11/04/2026
Tawagar ADC ƙarƙashin jagorancin Sanata David Mark ta gana da sabon shugaban jam’iyyar PRP na ƙasa, Hakeem Baba-Ahmed, kwanaki 48 kacal bayan wata irin wannan ganawa da s**a yi da wani ɓangare na jam’iyyar PDP ƙarƙashin jagorancin Tanimu Turaki.
Sai dai a wani muhimmin mataki, wata Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja ta sanya ranar Litinin domin yanke hukunci kan sahihancin kwamitin gudanarwa na ƙasa (NEC) na jam’iyyar ADC ƙarƙashin jagorancin David Mark.
Ɗan majalisar wakilai na jam’iyyar ADC, Leke Abejide mai wakiltar mazabar Yagba a jihar Kogi, shi ne ke ƙalubalantar shugabancin ɓangaren, inda yake neman kotu ta tsige David Mark da sauran mambobin kwamitin.
Ko da yake ba a bayyana cikakken bayanin ganawar ba, majiyoyi sun nuna cewa na da alaƙa da wani kira da shugaban PRP ya yi na haɗa kan ‘yan adawa domin kafa ƙarfi guda a fagen siyasa.
A cikin tawagar ADC da s**a halarci ganawar akwai mai magana da yawun jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, da Salihu Lukman, yayin da shugaban PRP tare da mai magana da yawunta Muhammed Ishaq s**a wakilci jam’iyyar.