22/05/2026
Kotu ta ɗage shari'ar Zargin almundahanar kuɗaɗen Naira Biliyan 8.7 da ake ma tsohon ministan Shari'a zuwa 23 ga watan Yuni.
Mai sharia'a Joyce Abdulmalik na babbar kotun tarayya dake Maitama Abuja , ya ɗage shari'ar da ake yi ta zargin almundahnar kudaden Naira Biliyan 8.7 da ake zargin tsohon Ministan Shari'a Abubakar Malami , SAN da matarsa Hajiya Bashir Asabe da kuma ɗan sa Abdulaziz Malami
Hukumar EFCC ce ta shigar da ƙarar da ta ƙunshi tuhume tuhume 16, da s**a haɗa da haɗa baki , ɓoyewa da karkatar da kuɗaɗe haɗi da almundahnar kuɗaɗe da sauran wasu haramtattu abubuwa waɗanda s**a saɓawa tanadin dokar hana almundahanar kuɗaɗe ta shekar 2022.
A zaman kotun na ranar Juma’a, lauyan masu shigar da kara, J.S. Okutepa, SAN, ya sanar da kotu cewa yaune ranar ci gaba da sauraron shari’ar, amma masu shigar da kara sun karɓi wasiƙa daga bangaren lauyoyin masu bada kariya na neman a dage zaman.
Ya bayyana cewa " yaune aka tsara cigaba da sauraron wannan shari’a ne An ma an ba mu wasiƙa ta hannun Rijistar Kotun a ranar 20 ga Mayu, 2026, daga lauyoyi bada kariya na J.B. Daudu . Mun so mu kaucewa buƙatar dagewar, amma ba mu so mu kawo naƙasu ga cigaba da gudanar shari’ar.”
Ya ƙara roƙon kotu ta lura da yawan lokutan da masu karewa s**a nemi a dage shari’ar.
A hukuncinta, Mai Shari’a Abdulmalik ta amince da buƙatar lauyan masu shigar da kara, inda ta ce rashin halartar babban lauyan waɗanda ake ƙara bai k**ata ya dakile zaman ba, musamman la’akari da yawan lauyoyin da gudanar da shari'ar.
Tace “Na amince da bukatar ka , babban lauya ta cewa lauyan waɗanda ake ƙara yana da lauyoyi da yawa , babu pp 0pí dalilin dakile zaman a yau. Amma tunda suna da damar neman dage shari'ar sau biyar, za mu amince da wannan sau ɗaya,” in ji maisharia
Saboda haka, kotun ta dage shari’ar zuwa 23 ga Yuni, 2026 domin ci gaba da saurara, k**ar yadda babban lauyan waɗanda ake ƙara ya gabatar.
Dahiru Kasimu Adamu