Muhimmiya

Muhimmiya Media/News Company
(1)

Kotu  ta ɗage shari'ar Zargin almundahanar kuɗaɗen Naira Biliyan 8.7 da ake ma  tsohon ministan Shari'a zuwa 23 ga watan...
22/05/2026

Kotu ta ɗage shari'ar Zargin almundahanar kuɗaɗen Naira Biliyan 8.7 da ake ma tsohon ministan Shari'a zuwa 23 ga watan Yuni.

Mai sharia'a Joyce Abdulmalik na babbar kotun tarayya dake Maitama Abuja , ya ɗage shari'ar da ake yi ta zargin almundahnar kudaden Naira Biliyan 8.7 da ake zargin tsohon Ministan Shari'a Abubakar Malami , SAN da matarsa Hajiya Bashir Asabe da kuma ɗan sa Abdulaziz Malami
Hukumar EFCC ce ta shigar da ƙarar da ta ƙunshi tuhume tuhume 16, da s**a haɗa da haɗa baki , ɓoyewa da karkatar da kuɗaɗe haɗi da almundahnar kuɗaɗe da sauran wasu haramtattu abubuwa waɗanda s**a saɓawa tanadin dokar hana almundahanar kuɗaɗe ta shekar 2022.
A zaman kotun na ranar Juma’a, lauyan masu shigar da kara, J.S. Okutepa, SAN, ya sanar da kotu cewa yaune ranar ci gaba da sauraron shari’ar, amma masu shigar da kara sun karɓi wasiƙa daga bangaren lauyoyin masu bada kariya na neman a dage zaman.

Ya bayyana cewa " yaune aka tsara cigaba da sauraron wannan shari’a ne An ma an ba mu wasiƙa ta hannun Rijistar Kotun a ranar 20 ga Mayu, 2026, daga lauyoyi bada kariya na J.B. Daudu . Mun so mu kaucewa buƙatar dagewar, amma ba mu so mu kawo naƙasu ga cigaba da gudanar shari’ar.”

Ya ƙara roƙon kotu ta lura da yawan lokutan da masu karewa s**a nemi a dage shari’ar.

A hukuncinta, Mai Shari’a Abdulmalik ta amince da buƙatar lauyan masu shigar da kara, inda ta ce rashin halartar babban lauyan waɗanda ake ƙara bai k**ata ya dakile zaman ba, musamman la’akari da yawan lauyoyin da gudanar da shari'ar.

Tace “Na amince da bukatar ka , babban lauya ta cewa lauyan waɗanda ake ƙara yana da lauyoyi da yawa , babu pp 0pí dalilin dakile zaman a yau. Amma tunda suna da damar neman dage shari'ar sau biyar, za mu amince da wannan sau ɗaya,” in ji maisharia

Saboda haka, kotun ta dage shari’ar zuwa 23 ga Yuni, 2026 domin ci gaba da saurara, k**ar yadda babban lauyan waɗanda ake ƙara ya gabatar.

Dahiru Kasimu Adamu

Thanks for being a top engager and making it on to my weekly engagement list! 🎉 Zainab Suleman, Abdullahi Hassan, Baka A...
19/05/2026

Thanks for being a top engager and making it on to my weekly engagement list! 🎉 Zainab Suleman, Abdullahi Hassan, Baka Aqkshz, Nafeesat Nafeesat, Hajiya Halima Muhammad, Ismail Oscar, Gemu Jinjawa, Muhammad Young, Asemi Modo, Hamidan Kamal, Zahara Umar, Abubakar Mukhtar, Maryam S Adam, Ibrahim Halil, Rabo Afiniki, Zainab Bello, Bappah Misau Mohammed, Mustapha Musa, Salim A Gwaska, Lydia Bitrus, Muhammad Yusuf, Surajo Basanya, Real Inna Sd Jamal, Oumar Lawan, Hafsat Aliyu, Abbakar Abbakar, Maii Kusanci, Sadiq Usman Sadiq Usman, Fatima Aliyu Mamman, Kadan Salame, Ali Mahamat Ousmane, Umar Aloma, Babangida Muhammat, Shaaba Kabrn, Atiku Hashim Wurno, Basir Idris Shu'aib

Harbin Bindiga Ya Jikkata Mata Da Namiji 1 a Yayin Wata Arangama A Kusa Da Asibitin Murtala KanoMata uku da namiji guda ...
17/05/2026

Harbin Bindiga Ya Jikkata Mata Da Namiji 1 a Yayin Wata Arangama A Kusa Da Asibitin Murtala Kano

Mata uku da namiji guda sun samu raunukan harbin bindiga yayin wani arangama da ya barke tsakanin jami’an hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi da wasu mutane a kusa da Asibitin Murtala da ke Kano.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa wadanda s**a jikkata sun hada da karamar yarinya da matar aure, inda aka garzaya da su zuwa sashen bayar da agajin gaggawa na Asibitin Murtala domin ceto rayuwarsu.

Majiyoyi sun ce ana ci gaba da kokarin cire alburushin da ya shiga jikin wasu daga cikin wadanda abin ya shafa.

Rahotanni sun kuma nuna cewa wadanda aka harba ba su da alaka da rikicin, domin mafi yawansu masu wucewa ne da kuma mata da ke zaune a kofar gidajensu lokacin da lamarin ya faru.

Sanata mai wakiltar Kebbi ta Kudu  ya sanar da  ficewarsa daga jami'iyar  Apc.Sanata Garba Musa Maidoki, wanda ke waƙilt...
16/05/2026

Sanata mai wakiltar Kebbi ta Kudu ya sanar da ficewarsa daga jami'iyar Apc.

Sanata Garba Musa Maidoki, wanda ke waƙiltar Kebbi ta Kudu a Majalisar Dattijai ta ƙasa sanar da ficewarsa daga APC .

Garba Musa Maidoki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar APC, a wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan watan 14 ga Mayu, 2026, da ya aika wa shugaban jami'iyar APC na mazabar Rafin Zuru.

A cikin wasiƙar Sanatan ya bayyana cewa " rikicin cikin gida na jam’iyyar ya kawo cikas ga burinsa na siyasa "

Sai dai ya gode wa APC bisa damar da ta ba shi na yin hidima ƙarƙashin tutar jam’iyyar.

A shekar 2023 ne aka zaɓi Garba Musa Mai doki Sanatan Kebbi ta Kudu a jami'yar PDP kafin daga bisani ya sauya sheƙa zuwa jami'yar APC.

Ficewar Maidoki na zuwa ne a dai dai lokacinda jami'iyyu ke cigaba da ƙoƙarin fitar da 'yan takarar da za fafata a babban zaɓen 2027.

Dabiru Kasmi Adamu.
#2027

WANNA RASHIN IMANI YAYI YAWA, IDAN KUN SAN BA ZA KU RIKE BA, KAR KU KARBA 😭😭😭A yau mai girma Kwamishiniyar Mata, Yara da...
14/05/2026

WANNA RASHIN IMANI YAYI YAWA, IDAN KUN SAN BA ZA KU RIKE BA, KAR KU KARBA 😭😭😭

A yau mai girma Kwamishiniyar Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Hannatu Suleiman Abba, ta kai ziyara garin Tsamiya da ke karamar hukumar Gezawa domin duba halin da wasu marayu suke ciki, wadanda aka karbo daga gidan yara na Nassarawa Orphanage Home.

Yayin ziyarar, Kwamishiniyar ta zubar da hawaye bayan ganin yadda wata mata da ta karbi yara guda biyu ke azabtar da su.

An kuma gano wani yaro dan shekara biyu da alamun kuna a bayansa, yayin da aka samu raunuka sama da guda ashirin a jikinsa.

A yanzu haka, Kwamishiniyar ta bada umarnin daukar mataki a kan matar, tare da dawo da yaran guda biyu. Haka kuma za a kai yaron da ke dauke da raunuka a jikinsa asibiti domin a duba lafiyarsa.

Hannatu Suleiman Abba

HISBAH TA K**A SAURAYI DA ‘YANMATA BIYU KAN ZARGIN AIKATA BADALA A DUTSIN-MAHukumar Hisbah reshen karamar hukumar Dutsin...
14/05/2026

HISBAH TA K**A SAURAYI DA ‘YANMATA BIYU KAN ZARGIN AIKATA BADALA A DUTSIN-MA

Hukumar Hisbah reshen karamar hukumar Dutsin-Ma a Jihar Katsina ta ce ta k**a wani saurayi da wasu ‘yanmata biyu bisa zargin yunkurin aikata badala a garin.

Hukumar ta ce kamen ya gudana ne a ranar 13 ga Mayu, 2026 karkashin jagorancin Kwamandan Hisbah na Dutsin-Ma, Shafi’u Ibrahim, bayan samun bayanan sirri.

A cewar hukumar, ta samu rahoton cewa ‘yanmatan na amfani da dakunan dalibai a matsayin wuraren fakewa domin aikata ayyukan da s**a saba da tarbiyya.

An ce jami’an Hisbah sun k**a su ne tare da saurayin a bayan gidan Radio da ke cikin garin Dutsin-Ma.

Hukumar ta kuma ce daya daga cikin ‘yanmatan na amfani da sunan Hisbah tana ikirarin cewa jami’ar hukumar ce domin samun kariya idan ta aikata laifi.

Sai dai hukumar ba ta bayyana sunayen wadanda aka k**a ba, ko kuma matakin da za a dauka a kansu.

ABIN TAUSAYI: Wadannan su ne iyalan gidan CSI Muttaka Lukman da wasu ‘yan bindiga s**a sace a daren jiya bayan sun kai h...
14/05/2026

ABIN TAUSAYI: Wadannan su ne iyalan gidan CSI Muttaka Lukman da wasu ‘yan bindiga s**a sace a daren jiya bayan sun kai hari gidansa da ke garin Kaura Namoda a Jihar Zamfara.

Maharan sun yi awon gaba da matansa biyu da kuma yaransa biyar, lamarin da ya jefa iyalai da mazauna yankin cikin jimami da alhini.

Hakika babu wani tashin hankali da ya fi wa mutum Musulmi magidanci radadi k**ar rasa iyalansa ta irin wannan hanya.

Muna rokon Allah SWT Ya kubutar da su cikin koshin lafiya da aminci, Ya kawo karshen wannan masifa da ta addabi al’umma, amin.

Yan bindiga sun sace dagaci da 'yarsa a KatsinaWasu yan bindiga dauke da manyan mak**ai sun kutsa cikin kauyen Kogari da...
13/05/2026

Yan bindiga sun sace dagaci da 'yarsa a Katsina

Wasu yan bindiga dauke da manyan mak**ai sun kutsa cikin kauyen Kogari da ke karamar hukumar Matazu a jihar Katsina, inda s**a sace Dagacin garin, Bello Abdulkarim, tare da diyarsa da wasu mazauna kauyen.

Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata yayin da mazauna garin ke gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

Wasu mazauna kauyen da s**a nemi a sakaya sunayensu sun shaida cewa maharan sun yi awon gaba da kimanin mutane goma, sai dai mutum hudu daga cikin wadanda aka sace sun samu nasarar kubucewa.

Majiyoyin sun ce a halin yanzu akalla mutane shida ne ke hannun yan bindigar.

Ko da yake ba a samu asarar rai ko raunuka ba yayin harin, mazauna yankin sun ce al’umma na cikin fargaba da zaman dar-dar sak**akon yawaitar hare-haren yan bindiga a yankunan Matazu da Musawa.

A cewar mazauna yankin, hare-haren na ci gaba da tilasta wa wasu iyalai barin garuruwansu domin neman mafaka a wuraren da suke ganin sun fi aminci.

Lamarin ya kuma sake tayar da tambayoyi daga wasu mazauna yankin kan tasirin sasancin da aka yi da wasu kungiyoyin yan bindiga a watannin baya.

IBTILA’I: Wani Matashi Dan Jihar Kano Ya Yanke Gabansa A LibyaWani matashi ɗan asalin Jihar Kano mai suna Sani, daga ung...
12/05/2026

IBTILA’I: Wani Matashi Dan Jihar Kano Ya Yanke Gabansa A Libya

Wani matashi ɗan asalin Jihar Kano mai suna Sani, daga unguwar Tukuntawa da ke ƙaramar hukumar Kumbotso, ya yanke gaban sa a ƙasar Libya inda ya je neman kuɗi.

Rahotanni sun ce matashin ya aikata hakan ne bayan ya kamu da larurar ƙwaƙwalwa a ƙasar.

Kakakin ƙungiyar Northern Nigerian Organization (NNO), ƙungiyar ’yan Arewacin Najeriya mazauna Libya, Abba Na-Gaida Fagge, ya shaida cewa matashin ya dade ya na fama da matsalar ƙwaƙwalwa.

A cewarsa, kafin faruwar lamarin, matashin ya tuka motar katafila a kamfanin da ya ke aiki inda ya rushe wani gini, lamarin da ya sa aka killace shi.

Fagge ya ce bayan an killace shi ne aka ji ya na ihu, sannan da aka duba aka tarar ya ji wa kansa mummunan rauni.

“Da aka kira mu muka zo, muka tarar ya jiƙe da jini. Muna dubawa muka ga ya yanke gaban sa, saura kaɗan ya cire gaba ɗaya,” in ji shi.

Ya ce nan take s**a haɗa kuɗi domin kai shi asibiti inda ake kula da lafiyarsa.

A cewarsa, likitoci za su yi masa aiki saboda sashen bai yanke gaba ɗaya ba.

Fagge ya kuma yi zargin cewa tun da farko sun sanar da ofishin jakadancin Najeriya da ke Libya game da halin da matashin ya ke ciki amma ba a ɗauki mataki ba.

Ya ce yanzu haka suna ƙoƙarin ganin an dawo da matashin gida Kano domin cigaba da kula da lafiyarsa.

-Daily Nigerian Hausa

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UNAn yi jana’izar mutum 5 da wasu ’yan bindiga s**a kashe a Tsohon Garin Yank**aye da ke...
12/05/2026

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN

An yi jana’izar mutum 5 da wasu ’yan bindiga s**a kashe a Tsohon Garin Yank**aye da ke ƙaramar hukumar Tsanyawa a Jihar Kano.

An gudanar da jana’izar mamatan ne k**ar yadda addinin Musulunci ya tanada, inda al’umma s**a taru domin yi musu addu’ar samun rahama da gafarar Allah SWT.

Mazauna yankin sun bayyana alhini da jimamin wannan hari, tare da roƙon Allah ya kawo ƙarshen matsalar tsaro da ke addabar al’umma.

Ya Allah ka jikansu da rahama, ka kawo mana zaman lafiya mai ɗorewa. Ameen.

An Samu Hatsari A Gadar Lado Da Ke KanoWani hatsari ya afku a safiyar yau a gadar Ado Bayero da aka fi sani da Gadar Lad...
11/05/2026

An Samu Hatsari A Gadar Lado Da Ke Kano

Wani hatsari ya afku a safiyar yau a gadar Ado Bayero da aka fi sani da Gadar Lado a cikin birnin Kano.

Rahotanni sun bayyana cewa, wata motar tirela ɗauke da mashinan adaidaita sahu ce ta yi taho-mu-gama da wata mota ƙirar Honda tare da wani babur mai ƙafa biyu a daidai gadar.

Lamarin ya jawo cunkoso da tashin hankali a yankin, inda jama’a da masu ababen hawa s**a tsaya domin ganin yadda abin ya faru, yayin da wasu ke ƙoƙarin taimakawa wajen daidaita zirga-zirga.

Address

Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muhimmiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share