Daily News Hausa

Daily News Hausa Daily News Hausa, is a licensed Nigerian newspaper company dedicated to delivering verified news and entertainment content in the Hausa language."
(3)

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Aikin Gyaran Titin Mando–Birnin Gwari Kan Naira Biliyan 178.1Daga Aliyu SambaGwamnatin ...
04/08/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Aikin Gyaran Titin Mando–Birnin Gwari Kan Naira Biliyan 178.1

Daga Aliyu Samba

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da aikin sake gina Titin Mando zuwa Birnin Gwari mai tsawon kilomita 122.8 a Jihar Kaduna, wanda aka ware wa kuɗaɗen da s**a kai Naira biliyan 178.1. Titin ya tashi daga Mando da ke kusa da Filin Jirgin Sama na Kaduna zuwa iyakar Jihar Neja.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, wanda Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya wakilta wajen ƙaddamar da aikin a ranar Talata, ya ce aikin zai taimaka wajen inganta harkokin sufuri, ƙarfafa tsaro da kuma bunƙasa tattalin arzikin yankin. Ya ce t**in na daga cikin manyan ayyukan raya ƙasa da za su ƙara haɗa yankunan Arewacin Najeriya da Kudu maso Yammacin ƙasar, tare da sauƙaƙa zirga-zirgar mutane da kayayyaki.

Shugaban ya bayyana cewa aikin na cikin manyan ayyukan hanyoyin tarayya da gwamnatinsa ta amince da su a watan Mayun 2026 domin faɗaɗa ababen more rayuwa a faɗin ƙasar. Ya kuma tuna cewa tun lokacin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a shekarar 2022 ya yi alƙawarin sake gina t**in idan aka zaɓe shi, yana mai cewa fara aikin ya nuna yadda gwamnatinsa ke cika alƙawuran da ta ɗauka ga 'yan Najeriya.

Tinubu ya ce tsawon shekaru da dama Titin Birnin Gwari ya kasance cikin halin lalacewa sakamakon rashin kulawa da gyara yadda ya kamata. Ya ƙara da cewa gwamnatin tarayya ta ƙuduri aniyar kawo ƙarshen wannan matsala ta hanyar ci gaba da zuba jari a ayyukan hanyoyi, yana mai jaddada cewa matsayin Jihar Kaduna a matsayin ƙofar shiga yankin Arewa ya sa samar da ingantattun hanyoyi ya zama wajibi domin bunƙasa kasuwanci, zirga-zirga da ci gaban yankin.

Da yake jawabi, Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi, ya ce aikin ya nuna ƙudirin gwamnatin Shugaba Tinubu na samar da ababen more rayuwa da za su inganta rayuwar al'umma kai tsaye. Ya ce baya ga ƙarfafa tsaro a hanyar, aikin zai buɗe damar bunƙasa noma a yankin, wanda zai taimaka wajen ƙara samar da abinci da kuma yaƙi da yunwa.

Umahi ya kuma bayyana cewa sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatin Tinubu ta fara aiwatarwa suna ci gaba da haifar da sakamako mai kyau duk da ƙalubalen da gwamnatin ta gada a shekarar 2023. "Ta hanyar aiwatar da wannan aiki, Shugaban Ƙasa na cika alƙawarin da ya ɗauka ga al'umma, kuma hakan zai haifar da gagarumin sauyi a fannin noma a wannan yanki," in ji shi.

Tun da farko, Babban Sakataren Ma'aikatar Ayyuka ta Tarayya, Adeladan Rafiu Olarinre, ya ce aikin wani ɓangare ne na shirin gwamnatin tarayya na zamani da faɗaɗa hanyoyin Najeriya. Ya ce ana sa ran kammala aikin zai rage wahalar zirga-zirga, ya ƙara bunƙasa kasuwanci, tare da haɓaka tattalin arzikin Jihar Kaduna da jihohin da ke maƙwabtaka da ita.

Tinubu Ya Amince da Ƙarin Albashi Har Kashi 80 Ga Jami’an Sojin NajeriyaDaga Aliyu SambaShugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu...
04/08/2026

Tinubu Ya Amince da Ƙarin Albashi Har Kashi 80 Ga Jami’an Sojin Najeriya

Daga Aliyu Samba

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da ƙarin albashi ga jami’an Rundunar Sojin Najeriya da ya kai tsakanin kashi 30 zuwa 80 cikin ɗari, a wani mataki da gwamnatin tarayya ta ce na inganta jin daɗin jami’an tsaro da ƙarfafa musu gwiwa wajen gudanar da ayyukansu.

Sanarwar da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Talata ta bayyana cewa kimanin jami’ai da sojoji 250,000 ne za su amfana da sabon tsarin albashin, wanda zai fara aiki daga 1 ga Satumban 2026.

A cewar sanarwar, jami’an da ke daga mukamin Brigadier Janar zuwa Janar za su samu ƙarin albashi na kashi 30 cikin ɗari, yayin da jami’an daga mukamin Kanal zuwa Warrant Officer za su samu ƙarin kashi 50 cikin ɗari. Haka kuma, sojojin da ke daga mukamin Private zuwa Staff Sergeant za su amfana da ƙarin albashi mafi girma na kashi 80 cikin ɗari.

Sanarwar ta ƙara da cewa sabon tsarin zai ƙara yawan kuɗin da gwamnati ke kashewa kan albashin jami’an sojin daga Naira biliyan 660 zuwa Naira biliyan 924 a duk shekara.

Shugaba Tinubu ya ce gwamnatinsa na yaba wa jajircewa da sadaukarwar jami’an rundunar sojin wajen yaƙi da matsalolin tsaro da s**a haɗa da ta’addanci, garkuwa da mutane da kuma ayyukan ‘yan bindiga a wasu sassan ƙasar.

Ya ce, “Mazan da matan da ke tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyinmu sun cancanci a tallafa musu tare da nuna musu godiya saboda hidimar da suke yi wa ƙasa. Gwamnatinmu za ta ci gaba da ba da fifiko ga jin daɗin jami’an tsaro tare da samar musu da makamai da fasahohin zamani domin su gudanar da aikinsu yadda ya kamata.”

Shugaban ya kuma jaddada cewa babu wata ƙasa da za ta iya samun ci gaba mai ɗorewa ba tare da ingantaccen tsaro ba, yana mai tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen amfani da dukkan rundunonin tsaro domin kawar da barazanar tsaro da kare rayuka da dukiyoyin ‘yan Najeriya.

Tinubu ya kuma yi kira ga jami’an rundunar sojin da su ɗauki wannan ƙarin albashi a matsayin wata alamar godiya daga gwamnati bisa irin hidimar da suke yi wa ƙasa, yana mai bayyana ƙwarin gwiwar cewa Najeriya za ta yi nasara kan masu neman tada zaune tsaye da tarwatsa zaman lafiyar ƙasar.

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙara Ƙaimi Wajen Yaƙi da Rashin Tsaro, Ta Yaye Dakarun Forest Guards a Kaduna da Kogi Gwamnatocin J...
04/08/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙara Ƙaimi Wajen Yaƙi da Rashin Tsaro, Ta Yaye Dakarun Forest Guards a Kaduna da Kogi

Gwamnatocin Jihohin Kaduna da Kogi sun yaye sabbin dakarun Forest Guards domin kara karfafa yaki da 'yan ta'adda, masu garkuwa da mutane da sauran masu aikata laifuka da ke amfani da dazuka a matsayin maboya. Matakin na daga cikin kokarin gwamnatin tarayya da jihohi na inganta tsaro ta hanyar amfani da dabarun tattara bayanan sirri da kuma kare al'ummomi.

A Jihar Kaduna, Gwamna Sanata Uba Sani ya jagoranci bikin yaye dakaru sama da 1,000 da aka horas ta hadin gwiwar Ofishin Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro (ONSA) da Hukumar DSS. An zabo dakarun ne daga cikin jami'an Kaduna Vigilance Service (KADVS) guda 7,000, inda aka basu horo na musamman tare da tanadar musu manyan makamai domin kara musu karfin dakile ayyukan 'yan ta'adda a yankunan dazuka da sauran wuraren da ake fama da matsalar tsaro.

A daya bangaren kuma, Gwamnan Jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, ya yaye rukunin farko na dakarun Forest Guards guda 530 bayan kammala horo na makonni takwas. Ya ce sabuwar rundunar za ta yi aiki tare da sauran hukumomin tsaro wajen kare dazuka, tattara bayanan sirri da hana masu aikata laifuka samun mafaka a ko'ina cikin jihar.

Gwamnonin biyu sun yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Ofishin Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro da dukkan hukumomin tsaro bisa hadin kai da goyon bayan da s**a bayar wajen nasarar shirin. A Kaduna, jami'in ONSA ya bayyana cewa jihar ce ta farko da ta nemi gwamnatin tarayya ta horas da Forest Guards, tare da bayyana shirin horaswar a matsayin mafi nasara irinsa a Najeriya.

Masu sa ido kan harkokin tsaro na ganin cewa fadada rundunar Forest Guards wani muhimmin ci gaba ne a manufar gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta dakile ayyukan 'yan ta'adda da masu garkuwa da mutane ta hanyar hana su amfani da dazuka a matsayin maboyarsu. Ana kuma sa ran shirin zai kara tabbatar da zaman lafiya, tare da samar da ingantaccen yanayin da zai bunkasa noma, kasuwanci da sauran ayyukan raya kasa.

Takarar Shugaban Ƙasa Na So Sheik Pantami Ya Nema, Inji Halliru Bande, KontagoraBabba abinda nake kallo a wannan siyasa ...
04/08/2026

Takarar Shugaban Ƙasa Na So Sheik Pantami Ya Nema, Inji Halliru Bande, Kontagora

Babba abinda nake kallo a wannan siyasa ta Malam shine alherin dake cikinta ya fi sharrin ta yawa.

Ni ba Gwamna na so Malam ya nema ba, takarar ahugaban ƙasa na so ya nema saboda alherin dake cikin ta ya fi na neman gwamnan Gombe girma.

Tazarar Dake Tsakanin Shata Da Rarara, Kamar Misali Girman Al'arshi Ne Da Ķuma Girman Ķasa, Inji Farfesa Aliyu Ibrahim Ƙ...
04/08/2026

Tazarar Dake Tsakanin Shata Da Rarara, Kamar Misali Girman Al'arshi Ne Da Ķuma Girman Ķasa, Inji Farfesa Aliyu Ibrahim Ƙanƙara

Farfesa A Kankara ya bayyana hakan ne a taron KTFest 5.0, inda ya ƙara da cewa kwatanta babban mawaki Mamman Shata mai waƙoƙi dubu 10,000 da mawaƙi Dauda Kahutu Rarara mai waƙa 13 bai ma taso ba. Masanin ya ce binciken sa ya nuna Shata ne shugaban mawaƙa, shi kuma Rarara mawakin yabo ne na zamani.

Gwamna Uba Sani ya bai wa mijin marigayiya Malama Ummulkhairi kyautar gidaGwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bai wa miji...
04/08/2026

Gwamna Uba Sani ya bai wa mijin marigayiya Malama Ummulkhairi kyautar gida

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bai wa mijin marigayiya Malama Ummulkhairi, wadda aka kashe a Mararrabar Jos, kyautar gida.

An bayyana matakin a matsayin tallafi da nuna tausayi ga iyalan marigayiyar, musamman mijinta, bayan mummunan lamarin da ya faru.

DA ƊUMI-ƊUMI: Majalisar Dokokin Kano ta dakatar da shugabannin ƙananan hukumomi ukuMajalisar Dokokin Jihar Kano ta dakat...
04/08/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Majalisar Dokokin Kano ta dakatar da shugabannin ƙananan hukumomi uku

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta dakatar da shugabannin ƙananan hukumomin Bebeji, Rogo da Ɓagwai na tsawon watanni uku.

Matakin ya shafi shugabannin ƙananan hukumomin uku, yayin da ake jiran ƙarin bayani kan dalilan da s**a jawo dakatarwar.

DA DUMI-DUMI: Sakataren jam’iyyar ADC na Gombe ya fice daga jam'iyyar zuwa jam'iyyar PDP domin marawa Professor Isa Ali ...
04/08/2026

DA DUMI-DUMI: Sakataren jam’iyyar ADC na Gombe ya fice daga jam'iyyar zuwa jam'iyyar PDP domin marawa Professor Isa Ali Pantami baya a zaben 2027.

A daren jiya Litinin Sakataren jam’iyyar ADC na karamar hukumar Gombe Hon Babangida Usman (Babangida Ventures), ya sanar da ajiye mukaminshi na Sakataren jam’iyyar tare da ficewa daga jam'iyyar.

Hon Babangida Ventures yace, ya fice daga jam'iyyar ADC ne zuwa jam'iyyar PDP domin ya marawa Professor Isa Ali Pantami CON, PhD (Majidadin Daular Usmaniyya) baya a zaben 2027, kasancewar yafi kowane dan takara cancanta a jihar Gombe.

ROMON DIMOKRAƊIYYA: Matattakalar tsallaka t**i da wani ɗan siyasa ya yi wa al'umma a KanoWani ɗan siyasa a Kano ya yi wa...
04/08/2026

ROMON DIMOKRAƊIYYA: Matattakalar tsallaka t**i da wani ɗan siyasa ya yi wa al'umma a Kano

Wani ɗan siyasa a Kano ya yi wa al'umma matattakalar tsallaka t**i, abin da ya jawo cece-kuce da ra'ayoyi daban-daban daga jama'a.

Wani ya damfari ɗan bìndiga Kachallah Maha Naira miliyan 95Rahotanni sun bayyana cewa wani mutum ya damfari wani da ake ...
04/08/2026

Wani ya damfari ɗan bìndiga Kachallah Maha Naira miliyan 95

Rahotanni sun bayyana cewa wani mutum ya damfari wani da ake zargin shugaban ƙungiyar 'yan bìndiga, Kachallah Maha, da kuɗi har Naira miliyan 95, bayan ya yi masa alkawarin cewa zai samo masa makamai.

An ce mutumin ya karɓi kuɗin ne da sunan zai samar wa Kachallah Maha makamai, amma daga bisani ya gaza cika alkawarin da ya yi.

Address

Rwang Street
Jos
7979101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Daily News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Daily News Hausa:

Shortcuts

Share