AMALE Hausa24

AMALE Hausa24 Media House
(1)

SALLAR ROKON RUWAN SAMAAn Gudanar Da Sallar Rokon Ruwa a Kaura Namoda Bayan Shafe Kwanaki Da Dama Babu Ruwan Sama, Wanda...
18/06/2025

SALLAR ROKON RUWAN SAMA

An Gudanar Da Sallar Rokon Ruwa a Kaura Namoda Bayan Shafe Kwanaki Da Dama Babu Ruwan Sama, Wanda Har Ta Kai mutane da dama hankulansu ya fara tashi duba da cewar kwanukan damina sun jima da tsayuwa amma har yanzu shiru, yayinda wasu mutanen iraruwansu na cikin ƙwarya domin jiran ruwan shukar.

Liman Malam Badamasu ne ya jagoranci Sallar yayinda Sheikh Malam Muhammad na gangaren Makaranta ya gabatarda Nasihohi masu ratsa zukata akan Muhimman lamura dake kawowa fadawa acikin waɗannan musifu na ɗaukewar ruwan sama da kuma ibada daya kamata a yawaita yinsu adai dai wannan lokaci domin gushewar Wannan farin.

Muhimman mutane da dama sun samu halartar Masallacin dafatan Allah ya bamu ruwan rahama Ameen.

Yahaya Mahi Na-Malam Babba
AMALE Hausa24

SAKON TAYA MURNASponsored:Babban Mai Taimakawa Gwamnan Jihar Kaduna Kan Harkokin Addinai, Shiekh Abdurrahman Zakariyya U...
12/06/2025

SAKON TAYA MURNA

Sponsored:

Babban Mai Taimakawa Gwamnan Jihar Kaduna Kan Harkokin Addinai, Shiekh Abdurrahman Zakariyya Usman (HUNAIN), Na Ta ya Mai Girma Gwamna Sen. Mal. Uba Sani CON. Murnar samun lambar yabo ta CON da Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu ya bashi.

Allah ya kara daga Darajar BALARABEN Gwamna Sen. Uba Sani CON., Kuma ya kare Martabar Shi, Allah yasa ya maimaita ✌️

Allah ya kara Mana zaman lafiya da yalwal Arziki a Jihar Kaduna. Ameen

Maimuna Abdullah
AMALE Hausa24

Jiya Gov Zulum ya bada talkafin N300,000,000 ga Gwamnatin Jahar Niger State Saboda Ambaliyan Ruwa da yayi sanadiyar mutu...
11/06/2025

Jiya Gov Zulum ya bada talkafin N300,000,000 ga Gwamnatin Jahar Niger State Saboda Ambaliyan Ruwa da yayi sanadiyar mutuwar Mutane sama da 170 a jahar Niger.

Idan zaku tuna shekara da ya wuce, anyi Ambaliya a Birnin Maiduguri wanda yayi sanadiyar rusa gidajen mutane da kuma sanadiyar Mutuwar mutane 10. Da kuma barnatar da dukiyoyin mutane da rasa mahallinsu.

Wanda Alokacin Jama’a daga warure da dama s**a kawo tallafi, jajantawa, ta’a ziyya da gudummuwa zuwa Maiduguri, wanda Shi Gov Bago na Jahar Niger ya bayar da N250,000, 000 a matsayin Gudummuwansa.

Abun Da naji Dadi a nan shine, Amana da kuma kyautatawa da shi Gov Zulum yayi. Ance Respect is reciprocal. Gov Zulum bai manta da Gudummuwa da akayi mishi ba a lokacin, shima sai ya sakawa Mutanen Niger state da na shi Gudummuwar.

Abun Bakin ciki kuma shine, Banga Saura Gomnonin Arewa sunyi yunkurin Jajantawa mutanen Niger ba, b***e ace Zasu bada Gudummuwarsu ba kamar yadda s**ayi a maiduguri. Duk da cewa mutanen da s**a mutu a Niger State ya wuce Na Maiduguri.

Yanzu abun nufi kenan, Gov Prof Zulum ne kadai wanda zai bada tallafi? Wannna ibtila’in ya faru sama da kusan wata daya anma Babu wanda zaizo ya tallafawa waenann mutane Banda Shi kadai?

Kuma Banga Jama’a sun nuna Alhini sosai ga wannan ibtila’in ba. Duk dama cewa Abun ya shafi Al’ummah sosai , dukkaninsu Talakawa ne kuma yan Arewa ne.

Ina kira da Yan Uwa da Abokanan Arziki, masu Hali da Gomnonimu na Arewa da su dubi Irin ta’adi da kuma rasa rayuka da akayi a Niger state Da Sukawo musu Agaji da kuma Gudummuwa.

Ina mika ta’aziyyata ga Mutanen Niger State da kuma Gov Bago.

Daga Shafin: Nuhu Hamza Danta
AMALE Hausa24

YANZU YANZU: Wata Hajiya Daga Jihar Kaduna Ta Rasu A Mina, Saudiyya Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kaduna a yau ta s...
07/06/2025

YANZU YANZU: Wata Hajiya Daga Jihar Kaduna Ta Rasu A Mina, Saudiyya

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kaduna a yau ta sanar da rasuwar daya daga cikin alhazanta Hajiya Hauwa Umar.

Hajiya Umar ta rasu ne a jiya, 6 ga watan Yuni, 2025, a yayin da take kan hanyarta ta zuwa Jamarat a Mina, kusa da birnin Makkah na kasar Saudiyya.

Jami'in Hulda da Jama'a na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna Yunusa Muhammad Abdullahi ne ya sanar da rasuwar.

Hukumar tana mika ta'aziyyarta ga iyalan Hajiya Hauwa Umar, da masoyanta, da daukacin al'ummar musulmin jihar Kaduna.

“Muna addu’ar Allah (SWT) ya ba ta zaman lafiya a gidan Aljannar Firdaus, ya kuma baiwa iyalanta karfin gwiwar jure wannan rashi da ba za a iya maye gurbinsu ba.

Abubakar Yahaya Ibrahim
AMALE Hausa24

07/06/2025

Celebrating my 6th year on Facebook. Thank you for your continuing support. I could never have made it without you. 🙏🤗🎉

Hoto Mafi Kayatarwa Yau Juma’a daga Ka’aba! Taofeek Ibrahim Adeshina ke nan da mahaifiyar sa a Mecca kuma dakin Allah.Ta...
30/05/2025

Hoto Mafi Kayatarwa Yau Juma’a daga Ka’aba!

Taofeek Ibrahim Adeshina ke nan da mahaifiyar sa a Mecca kuma dakin Allah.

Taofeek Kwararren mai Daukar hoto Kuma sananne a duniya, a Jihar Kano yayi bautar kasar sa.

Allah ya karbi Ibada. Amin. Wace Addu'a zaku Mai

Hoto: SIDE Media
AMALE Hausa24

Akalla Mahajjatan Najeriya 38,397 ne s**a isa Saudi Arabiya domin aikin hajjin 2025A sabon rahoton da Hukumar Alhazzai t...
24/05/2025

Akalla Mahajjatan Najeriya 38,397 ne s**a isa Saudi Arabiya domin aikin hajjin 2025

A sabon rahoton da Hukumar Alhazzai ta Najeriya NAHCOM ta wallafa a shafinta, ta nuna cewar zuwa safiyar jumu'a 23 ga watan mayun 2025, ta samu nasarar kwashe mahajjatan Najeriya 38,397 daga Kasar.

Mahajjata 35,264 sun sauka a Madina, yayin da mahajjata 3,133 s**a sauka a Jedda.

NAHCOM ta nuna cewar kawowa yanzu jirage 94 s**a tashi daga Najeriya zuwa Saudiya, 88 sun sauka a Madina yayin da 6 kacal s**a sauka a Jedda.

Yanzu haka Alhazzan Najeriya 13,455 suna Madina, inda Alhazzai 24,942 s**a isa Birnin Makka.

Abubakar Yahaya Ibrahim
AMALE Hausa24

HAJJIN BANA 2025:SANARWAJIRGI NA 12HukumarJin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna tana kira ga wasu daga cikin maniyyatan kana...
22/05/2025

HAJJIN BANA 2025:
SANARWA

JIRGI NA 12

HukumarJin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna tana kira ga wasu daga cikin maniyyatan kananan hukumomin Kachiya, Kaduna ta Arewa, Kagarko, Jemaá da aka lika sunayensu a ofisoshin ƙananan hukumominsu da s**a yi rajista da su hallara a sansanin alhazai da ke Mando, Kaduna yau Alhamis 22 ga watan Mayu, 2025 da zaran sun ji wannan sanarwa domin daukarsu zuwa kasa mai tsarki.

Ana bukatar maniyyata da wannan sanarwar ta shafa su tuntubi jami’ansu domin karin bayani.

Duk maniyyacin da ba sunansa, ba za a bari ya shiga sansanin alhazai ba.

Ana tunatar da maniyyata cewa su sanya unifom dinsu na alhazai tare da rike dukkan takardunsu na tafiya.

Ana gargadin maniyyata duk wanda ya ki fitowa, zai iya asarar kujerarsa tare da kudaden tikitin jirgi, masauki, sufuri da kudin ciyar da maniyyaci a kasa mai tsarki.

Ana bukatar 'ýan rakiya su tsaya iyakar da aka kebe na shigar maniyyata ne kadai a yayinda da s**a iso sansanin alhazai da ke Mando.
Allah Ya kawo ku lafiya.

Sanarwa daga
Yunusa Muhammad Abdullahi
Jami'in Hulda da Jama'a, na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna

HAJIN BANA 2025:Jirgi na 6 ✈️ na Alhazan jihar Kaduna ya tashi daga Jihar Kaduna Zuwa Kasa Mai Tsarki (Madina), da alhaz...
19/05/2025

HAJIN BANA 2025:
Jirgi na 6 ✈️ na Alhazan jihar Kaduna ya tashi daga Jihar Kaduna Zuwa Kasa Mai Tsarki (Madina), da alhazai 307 maza 236 mata 71....
Umza Air Services

HAJJIN BANA 2025:LABARI CIKIN HOTUNAHotunan ziyarar da wasu daga cikin Mahajjatan Jihar Kaduna s**a kai makabartar shahi...
19/05/2025

HAJJIN BANA 2025:

LABARI CIKIN HOTUNA

Hotunan ziyarar da wasu daga cikin Mahajjatan Jihar Kaduna s**a kai makabartar shahidai ta Uhudu.
Abubakar Yahaya Ibrahim
AMALE Hausa24

YADDA GIDAUNIYAR UMMUL-KHAIRI FOUNDATION KE RABAWA MANIYYATA ABINCI KYAUTASponsoredGidauniyar UmmulKhairi Foundation na ...
17/05/2025

YADDA GIDAUNIYAR UMMUL-KHAIRI FOUNDATION KE RABAWA MANIYYATA ABINCI KYAUTA

Sponsored

Gidauniyar UmmulKhairi Foundation na rabawa Maniyyata abinci kyauta a Sansanin Alhazai na Jihar Kaduna.

Gidauniyar ta UmmulKhairi Foundation na rabawa Maniyyatan abincin ne yayin da aka kira su izuwa Sansanin Alhazai domin tantance su (Screening) wasu lokutan ma har a filin sauka da tashin jiragen sama (Airport) s**an bisu su basu. K**a daga kan Tuwon Shinkafa, Kunu, da Kuma Shinkafa Kaza, Mai inganci da Kuma tsafta.

Haj. Maryam Yahaya Sani itace shugabar Gidauniyar ta UmmulKhairi Foundation, ta ce suna rabawa Maniyyata abincin ne domin kyautatawa da Kuma Taimakawa saboda duk inda matafiya suke suna bukatar taimako a Koda yau she.

Ta Kara da cewa suna wannan aiki ne da gudummuwar Ma'aikatar Kananan Hukumomi ta Jihar Kaduna, karkashin Jagorancin Hon. Sadiq Mamman Lagos

Maimuna Abdullah
AMALE Hausa24

SHEIK MUSA YUSUF ASSADUS SUNNA YAYI ABUN A YABA.Wannan bawan Allah na kicin matasan Mallamai da suke kokarin yin da'awa,...
06/05/2025

SHEIK MUSA YUSUF ASSADUS SUNNA YAYI ABUN A YABA.

Wannan bawan Allah na kicin matasan Mallamai da suke kokarin yin da'awa, Assadus Sunna na cikin Malaman da sukeda tarin mabiya na kusa dana nesa. Duk da a lokuta da dama yakan samu matsala da mutane wurin fahimta ko ra'ayi kamar yadda kowane Malamin addini yake samu. Assadu na cikin Malaman da basu bari sai ta kwana. Duk Inda yaji anyi kuskure ko anzo da wata fahimta data sabawa addini yakanyi iyayinshi yaga an warware wannan takaddama cikin ruwan sanyi.

Abunda ya yawo hankalina har yasani yin wannan rubutun shi ne idan Assadu yai wani dan karamin kuskure a matsayinsa na dan Adam da yake da ajizanci, cikin yan mintina kadan yan media s**an tasashi a gaba, da s**a zagi da cin mutunci. A wasu lokutama s**an kirashi da wasu sunaye munana. Wanda ake jira yayi kuskure a diranmasa ai yakamata idan yai wata bajinta kuma a yaba mishi. Duk da kasancewar duk Malami mai da'awa zai fuskanci irin wayannan abubuwan.

Shekaranjiya Gwamna Uba Sani yazo yima Assadu ta'aziyar Mahaifiyarshi data rasu. Bayan Uba Sani ya gama ta'aziyar, Assadu yace mashi yanada wata alfarma da yakeso ya roki Gwamna. Bayan Gwamna ya bashi damar rokon wannan alfarmar. Assadu ya fadawa Gwamnan a kuma gaban duk wanda yake wurin akayi. Maigirma Gwamna sanda kake shigowa Tudun-Wada kaga yadda mata da kananan yara suke yawon neman ruwa. Matanmu na Tudun-Wada sun zama kamar yangaruwa, muna rokon Gwamna yayi wani abu akai.

Wannan magana ba'a boye Assadu ya yitaba a bainar jama'a ya yita. Wanda na tabbatar da kuskure yayi da yanzu maganar na nan tana zagaya media. Nan take kuma shi Gwamnan yai alkawarin cewar in Allah ya yarda za'ayi dukkan mai yuwuwa aga a fidda Tudun-Wada cikin wannan tsaka mai wuyan. Junjina ga Sheik Musa Yusuf Assadus Sunna, shikuma Gwamna Uba Sani Allah ya bashi ikon aiwatar da wannan kudirin nashi. Abdullahi Musa Badayi

Address

Kaduna South

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AMALE Hausa24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AMALE Hausa24:

Share