
Sec.Hubusi media jos