Dandume Post

Dandume Post Domin Samun Labarai ku Kasance da jaridar baturiya Hausa

13/09/2025

Sakon Barka da Juma’a daga Sanata Muntari Mohammed Dandutse

A yau, ranar Juma’a mai albarka, ranar da ta fi kowace rana daraja a cikin mako, mai girma Sanata Muntari Mohammed Dandutse, dan majalisar dattawa mai wakiltar Katsina ta Kudu kuma shugaban kwamitin majalisar dattawa kan manyan makarantu da TETFund, ya taya al’ummar Musulmi murnar isowar wannan rana mai cike da rahama da falala.

Sanata Dandutse ya yi addu’a ga Allah Madaukakin Sarki da Ya kawo zaman lafiya a shiyyar Katsina ta Kudu da Najeriya baki ɗaya, Ya kare al’umma daga dukkan fitintinu, Ya karɓi ibadu da addu’o’i, tare da albarkar jagororinmu da shugabannin da ke ƙoƙarin kawo ci gaba da jin daɗin jama’a.

Ya ƙara da cewa Allah ya sa wannan Juma’ar ta kasance mafi alheri a cikin ranakunmu, ta zama kafa ta samun gafara, tsari da kusanci da Allah (SWT).”

Daga ƙarshe, Sanata Dandutse ya yi fatan alherin wannan Juma’a ya kasance tare da kowa da iyalansa, Barkanmu da Juma’a. ✍️ Sen. Dandutse Media Reporters

“Zamu Fito da Tsare tsare masu kyau da zasu Bunkasa Kasuwar waya ta karamar hukumar Dandume"  Inji Hon. Ashiru Umar Gaye...
13/07/2025

“Zamu Fito da Tsare tsare masu kyau da zasu Bunkasa Kasuwar waya ta karamar hukumar Dandume" Inji Hon. Ashiru Umar Gaye

Daya daga cikin fitattun ‘yan takarar shugabancin kungiyar masu sana’ar sayar da waya a karamar hukumar Dandume, wato Dandume Phone and Accessories Sellers Association (DAPAS), Hon. Ashiru Umar Gaye, ya bayyana cewa babban burinsa shi ne inganta kasuwanci, musamman ga matasa da kananan ‘yan kasuwa.

A wata tattaunawa da ya yi da manema labarai a Dandume, Hon. Ashiru Umar Gaye ya ce, idan ya samu nasarar lashe zaben shugabancin kungiyar, zai bullo da tsare-tsare na musamman da za su taimaka wajen bunkasa sana’o’in masu ƙaramin karfi, tare da samar musu da damammaki na ci gaba.

Burina shi ne bunƙasa kasuwar waya ta Dandume gaba ɗaya. Zamu fito da shirye-shirye na musamman da za su bai wa matasa da kananan ‘yan kasuwa damar faɗaɗa harkokinsu cikin gaskiya da rikon amana,” inji shi.

Manufofi da Tsare-tsaren Hon. Ashiru Umar Gaye ya bayyana wasu daga cikin muhimman abubuwan da yake da niyyar aiwatarwa idan aka ba shi damar jagorantar DAPAS:

1 Kare martabar kowane mamba na ƙungiya a ko’ina, musamman a cikin jihar Katsina.

2 Ƙarfafa dangantaka mai kyau tsakanin masu sayar da waya da abokan hulɗarsu, domin kasuwanci ya gudana cikin fahimta da jin daɗi.

3 Inganta tsarin warware sabani da rikice-rikice cikin gaskiya da adalci tsakanin abokan kasuwanci.

4 Ƙirƙiro hanyoyin tallafi ga kananan ‘yan kasuwa domin ƙarfafa su su zama masu gaskiya da nagarta a harkokinsu.

5 Inganta hanyoyin samun kudaden shiga na ƙungiya ba tare da takura wa mambobi ba.

Ya ce zai tabbatar da cewa, idan aka ba shi amanar shugabanci, DAPAS za ta zama abar koyi a fannin shugabanci da haɗin kai a fadin jihar.

Idan har aka bani amanar shugabanci, zan tabbatar da cewa wannan ƙungiya ta zama tubalin ci gaba a Dandume da ma jihar Katsina baki ɗaya,” inji Hon. Ashiru Umar.

Tuni dai zaben shugabancin ƙungiyar DAPAS ya ɗauki zafi a Dandume, inda ‘yan takara da dama ke ci gaba da bayyana manufofinsu. Sai dai, Hon. Ashiru Umar Gaye na daga cikin fitattun ‘yan takarar da s**a fi jan hankalin matasa da ‘yan kasuwa, sakamakon tsare-tsaren ci gaba da yake gabatarwa da kuma irin kwarin gwiwar da yake bai wa jama’a.

DUNIYA BA GURIN ZAMA BAShikenan fa Shugaba Buhari rayuwa tayi halinta, ya kwanta ya mutu, tabbas duk wata rayuwa sai ta ...
13/07/2025

DUNIYA BA GURIN ZAMA BA

Shikenan fa Shugaba Buhari rayuwa tayi halinta, ya kwanta ya mutu, tabbas duk wata rayuwa sai ta dandani mutuwa

Don Allah jama'ar Nigerua mu yafe wa Shugaba Buhari, kowa ya yafe masa don girman Allah

Allah Ka jikansa da rahama, Ka sa jinyar da yayi ta zama kaffara a gareshi🙏🙏🙏😭😭😭

Innalillahi wa inna ilaihirraji’un 😭Allah yayiwa baba buhari rasuwa
13/07/2025

Innalillahi wa inna ilaihirraji’un 😭

Allah yayiwa baba buhari rasuwa

27/02/2024

Address

Ddm
Kaduna South
KJR

Telephone

+2348087715994

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dandume Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Dandume Post:

Share