AMALE Hausa24

AMALE Hausa24 Media House
(2)

KADUNA: Gwamnati Ba Ta Da Hannu Wajen Rusau Shagunan Police Quarters — Hon. Rayyan HusseinShugaban Ƙaramar Hukumar Kadun...
10/04/2026

KADUNA: Gwamnati Ba Ta Da Hannu Wajen Rusau Shagunan Police Quarters — Hon. Rayyan Hussein

Shugaban Ƙaramar Hukumar Kaduna ta Kudu, Hon. Rayyan Hussein, ya bayyana cewa gwamnatin Jihar Kaduna karkashin jagorancin Gwamna Malam Uba Sani ba ta da masaniya ko hannu a rushe-rushen shaguna da aka yi a jikin rukunin gidajen ‘yan sanda (Police Quarters) da ke kan hanyar Poly Road, Tudun Wada Kaduna.

AMALE Hausa24 ta riwaito cewa, Hon. Rayyan Hussein ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin da ya kai ziyarar gani da ido domin jajantawa ‘yan kasuwar da lamarin ya shafa. A yayin ziyarar, shugaban ya tabbatar wa da masu shagunan cewa burin Gwamna Uba Sani shi ne gina al'umma da inganta rayuwar talakawa, ba wai ruguza hanyoyin samun abincinsu ba.

"Ina son in tabbatar muku da cewa wannan gwamnati ba ta rusau ba ce; gwamnati ce ta gina al'umma, bunkasa kasuwanci, noma, ilimi, da kiwon lafiya. Mai Girma Gwamna ba shi da wani buri da ya wuce ganin jama'arsa sun rayu cikin sauki da walwala," in ji Hon. Hussein.

Shugaban ya kara da sanar da cewa tuni Gwamna Uba Sani ya ba da umarnin kafa wani kwamitin gaggawa don gudanar da bincike mai zurfi a kan lamarin. Ya bayyana cewa kwamitin zai tabbatar da an bi doka da oda, sannan a samar da mafita ga ‘yan kasuwar da s**a yi asara don su ci gaba da harkokinsu na yau da kullum.

Wata majiya mai Karfi ta tabbatar ma da wakilinmu cewa wani (Developer) Wanda aka BA sake gina wurin Ake zargi da yin wannan rusau.

A nashi bangaren Shugaban 'Yan Kasuwar da abin ya shafa Alh. Yahaya Adamu ya bayyana Jin dadin su na yadda dukkan Bangarorin gwamnati da s**a hada da gwamnatin Jihar dana Karamar Hukumar s**a kawo musu dauki tare da tabbacin rashin hannun su a Wannan rasau.

Daga karshe, Hon. Rayyan Hussein ya jajantawa wadanda abin ya shafa, inda ya yi addu'ar Allah ya musanya musu da abin da ya fi alheri, tare da jaddada cewa gwamnati za ta tsaya tsayin daka wajen ganin kowa ya sami hakkinsa.

Abubakar Yahaya Ibrahim
AMALE Hausa24

08/04/2026

Hon. Sulaiman Ibrahim Kotu yayi wannan kalamai ne yayin zantawarsa da AMALE Hausa24.

Kotu ya ce a shirye suke (ADC) tsaf domin amsar Mulki tun daga sama har kasa.

Me za Ku ce?

Bayern Munich ta samu nasara biyu ne cikin wasanni bakwai na baya da s**a buga da Real Madrid (canjaras 2, rashin nasara...
07/04/2026

Bayern Munich ta samu nasara biyu ne cikin wasanni bakwai na baya da s**a buga da Real Madrid (canjaras 2, rashin nasara 3). Sun rasa bakwai daga cikin wasanni 8 ɗin su na baya da s**a buga a matakin siri ƙwale da ƙungiyar Spain.

Real Madrid ta rasa wasa ɗaya ne kacal cikin wasanni 23 na baya da ta buga da ƙungiyar ƙasar Jamus (Nasara 16, canjaras 6) kuma sun samu nasara a wasanni 9 da s**a buga na baya da ƙungiyar Bundes Liga a matakin siri ƙwale.

06/04/2026

Daga Ina Kuke Bibiyarmu?

Zargin Rashin Aiki: Ina Kuɗaɗen Kananan Hukumomi S**a Nufa? Wasu Al’ummar kananan hukumomi 23 a Jihar Kaduna sun bayyana...
05/04/2026

Zargin Rashin Aiki: Ina Kuɗaɗen Kananan Hukumomi S**a Nufa?

Wasu Al’ummar kananan hukumomi 23 a Jihar Kaduna sun bayyana rashin gamsuwa da yadda ake tafiyar da harkokin mulki a matakin kananan hukumomi, inda s**a zargi shugabanninsu da gaza sauke nauyin da aka dora musu.

Rahotanni sun nuna cewa mazauna yankunan na ganin babu wani gagarumin ci gaba da aka samu a fannoni kamar gyaran hanyoyi, tsaftar muhalli da kuma kula da cibiyoyin lafiya na matakin farko, duk da cewa kananan hukumomi su ne mafi kusa da talakawa a tsarin mulki.

Wasu daga cikin al’ummar da s**a zanta da Amale sun bayyana cewa sun dade suna jiran ganin tasirin ayyukan gwamnati a matakin kananan hukumomi, amma har yanzu basu ga sauyi mai ma’ana ba.

“Ba mu ganin ayyukan da ya kamata a ce kananan hukumomi suna yi. Hanyoyi sun lalace, babu kulawa da muhallinmu,” in ji wani mazaunin karamar hukumar Lere.

Sai dai a bangaren gwamnati, Kwamishinan kula da kananan hukumomi da masarautu na jihar, Sadiq Mamman Lagos, ya sha bayyana cewa ana bai wa kananan hukumomi hakkokinsu yadda ya kamata kuma akan lokaci.

Duk da wannan bayani, al’ummar na ci gaba da nuna shakku, suna tambayar dalilin da yasa ba a ganin ayyukan a kasa idan har ana fitar da kudade kamar yadda aka bayyana.

Lamarin ya sa ake kira ga Shugaban kungiyar shugabannin kananan hukumomi (ALGON) na jihar da ya fito ya bayyana gaskiyar halin da ake ciki, ko dai gwamnatin jiha na sauke nauyinta yadda ya kamata, ko kuma akwai matsala wajen raba ko amfani da kudaden kananan hukumomi.

Masu sharhi kan harkokin mulki na ganin cewa rashin daidaito tsakanin bayanan gwamnati da koken jama’a na bukatar cikakken bincike domin gano hakikanin gaskiya.

Al’ummar Jihar Kaduna dai na jiran karin bayani daga hukumomi domin sanin ainihin inda matsalar take - ko a bangaren gwamnati, ko shugabannin kananan hukumomi.

Me za Ku ce?

Kamal Haruna Jere
AMALE Hausa24

Matan Makarfi Sun Nuna Goyon Bayan subga Uba SaniKungiyar mata a karamar hukumar Makarfi da ke jihar Kaduna sun gudanar ...
05/04/2026

Matan Makarfi Sun Nuna Goyon Bayan subga Uba Sani

Kungiyar mata a karamar hukumar Makarfi da ke jihar Kaduna sun gudanar da gagarumin taro domin nuna goyon bayansu ga gwamnan jihar, Uba Sani da Shugaban Karamar Hukumar.

A yayin taron, shugabar mata ta shiyya ta daya a jihar, Hajiya Jummai Shuibu, ta bayyana cewa gwamnan da kuma shugaban karamar hukumar Makarfi, Garba Muhammad Sabangari, suna kokari wajen kawo ci gaba ga al’umma.

"A wannan mulkin mu Mata da yayanmu Matasa, mun shaida Kuma muka kwankwadi romon Demokaradiyya, domin Hon. Garba Sabon Gari Yana kulawa da mu, kuma yana Jin koken mu"

Ta kara da cewa za su ci gaba da zagayawa sassa daban-daban na yankin domin wayar da kan mata kan ayyukan alherin da shugaban karamar hukumar ke aiwatarwa a Makarfi, karkashin jagorancin Mai girma Gwamnan Jihar Kaduna Mal. Uba Sani.

Hamza Lawal
AMALE Hausa24

Tsohon Dan Takarar Gwamnan Jihar Kaduna, Hon. Isa Ashiru Kudan, ya yanki katin zama memba a Jam'iyyar ADC.Wace fata za K...
05/04/2026

Tsohon Dan Takarar Gwamnan Jihar Kaduna, Hon. Isa Ashiru Kudan, ya yanki katin zama memba a Jam'iyyar ADC.

Wace fata za Ku mai?

Gwamnan kano ya bayyana haka ne a wani faifan bidiyon da Premier Radio, s**a wallafa, in da ya ke jawabi jim kadan bayan...
05/04/2026

Gwamnan kano ya bayyana haka ne a wani faifan bidiyon da Premier Radio, s**a wallafa, in da ya ke jawabi jim kadan bayan dawowar Shi Daga Abuja.

Abba yace Kano na bukatar Zaman Lafiya da hadin Kai tare da taimakon gwamnatin Tarayya Wanda a da basu samu hakan ba.

Me za Ku ce?

DA DUMI-DUMI: Motar CNG Ce Ta Fashe a Kaduna, Ba Bam Ba NeWata motar bas mai amfani da iskar gas (CNG) ta fashe a tashar...
05/04/2026

DA DUMI-DUMI: Motar CNG Ce Ta Fashe a Kaduna, Ba Bam Ba Ne

Wata motar bas mai amfani da iskar gas (CNG) ta fashe a tashar Lagos Garage da ke cikin Kaduna, lamarin da ya janyo firgici a tsakanin jama’a.

AMALE Hausa24 Motar, wadda mallakin kamfanin Silver Transport ce, ta samu matsala ne kafin fashewar, inda sassan ta s**a Tarwatse a wurin.

Sai dai duk da tashin hankalin da lamarin ya haifar, babu rahoton rasa rai ko jikkatar kowa izuwa hada wannan rahoto.

Rahotanni sun tabbatar da cewa fashewar na da alaka da na’urar CNG da motar ke amfani da ita, ba wani harin bam ba ne kamar yadda wasu ke yadawa a kafafen sada zumunta.

Hukumomi da jami’an agaji sun isa wurin domin shawo kan lamarin tare da tabbatar da tsaron jama’a.

Abubakar Yahaya Ibrahim
AMALE Hausa24

RIKICIN JOS: Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Kwaso Dalibai 400 A Jos.Gwamnatin Jihar Kaduna ta Kwaso a kalla Dalibai 400 da ke...
05/04/2026

RIKICIN JOS: Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Kwaso Dalibai 400 A Jos.

Gwamnatin Jihar Kaduna ta Kwaso a kalla Dalibai 400 da ke Karatu a Jami'ar Jos, biyo bayan sanarwar da Jami'an ta fitar da na cewa Dalibai su fice daga Gidajen kwanansu (Hostels) mallakin Jami'ar saboda halin tsaro.

AMALE Hausa24 ta riwaito cewa, Biyo bayan wannan sanarwar ne, Gwamnan Jihar Kaduna Sen. Uba Sani, ya bada umurnin kwaso daliban karkashin jagorancin Mai taimaka masa Kan harkokin Dalibai, Engr. Shu'aibu S.K. Bello.

Engr. S.K ya aike da Motoci Kirar 18 sita har Sha takwas da Jami'an tsaro domin jigilar Daliban, Kamar yadda gwamnan ya bada umurni, Kuma ko Wani Dalibi sai da aka Kaishi Karamar Hukumar Shi, Sannan aka damkawa iyayensu Su.

Daya daga cikin wadanda s**a jagoranci aikin, Engr. Aminu Y Umar, ya shaida mana Yadda Iyaye da Yan'uwan Daliban s**a nuna farin cikin da murnar su tare da yiwa Gwamnan UBA Sani Addu'u'a da fatan Alkhairi.

Amina Haruna Khalil
AMALE Hausa24

INDA RANKA: An Bude Gidan Dambe A Rigasa Don Samun Kudin Shiga.A ranar Asabar 4-4-2026 ne aka Bude Gida Dambe a garin Ri...
05/04/2026

INDA RANKA: An Bude Gidan Dambe A Rigasa Don Samun Kudin Shiga.

A ranar Asabar 4-4-2026 ne aka Bude Gida Dambe a garin Rigasa dake Karamar Hukumar Igabi ta Jihar Kaduna.

AMALE Hausa24 ta riwaito cewa an bude Gidan Damben ne da zammar samun Karin kudin shiga a Kasuwar ta Rigasa da a ke kira (Kasuwar Sati). Kamar yadda kansilan yankin Hon. Auwal Orbit ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Kansilan ya bayyana hakan a matsayin ci gaba, raya al'adu da bunkada Sana'o'in gargajiya. Sai dai a hannu guda wasu Al'ummar na ganin wannan a matsayin ci baya da kuma abun da zai jawo silar bata tarbiyar Yaran wannan yankin na Rigasa.

Me zaku ce?

Address

Kaduna South

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AMALE Hausa24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AMALE Hausa24:

Share