02/09/2026
GIDAUNIYAR LAMIR TA SHIRYA GAGARUMIN SHIRIN DUBA LAFIYA DA TALLAFAWA MABUKATA A YELWA.
Gidauniyar Lamir ta sanar da gudanar da wani gagarumin shirin duba lafiya da tallafawa al’umma na tsawon kwanaki biyu, domin taimaka wa mutane masu karamin karfi da wadanda ke cikin mawuyacin hali.
Za a gudanar da shirin ne a ranakun 5 da 6 ga Satumbar, 2026, a Lalong Legacy Project, da ke kan titin Garkawa, Yelwa, Ƙaramar Hukumar Shendam ta Jihar Plateau.
Shirin dai wani bangare ne na bikin cikar Hon. Lamir Umar Ibrahim shekaru 40, kuma zai kunshi binciken lafiya da ba da magunguna kyauta, da kuma tallafa wa marasa karfi domin inganta rayuwarsu.
A yayin shirin, jama’a za su samu damar duba lafiyarsu ba tare da biyan wani kudi ba, yayin da wadanda ke cikin bukata za su samu tallafi da sauran abubuwan da aka tanada domin rage musu radadin matsalolin rayuwa.
Gidauniyar Lamir ta bayyana cewa wannan shiri na daga cikin kokarinta na inganta jin dadin al’umma, tallafa wa mabukata da kuma gina kyakkyawar makoma.
Ana kuma sa ran shirin zai samu halartar dimbin jama’a daga Yelwa da sauran sassan Ƙaramar Hukumar Shendam, musamman wadanda ake sa ran za su amfana da ayyukan jin kai na gidauniyar.
Gidauniyar ta yi kira ga al’ummar Yelwa da kewayenta da su yi amfani da wannan dama, domin amfana da ayyukan kiwon lafiya da tallafin da aka tanada.
✍️ DY Musa.