23/02/2026
Sama Da Mutum Ɗari Biyu Aka Kashe, An Sace Wasu A Cikin Kwanaki Biyu A Jihohin Zamfara Da Kebbi
Daga Kungiyar Arewa Media Writers
Kungiyar Arewa Media Writers, karkashin jagorancin shugaban ƙungiyar na ƙasa Comr Haidar H Hasheem, ta bayyana matukar alhini da fusatarta kan hare-haren kisan gilla da sace jama’a da s**a afku a jihohin Zamfara da Kebbi cikin kwanaki biyun da s**a gabata.
Kungiyar ta ce abin takaici ne yadda rayukan al’ummar Arewa ke ci gaba da salwanta ba tare da daukar tsauraran matakan da s**a dace ba daga hukumomin da abin ya shafa.
A cewar kungiyar, rahotannin da ke fitowa daga jaridar The Cable sun nuna cewa harin ya auku ne a jihar Zamfara a ranar Asabar, inda akalla mutane 50 s**a rasa rayukansu, yayin da sama da mutane 150, ciki har da mata da kananan yara, aka yi garkuwa da su a kauyen Tungan Dutse da ke karamar hukumar Bukkuyum.
Haka zalika, jaridar Vanguard ta ruwaito cewa an kashe mutane 34 a wasu garuruwa daban-daban na karamar hukumar Arewa a jihar Kebbi.
Kungiyar ta bayyana cewa shiru ko sakaci daga bangaren gwamnati kan irin wannan mummunan lamari tamkar amincewa ne da ci gaba da zubar da jinin bayin Allah. Ta jaddada cewa rayukan al’ummar Arewa suna da daraja kamar na kowanne yanki na kasar nan.
Don haka, Arewa Media Writers ta bukaci gwamnatocin jihohin Kebbi da Zamfara tare da gwamnatin tarayya da su dauki matakan gaggawa, ciki har da:
- Kara yawan jami’an tsaro a yankunan da rashin tsaron ke kara yawaita
- Tallafawa wadanda harin ya rutsa da su
- Bincike mai zurfi kan lamarin
- Daukar mataki kan duk wani jami’i ko mai ruwa da tsaki da aka samu da sakaci ko hannu a matsalar tsaro
Kungiyar ta jaddada cewa ba za ta yi shiru ba har sai an tabbatar da adalci, an kamo masu hannu a wannan ta’asa, tare da daukar matakan da za su kawo karshen wannan bala’i da ke addabar yankin Arewa.
Daga ƙarshe ƙungiyar tayi addu'a kan Allah ya bawa ƙasarmu zaman lafiya musamman yankinmu na Arewacin Najeriya, haka kuma ƙungiyar tayi addu'ar dukkan mai hannu a wannan ta'addancin Allah yayiwa al'umma maganinsa.
✍️ Muhammad Kwairi Waziri, Chief Editer "Arewa Media Writers"