05/06/2026
Sarkin Argungu, Alhaji Muhammad Samaila Mera, ya buƙaci al’ummomin masarautarsa da su mallaki makamai bisa ka’ida domin kare kansu daga hare-haren ’yan bindiga da ke addabar yankin.
Sarkin ya kuma yi kira ga al’ummomin masarautar da su kasance cikin shiri tare da ɗaukar matakan kariya daga ’yan ta’adda da sauran masu aikata laifuka da ke kai hare-hare a yankunansu.
Ya bayyana hakan ne yayin wani taro da hakimai, masu unguwanni da shugabannin gundumomi da aka gudanar a fadarsa da ke Argungu, a cewar rahoton jaridar Daily Trust.
Alhaji Samaila Mera ya ce ya kamata al’umma su haɗa kai wajen tara kuɗaɗe domin sayen makaman da doka ta amince da su domin kare kansu.
A cewarsa, “Idan kuka mallaki irin waɗannan makamai bisa doka, ’yan bindiga zasu san cewa al’ummarku na da damar kare kanta. Wannan kaɗai na iya hana su kusantar yankin.”