27/07/2026
Budurwa ta yanke mazakutar saurayinta a otal da ke Kano
Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kano ta tabbatar da k**a wata budurwa mai shekaru 25 da ake zargi da yanke mazakutar saurayinta yayin da yake barci a wani otal da ke unguwar Badawa a Kano.
Kakakin rundunar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce lamarin ya faru da misalin ƙarfe 12 na ranar Litinin, bayan samun rahoton abin da ya faru.
Ya bayyana cewa duk da masoyan biyun 'yan asalin Jihar Jigawa ne, lamarin ya faru ne a Kano.
A cewarsa, binciken farko ya nuna cewa wadda ake zargin ta zo daga Maigatari da wata wuka, wadda ake zargin ta yi amfani da ita wajen aikata laifin.
Kiyawa ya ce matar ta shaida wa 'yan sanda cewa ta aikata lamarin ne yayin da saurayin nata ke barci bayan ya sha maganin ciwon kai, wanda ya sa ya yi barci mai nauyi.
Ya ce bayan faruwar lamarin, ana zargin ta ja saurayin zuwa banɗaki domin wanke jinin kafin mutanen da ke wajen s**a fahimci abin da ke faruwa tare da sanar da jami'an tsaro.
Dangane da rade-radin cewa an yi amfani da wani sinadari ko kayan maye, kakakin rundunar ya ce har yanzu babu wata hujja da ke tabbatar da hakan.
Ya ƙara da cewa jami'an 'yan sanda sun samu kwalbar Lacasera da ruwa a ɗakin, kuma ana ci gaba da bincike domin gano ko suna da alaƙa da lamarin.
Kiyawa ya tabbatar da cewa saurayin na raye kuma yana karɓar magani a asibiti.
Ya ce wadda ake zargin tana tsare a hannun 'yan sanda, yayin da bincike ke ci gaba kafin gurfanar da ita a gaban kotu.
-Daily Nigerian