22/02/2026
Jami'an hukumar ICPC da ke yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya sun je gidan tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai, a Abuja ranar Alhamis, inda s**a gudanar da bincike.
Wata sanarwa da Muyiwa Adekeye, mai magana da yawun El-Rufai ya fitar ta ce jami'an na ICPC sun isa gidan tsohon gwamnan ne da misalin ƙarfe 2 na rana inda s**a ƙaddamar da bincike.
A cewarsa, lauyan El-Rufai, Ubong Akpan, ya soki wannan mataki wanda ya bayyana a matsayin "karya doka da 'yancin ɗan'adam."
A ranar Laraba ne hukumar ICPC ta ce El-Rufai yana hannunta bayan ya bar hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta'annati inda ya kai kansa ranar Litinin ɗin da ta wuce.
ICPC ba ta yi ƙarin bayani kan laifukan da take zargin El-Rufai da aikatawa ba, sai dai a baya tsohon gwamnan ya yi zargin cewa gwamnatin Nijeriya tana yin amfani da hukumar domin yi masa bi-ta-da-ƙulli.
Copied