09/05/2026
Ɗan Garin Kumo Ya Kafa Tarihi A Jihar Gombe Na Samun Nasara A Fannin Ilimi
Daga: Muhammad Chigari Kumo
Wani matashi ɗan asalin garin Kumo da ke ƙaramar hukumar Akko a Jihar Gombe, Muhammad Usman Yahya, ya kafa tarihi a fannin ilimi bayan kammala karatun digiri da na Masta da sakamako na First Class.
Rahotanni sun nuna cewa Muhammad Usman Yahya, wanda ke koyarwa a Gombe State University reshen Dukku, ya samu First Class a Abubakar Tafawa Balewa University (ATBU) da CGPA 4.83, inda ya kasance ɗaya daga cikin ɗaliban da s**a fi ƙwazo a sashensa da kuma a Faculty ɗinsa.
Bayan wannan nasara, ya ci gaba da karatun digirin Masta, inda kuma ya sake samun First Class da CGPA 4.93, abin da ya ƙara tabbatar da kwazonsa, jajircewarsa da kuma himmarsa wajen neman ilimi.
A halin yanzu, yana ci gaba da karatun Digirin Digirgir (PhD) a fannin Estate Management and Valuation, domin zurfafa bincike da kuma bayar da gudunmawa ga ci gaban ilimi da harkar kimanta kadarori.
Da yake bayyana sirrin nasararsa, Muhammad Usman Yahya ya ce jajircewa, haƙuri da mayar da hankali ga buri su ne ginshiƙan da s**a taimaka masa wajen cimma wannan matsayi.
Ya kuma shawarci ɗalibai da matasa da su guji kwatanta kansu da wasu, su dage wajen neman ilimi tare da yin aiki tukuru domin cimma burinsu.
Wannan nasara ta zama abin alfahari ga al’ummar Kumo, Jihar Gombe da ma Najeriya baki ɗaya, tare da nuna cewa ƙwazo da jajircewa na iya kai mutum ga manyan matsayi a rayuwa.