10/04/2026
KADUNA: Gwamnati Ba Ta Da Hannu Wajen Rusau Shagunan Police Quarters — Hon. Rayyan Hussein
Shugaban Ƙaramar Hukumar Kaduna ta Kudu, Hon. Rayyan Hussein, ya bayyana cewa gwamnatin Jihar Kaduna karkashin jagorancin Gwamna Malam Uba Sani ba ta da masaniya ko hannu a rushe-rushen shaguna da aka yi a jikin rukunin gidajen ‘yan sanda (Police Quarters) da ke kan hanyar Poly Road, Tudun Wada Kaduna.
AMALE Hausa24 ta riwaito cewa, Hon. Rayyan Hussein ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin da ya kai ziyarar gani da ido domin jajantawa ‘yan kasuwar da lamarin ya shafa. A yayin ziyarar, shugaban ya tabbatar wa da masu shagunan cewa burin Gwamna Uba Sani shi ne gina al'umma da inganta rayuwar talakawa, ba wai ruguza hanyoyin samun abincinsu ba.
"Ina son in tabbatar muku da cewa wannan gwamnati ba ta rusau ba ce; gwamnati ce ta gina al'umma, bunkasa kasuwanci, noma, ilimi, da kiwon lafiya. Mai Girma Gwamna ba shi da wani buri da ya wuce ganin jama'arsa sun rayu cikin sauki da walwala," in ji Hon. Hussein.
Shugaban ya kara da sanar da cewa tuni Gwamna Uba Sani ya ba da umarnin kafa wani kwamitin gaggawa don gudanar da bincike mai zurfi a kan lamarin. Ya bayyana cewa kwamitin zai tabbatar da an bi doka da oda, sannan a samar da mafita ga ‘yan kasuwar da s**a yi asara don su ci gaba da harkokinsu na yau da kullum.
Wata majiya mai Karfi ta tabbatar ma da wakilinmu cewa wani (Developer) Wanda aka BA sake gina wurin Ake zargi da yin wannan rusau.
A nashi bangaren Shugaban 'Yan Kasuwar da abin ya shafa Alh. Yahaya Adamu ya bayyana Jin dadin su na yadda dukkan Bangarorin gwamnati da s**a hada da gwamnatin Jihar dana Karamar Hukumar s**a kawo musu dauki tare da tabbacin rashin hannun su a Wannan rasau.
Daga karshe, Hon. Rayyan Hussein ya jajantawa wadanda abin ya shafa, inda ya yi addu'ar Allah ya musanya musu da abin da ya fi alheri, tare da jaddada cewa gwamnati za ta tsaya tsayin daka wajen ganin kowa ya sami hakkinsa.
Abubakar Yahaya Ibrahim
AMALE Hausa24