Kidaya

Kidaya Kidaya Is Online Newspaper that features truthful and reliable information in Nigeria and beyond. We

Sama Da Mutum Ɗari Biyu Aka Kashe, An Sace Wasu A Cikin Kwanaki Biyu A Jihohin Zamfara Da KebbiDaga Kungiyar Arewa Media...
23/02/2026

Sama Da Mutum Ɗari Biyu Aka Kashe, An Sace Wasu A Cikin Kwanaki Biyu A Jihohin Zamfara Da Kebbi

Daga Kungiyar Arewa Media Writers

Kungiyar Arewa Media Writers, karkashin jagorancin shugaban ƙungiyar na ƙasa Comr Haidar H Hasheem, ta bayyana matukar alhini da fusatarta kan hare-haren kisan gilla da sace jama’a da s**a afku a jihohin Zamfara da Kebbi cikin kwanaki biyun da s**a gabata.

Kungiyar ta ce abin takaici ne yadda rayukan al’ummar Arewa ke ci gaba da salwanta ba tare da daukar tsauraran matakan da s**a dace ba daga hukumomin da abin ya shafa.

A cewar kungiyar, rahotannin da ke fitowa daga jaridar The Cable sun nuna cewa harin ya auku ne a jihar Zamfara a ranar Asabar, inda akalla mutane 50 s**a rasa rayukansu, yayin da sama da mutane 150, ciki har da mata da kananan yara, aka yi garkuwa da su a kauyen Tungan Dutse da ke karamar hukumar Bukkuyum.

Haka zalika, jaridar Vanguard ta ruwaito cewa an kashe mutane 34 a wasu garuruwa daban-daban na karamar hukumar Arewa a jihar Kebbi.

Kungiyar ta bayyana cewa shiru ko sakaci daga bangaren gwamnati kan irin wannan mummunan lamari tamkar amincewa ne da ci gaba da zubar da jinin bayin Allah. Ta jaddada cewa rayukan al’ummar Arewa suna da daraja kamar na kowanne yanki na kasar nan.

Don haka, Arewa Media Writers ta bukaci gwamnatocin jihohin Kebbi da Zamfara tare da gwamnatin tarayya da su dauki matakan gaggawa, ciki har da:

- Kara yawan jami’an tsaro a yankunan da rashin tsaron ke kara yawaita
- Tallafawa wadanda harin ya rutsa da su
- Bincike mai zurfi kan lamarin
- Daukar mataki kan duk wani jami’i ko mai ruwa da tsaki da aka samu da sakaci ko hannu a matsalar tsaro

Kungiyar ta jaddada cewa ba za ta yi shiru ba har sai an tabbatar da adalci, an kamo masu hannu a wannan ta’asa, tare da daukar matakan da za su kawo karshen wannan bala’i da ke addabar yankin Arewa.

Daga ƙarshe ƙungiyar tayi addu'a kan Allah ya bawa ƙasarmu zaman lafiya musamman yankinmu na Arewacin Najeriya, haka kuma ƙungiyar tayi addu'ar dukkan mai hannu a wannan ta'addancin Allah yayiwa al'umma maganinsa.

✍️ Muhammad Kwairi Waziri, Chief Editer "Arewa Media Writers"

Kamfanin ABBA PANTAMI DATA LTD, suna muku barka da shigowa sabuwar shekara. A yanzu haka Datar 1GB mai kyau da inganci t...
01/01/2026

Kamfanin ABBA PANTAMI DATA LTD, suna muku barka da shigowa sabuwar shekara.

A yanzu haka Datar 1GB mai kyau da inganci ta koma kasa da Naira 500 a cikin Application din ABBA PANTAMI DATA LTD, kowa ya duba Application dinshi domin more garabasa, anyi ragi na musamman a sauran Data na Application din.

DA DUMI-DUMI: Ali Nuhu ya zama Ambasadan kamfanin ABBA PANTAMI DATA LTD, bayan kulla yarjejeniyar Naira miliyan 30 na ts...
25/12/2025

DA DUMI-DUMI: Ali Nuhu ya zama Ambasadan kamfanin ABBA PANTAMI DATA LTD, bayan kulla yarjejeniyar Naira miliyan 30 na tsawon shekara guda

ABBA PANTAMI DATA LTD ya sake rage muku farashin Data zuwa Naira 500 akan kowane 1GB, ku hanzarta ku sauke Application din, domin ku more garabasa.

Duk wanda ya sayi Data mai 30DAYS a Application din ABBA PANTAMI DATA LTD to sai tayi kwanaki 30 sannan za tayi Expired. Akwai bambanci tsakanin Expired da kuma karewa.

Matukar kuna amfani da Application din ABBA PANTAMI DATA LTD da zaran ka hadu da matsalar network ko makalewar kudi kana yiwa customer care dinsu magana anan take zasu gyara maka.

Idan baka taba amfani da Application din ba ka gwada, idan ka dade baka yi amfani dashi ba ka sake gwadawa a yanzu domin tabbatar da ingancin shi.

Kuyi Download din Application din ABBA PANTAMI DATA ta wannan link din a PlayStore da kuma AppStore

👇👇
Ga link din PlayStore
https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.com.abbapantamidata.app

Ga link din AppStore
https://apps.apple.com/us/app/abba-pantami-data-ltd/id6744061271

Mai bukatan karin bayani, ya tuntubi daya daga cikin customer care ta WhatsApp;
09138275183
08126081967
07046868000
07061347599

TIRKASHI: Hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ta bayar da Naira biliyan 2.5 ga kasar Najeriya domin su gina filin kwallo...
26/10/2025

TIRKASHI: Hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ta bayar da Naira biliyan 2.5 ga kasar Najeriya domin su gina filin kwallon kafa a jihar Kebbi da Delta.

Itama Kenya an bata irin wannan kudin domin ta gina.

Ga dai na Najeriya da aka gina a Kebbi an kashe mishi biliyan 1.2😅😂
Ga kuma na Kenya.

Dr. Bashir Abdullahi Gaddafi Ya Halarci Zaman Da Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar a AbujaDaya daga cikin m...
21/10/2025

Dr. Bashir Abdullahi Gaddafi Ya Halarci Zaman Da Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar a Abuja

Daya daga cikin manyan ‘ya’yan jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a Jihar Gombe, Hon. Dr. Bashir Abdullahi Gaddafi, ya kasance cikin tawagar shugabannin jam’iyyar da s**a ziyarci tsohon mataimakin shugaban ƙasa kuma jagoran kwatowa talakawa ‘yancinsu, Alhaji Atiku Abubakar, a babban birnin tarayya Abuja, a daren Litinin.

Ziyarar ta kasance wani ɓangare na ci gaba da tattaunawa tsakanin shugabannin jam’iyyu da fitattun ‘yan siyasa domin ƙarfafa haɗin kai da fahimtar juna a tsakanin ‘yan Najeriya, tare da neman hanyoyin da za su inganta rayuwar talakawa da haɓaka dimokuraɗiyya a ƙasar nan.

A cewar Dr. Gaddafi, wannan zama na da muhimmanci wajen ƙarfafa haɗin kai da samar da cigaba a yankin Arewa, musamman a Jihar Gombe da Karamar Hukumar Akko.

Ubangiji Allah Ya sanya wannan zama ya amfanar da al’ummar Najeriya, Jihar Gombe, da Karamar Hukumar Akko gaba ɗaya,” in ji Dr. Bashir Abdullahi Gaddafi yayin da yake ganawa da manema labarai bayan zaman.

Dr. Gaddafi ya kara da cewa lokaci ya yi da ‘yan siyasa za su mayar da hankali wajen warware matsalolin tattalin arziki, ilimi da zaman lafiya domin dorewar ƙasa.

Wannan ziyara ta Dr. Gaddafi ta ƙara nuna yadda matasa masu kishin ƙasa ke shiga harkokin siyasa cikin natsuwa da hangen nesa, tare da neman hanyoyin haɗin kai domin ci gaban al’umma.

Fatan Nasara Baba Atiku
Tare da Dr. Bashir Gaddafi Kumo. ✅🇳🇬

Hon. Dr. Bashir Abdullahi Gaddafi Ya Gana da Kungiyoyi a Garin KumoJagoran kawo canji a siyasar Karamar Hukumar Akko, Ho...
17/10/2025

Hon. Dr. Bashir Abdullahi Gaddafi Ya Gana da Kungiyoyi a Garin Kumo

Jagoran kawo canji a siyasar Karamar Hukumar Akko, Hon. Dr. Bashir Abdullahi Gaddafi, ya gudanar da ganawa da wasu kungiyoyi masu muhimmanci a garin Kumo, domin tattauna hanyoyin da za su inganta hadin kai da cigaban al’umma.

Kungiyoyin da s**a halarci taron sun haɗa da wakilan ƙungiyar makanikai, Northern Youth Solidarity Movement, Matasan Anguwan Makera Tambe, da kuma Akko Great Ambassadors Youth Forum.

A yayin tattaunawar, Dr. Gaddafi ya bayyana cewa tafiyar da suke yi tafiyar kowa da kowa ce, wacce nufinta shi ne samar da sauyi mai ma’ana da kuma tabbatar da cigaba ga jama’ar Akko.

Ya kara da cewa, da yardar Allah, zamu kai inda muka dosa, yana mai tabbatar da cewa wannan tafiyar za ta bai wa talakawa damar amfana da romon dimokaradiyya.

A ƙarshe, mahalarta taron sun yi addu’ar samun nasara ga tafiyar siyasar Dr. Gaddafi domin dorewar cigaba da zaman lafiya a Akko.

Dr. Gaddafi 2027: Muradin Jama’a, Al’umma ne suke son Dr. Gaddafi ya tsaya takara, ba shi ne yake neman mulki ba. Jama’a...
16/10/2025

Dr. Gaddafi 2027: Muradin Jama’a,

Al’umma ne suke son Dr. Gaddafi ya tsaya takara, ba shi ne yake neman mulki ba. Jama’a daga birane da karkara suna ganin ya cancanci jagoranci saboda nagarta da jajircewarsa wajen taimakon al’umma da ci gaban ƙasa.

Dr. Gaddafi ya riga ya yi abubuwan da ake buga misali da su aiki, gaskiya, da sadaukarwa. Wannan ne yasa jama’a ke haɗa kai suna cewa Dr. fito 2027, mulki na Allah ne, shi ne yake bayarwa, kuma ikon wani ba zai hana Allah nashi ba.

Mu mutanen birni da karkara muna tare da kai, Dr. Gaddafi.
Dr. Muke Fata 2027, Insha Allahu.

Sako Zuƙowa GaMai Girma Gwamnan Jihar GombeRt. Hon. Kakakin Majalisar Dokokin Jihar GombeHon. Shugaban Karamar Hukumar A...
06/10/2025

Sako Zuƙowa Ga

Mai Girma Gwamnan Jihar Gombe

Rt. Hon. Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Gombe

Hon. Shugaban Karamar Hukumar Akko

Senatan. Gombe ta tsakiya

Rt. Hon. Majalisar Dokokin Tarayya

Batun- Buƙatar Shigar da Garin Alkali, Garin Liman da jauro Musa kumo cikin Ayyukan Ci gaba

Da farko, mu al’ummar Garin Alkali, Garin Liman da jauro Musa muna miƙa godiya ga Allah Maɗaukaki, sannan kuma muna mika godiya da yabo gareku shugabanni bisa irin ƙoƙari da jajircewa wajen kawo ayyukan ci gaba a yankinmu na Garin Kumo da kewaye.

Duk da irin wannan cigaba, muna mai sanar da ku cewa, al’ummar Garin Alkali, Garin Liman da jauro Musa duk da kasancewarsu masu bada gudummawa mai yawa a lokutan zaɓe sun dade suna kasancewa a baya wajen cin gajiyar romon dimokuraɗiyya. Wannan ya shafi fannoni da dama musamman:

1. Ayyukan Tituna: Muna buƙatar a haɗa mu cikin shirin gina tituna da ake aiwatarwa a Garin Kumo domin rage wahalhalun zirga-zirga da matsalolin sufuri.

2. Wutar Solar: A tabbatar da saka hasken wutar solar a unguwanninmu domin kawo ƙarshen duhu da matsalar rashin wuta.

3. Matsalar Zaizayar Ƙasa: Garin Liman da jauro Musa ya dade suna fama da matsalar zaizayar ƙasa wadda ke barazana ga al’umma, duk kuwa da roƙon da aka ta gabatar tun shekaru da dama da s**a wuce.

Mun yi imanin cewa, idan aka kula da waɗannan bukatu, zai taimaka wajen rage matsalolin yau da kullum da al’ummarmu ke fuskanta, tare da ƙara haɗa su cikin tsarin ci gaban jihar.

Saboda haka, muna kira ga shugabannin siyasa na wannan yanki, tare da matasa da s**a shiga harkar siyasa, da su ɗauki koken al’ummarmu, domin a tabbatar da cewa Garin Alkali, Garin Liman da jauro Musa sun ci gajiyar dimokuraɗiyya kamar sauran yankuna.

Allah ya sanya wannan sako ya isa inda ake so, ya kuma sa ku sami nasara da albarka a dukkan ayyukan alheri.

✍️Muhammad chigari kumo
(Chigarin Barunde)
Madadin Al’ummar Garin Alkali, Garin Liman da Jauro Musa kumo

Kira ga Gwamnati da Masu Ruwa da TsakiDuba da yadda al’ummar Garin Alkali da Garin Liman suke taka muhimmiyar rawa wajen...
03/10/2025

Kira ga Gwamnati da Masu Ruwa da Tsaki

Duba da yadda al’ummar Garin Alkali da Garin Liman suke taka muhimmiyar rawa wajen bayar da gudummawa a lokacin zaɓe, ya dace a tabbatar da cewa suma sun amfana daga ayyukan ci gaba da ake aiwatarwa a Garin Kumo. Ayyuka irin su gina tituna da kuma saka wutar Solar ya kamata su kai har zuwa waɗannan yankuna, domin su ma su ci gajiyar romon dimokuraɗiyya.

Yankunan Garin Alkali da Garin Liman sun daɗe suna kasancewa a bayan baya wajen samun albarkacin ci gaban Gwamnati duk da yawan jama’ar da ke zaune a wuraren. Musamman ma Garin Liman ya shafe lokaci mai tsawo yana fama da matsalar zaizayar ƙasa, wacce ta addabi al’umma har zuwa yau.

Saboda haka, muna kira ga manyan ‘yan siyasa na wannan yanki tare da matasa masu tasowa a harkokin siyasa da su riƙa ɗaukar koken al’ummomin nan, domin a shigar da su cikin tsarin samun ci gaba.

Mu na roƙon Allah Madaukakin Sarki Ya sanya wannan kira ya isa inda ake so, kuma ya zamo abin amfana ga al’ummarmu baki ɗaya.

Daga Muhammad chigari kumo

NEMAN TAIMAKO! NEMAN TAIMAKO!‘Yan uwa da abokan arziki, muna neman taimakon ku a wannan lokaci mai muhimmanci.Wannan tak...
29/09/2025

NEMAN TAIMAKO! NEMAN TAIMAKO!

‘Yan uwa da abokan arziki, muna neman taimakon ku a wannan lokaci mai muhimmanci.

Wannan takaddar gwaji da kuke gani ta Goggo Addayo Dakkiti, wadda aka yi mata scanning tun ranar 16/09/2024. Likitoci sun tabbatar da cewa tana bukatar Lumbosacral Surgery, amma kudin aikin ya gagara saboda halin rayuwa.

Tun kimanin shekaru uku, Goggo tana fama da jinya mai tsanani, inda komai sai an mata, kuma yanzu haka tana kwance a gida cikin wahala

Duk wani mai jinya yasan cewa, jinya mai ɗaukar lokaci tana cin ƙarfi da ƙimarsa, b***e wadda ta kai tsawon shekaru.

A halin yanzu, ana buƙatar Naira Dubu Dari Takwas (₦800,000) domin gudanar da wannan aikin tiyata tare da sauran dawainiyarsa.

Saboda haka, muna roƙon ‘yan uwa Musulmai da masu zuciya ta alheri, kusa da nesa, da su taimaka gwargwadon iko ko da sisi ne, ko kuma daukar nauyin gaba ɗaya.
Idan ba da kai tsaye ba, zaka iya yada wannan saƙo zuwa kunnuwan wanda zai iya taimakawa.

Muna addu’a Allah ya ba Goggo lafiya, ya kuma ba kowane mara lafiya lafiya, ya kuma ƙara mana lafiya garemu da ‘ya’yanmu.

Ga lambobin tuntuɓa / bada gudunmawa:
09030772989
09039796363
08034829056

Al'umma A Jihar Imo Sun Yiwa El'rufai Tofin Alatsine, Sun Yi Watsi Da Shi Tare Da Nuna Ƙyma Da Irin SiyasarsaDaga Abdul-...
09/09/2025

Al'umma A Jihar Imo Sun Yiwa El'rufai Tofin Alatsine, Sun Yi Watsi Da Shi Tare Da Nuna Ƙyma Da Irin Siyasarsa

Daga Abdul-Azeez Suleiman

Nasir El-Rufai, tsohon gwamnan Kaduna, ya gamu da zanga-zangar ƙin karɓarsa a Owerri, Jihar Imo, lokacin da ya halarci Taron Odenigbo 2025 a Assumpta Cathedral. Jama’a sun fito da kwalaye da ƙorafe-ƙorafe, suna zarginsa da kalaman wariya kan kabilar Igbo a baya.

Wannan martani bai tsaya kan shi kaɗai ba, ya kuma fito da tsohuwar matsalar rashin haɗin kai, raunin Yaƙin Basasa, da kuma gajiyar jama’a ga shugabannin da ake ganin sun rabu da halin rayuwar talakawa.

Masu zanga-zangar har sun yi kira ga a tsawatar wa Peter Obi saboda kusancinsa da shi, abin da ya nuna cewa kowane ɗan siyasa na iya fuskantar tambaya muddin yana da alaƙa da mutanen da ake kallon masu raba kan ƙasa.

Zanga-zangar ta zama alamar cewa jama’a na da ƙarfi wajen kalubalantar manyan ‘yan siyasa, musamman a wannan zamani na kafafen sada zumunta. Darasin da ke ciki shi ne shugabanni su daina rarrabuwar kawuna, su rungumi tattaunawa, su girmama tarihi, domin kawai haka za a samu haɗin kan ƙasa mai bambance-bambance.

Jama’a Sun Yi Masa Watsi, Sun Nuna Ƙiyayya da Siyasar Rarrabuwar irin ta El'rufai, sun kuma shawarci Peter Obi da ya gaggauta nesanta kansa da El'rufai don tsira da mutuncinsa.

Dr. Bashir Abdullahi Gaddafi  Jagoran Al’umma, Ba Tare da Mukami BaA yau, Hon. Dr. Bashir Abdullahi Gaddafi ya sake tabb...
05/09/2025

Dr. Bashir Abdullahi Gaddafi Jagoran Al’umma, Ba Tare da Mukami Ba

A yau, Hon. Dr. Bashir Abdullahi Gaddafi ya sake tabbatar da cewa siyasa ba lallai ta tsaya kan mukami ba, illa hidima ga al’umma.

Ya bayar da Naira miliyan 1,500,000 (1.5m) domin gyaran Transformer na Anguwan Jerusalem, tare da ƙarin Naira dubu 800,000 domin gyaran Transformer na Anguwan Black Market.

Wannan ayyuka sun kara tabbatar da cewa Dr. Gaddafi shi ne jagoran da ya ke kula da jama’arsa ba tare da wani kujerar siyasa ba. A tarihi, babu wani ɗan siyasa a Akko da ya yi hidima irin ta Dr. Gaddafi tun kafin samun mukami.

Dr. Gaddafi nagartaccen shugaba ne, wanda burinsa shi ne ganin jama’arsa sun fita daga duhu zuwa haske, daga ƙunci zuwa jin daɗi.

Muna addu’a Allah ya kara masa iko, ya tsare shi, ya kuma bamu sa’a a siyasar 2027, domin samun shugaba nagari wanda al’umma ke alfahari da shi.

Address

Kaduna Zaria Round
Kaduna South
2580111

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kidaya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share