Muhimmiya

Muhimmiya Media/News Company

DA DUMI-DUMI: Alƙalin Babbar Kotun Kebbi da Aka Sace Ya Samu 'YanciAlƙalin Babbar Kotun Jihar Kebbi, Mai Shari'a Faruku ...
03/08/2026

DA DUMI-DUMI: Alƙalin Babbar Kotun Kebbi da Aka Sace Ya Samu 'Yanci

Alƙalin Babbar Kotun Jihar Kebbi, Mai Shari'a Faruku Hassan Bunza, wanda wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne s**a sace daga gidansa da ke Ƙaramar Hukumar Bunza a ƙarshen watan Yuli, ya samu 'yanci.

Har yanzu dai ba a bayyana yadda aka kuɓutar da alkalin ba, kuma hukumomin tsaro ba su fitar da cikakken bayani kan ko an biya kuɗin fansa kafin a sake shi ba.

Ana sa ran hukumomin da abin ya shafa za su yi ƙarin bayani kan yadda aka samu nasarar kuɓutar da Mai Shari'a Bunza.

Muhimmiya za ta ci gaba da bibiyar lamarin tare da kawo muku ƙarin bayani da zarar an samu.

Dan marigayi tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari wato Yusuf Buhari da mai ɗakinsa, Zahra Nasir Ado Bayero, sun sanar d...
31/07/2026

Dan marigayi tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari wato Yusuf Buhari da mai ɗakinsa, Zahra Nasir Ado Bayero, sun sanar da samu ƙaruwa na ƴa mace..

Ku taya su murna

Shin wakar Rarara da yayi ga Sheikh Pantami, masoya ta karawa malamin ko makiya?Ku bayyana mana ra'ayinku a comment
31/07/2026

Shin wakar Rarara da yayi ga Sheikh Pantami, masoya ta karawa malamin ko makiya?

Ku bayyana mana ra'ayinku a comment

Hisbah ta haramta DJ, Wazigidi, kayan "See I Love" da wasu al'adu a bukukuwan aure a SakkwatoHukumar Hisbah ta Jihar Sak...
28/07/2026

Hisbah ta haramta DJ, Wazigidi, kayan "See I Love" da wasu al'adu a bukukuwan aure a Sakkwato

Hukumar Hisbah ta Jihar Sakkwato ta haramta wasu nau'o'in al'adu da ayyukan da ta ce sun sabawa tarbiyya da kyawawan ɗabi'u a bukukuwan aure da sauran tarukan jama'a a faɗin jihar.

Sanarwar, wadda ta fara aiki daga yau Litinin, ta haɗa da haramta sanya kayan da aka fi sani da "See I Love", kaɗe-kaɗen DJ da Wazigidi, da kuma yin obalodi tare da ɗora lasifika ko ƙara sauti a kan baburan Adaidaita Sahu (Keke Napep).

Hukumar ta kuma haramta abin da ta kira askin banza ga yara da matasa, tare da tsaurara ko wuce gona da iri wajen kayan lefe.

Da yake jawabi ga manema labarai a hedikwatar hukumar da ke Sakkwato, Kwamandan Hukumar Hisbah ta Jihar Sakkwato, Malam Usman Abdullahi Jatau, ya ce matakin na daga cikin ƙoƙarin tsaftace al'umma da inganta tarbiyya da kyawawan ɗabi'u.

Ya yi kira ga al'ummar jihar da su ba hukumar cikakken haɗin kai domin tabbatar da aiwatar da sabbin matakan.

Jatau ya ƙara da cewa Hukumar Hisbah za ta ci gaba da ɗaukar matakan da s**a dace bisa doka kan duk wanda ya saɓa wa waɗannan umarni domin kare tarbiyya da kyawawan al'adun al'ummar Jihar Sakkwato.

Budurwa ta yanke mazakutar saurayinta a otal da ke KanoRundunar 'Yan Sandan Jihar Kano ta tabbatar da k**a wata budurwa ...
27/07/2026

Budurwa ta yanke mazakutar saurayinta a otal da ke Kano

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kano ta tabbatar da k**a wata budurwa mai shekaru 25 da ake zargi da yanke mazakutar saurayinta yayin da yake barci a wani otal da ke unguwar Badawa a Kano.

Kakakin rundunar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce lamarin ya faru da misalin ƙarfe 12 na ranar Litinin, bayan samun rahoton abin da ya faru.

Ya bayyana cewa duk da masoyan biyun 'yan asalin Jihar Jigawa ne, lamarin ya faru ne a Kano.

A cewarsa, binciken farko ya nuna cewa wadda ake zargin ta zo daga Maigatari da wata wuka, wadda ake zargin ta yi amfani da ita wajen aikata laifin.

Kiyawa ya ce matar ta shaida wa 'yan sanda cewa ta aikata lamarin ne yayin da saurayin nata ke barci bayan ya sha maganin ciwon kai, wanda ya sa ya yi barci mai nauyi.

Ya ce bayan faruwar lamarin, ana zargin ta ja saurayin zuwa banɗaki domin wanke jinin kafin mutanen da ke wajen s**a fahimci abin da ke faruwa tare da sanar da jami'an tsaro.

Dangane da rade-radin cewa an yi amfani da wani sinadari ko kayan maye, kakakin rundunar ya ce har yanzu babu wata hujja da ke tabbatar da hakan.

Ya ƙara da cewa jami'an 'yan sanda sun samu kwalbar Lacasera da ruwa a ɗakin, kuma ana ci gaba da bincike domin gano ko suna da alaƙa da lamarin.

Kiyawa ya tabbatar da cewa saurayin na raye kuma yana karɓar magani a asibiti.

Ya ce wadda ake zargin tana tsare a hannun 'yan sanda, yayin da bincike ke ci gaba kafin gurfanar da ita a gaban kotu.

-Daily Nigerian

Yanbindiga sunyi garkuwa da shugaban  karamar hukuma a Zamfara, kuma sun kashe jamian tsaronsaA cikin darennan, Yan bind...
25/07/2026

Yanbindiga sunyi garkuwa da shugaban karamar hukuma a Zamfara, kuma sun kashe jamian tsaronsa

A cikin darennan, Yan bindiga sun Sace shugaban karamar hukumar Bungudu dake jihar Zamfara, bayan sun harbe yan sanda guda biyu dake gadinsa da wani wanda ake kira ADC, sun kuma Jima wansa rauni.

Yan ta'addan Sunyi nasarar tafiya da Shugaban karamar hukumar ta Bungudu, tare da yayansa da matarsa.

Sai dai rahotannin da muke samu na nuna cewa matarsa da yayansa sun kubuta daga baya, Matar shugaban karamar hukumar ta tabbatar da cewa: "Ɓarayin su s**a sako su da kansu, s**ace: 'Dama mijinta dai s**a zo
Dauka kuma sun ɗauka'"

Muna rokon Allah ya kawo muna karshen wannan masifa.

- Lecturer Aminu Muhammad Kaura

Hotunan Gawarwakin wadanda aka kashe a ZamfaraYayin da kowa ya yi shiru, 'yan bindiga sun kashe manoma 23 a ƙauyen Sauna...
24/07/2026

Hotunan Gawarwakin wadanda aka kashe a Zamfara

Yayin da kowa ya yi shiru, 'yan bindiga sun kashe manoma 23 a ƙauyen Sauna/Ruwan Gora da ke Ƙaramar Hukumar Talata Mafara a Jihar Zamfara. Sama da mutum 50 ne aka kwantar a asibiti, yawancinsu mata da yara.

Wannan harin ya faru ne a wani ƙauye da ke kusa da garin da Ministan Tsaro na Ƙasa (Karamin Minista), Bello Matawalle, ya fito. Yankin Arewa maso Yamma na ƙara zama tamkar makabarta, amma duk da haka wahalhalun da al'ummarsa ke fuskanta na ci gaba da samun kulawa kaɗan daga masu ruwa da tsaki.

-Idris Mohammed

Ku kalli gawarwakin Mutum 24 da yan bindiga s**a yiwa yankan rago a Kauyen Sauna dake Ƙaramar Hukumar Talatar Mafara ta ...
23/07/2026

Ku kalli gawarwakin Mutum 24 da yan bindiga s**a yiwa yankan rago a Kauyen Sauna dake Ƙaramar Hukumar Talatar Mafara ta jihar Zamfara.

Kungiyar kare hakkin dan adam ta Amnesty International tayi Allah wadai da irin wannan kisa da ake yiwa alumma babu gaira babu dalili

Allah ya kawo mana karshen matsalar tsaron da ta addabemu.

Ƴan bindiga sun kashe Shugaban Ƴan Agajin Ƙungiyar Jama'atu Izalatil Bid'ah Wa'iqamatis Sunnah (JIBWIS) na karamar Ƙanƙa...
16/07/2026

Ƴan bindiga sun kashe Shugaban Ƴan Agajin Ƙungiyar Jama'atu Izalatil Bid'ah Wa'iqamatis Sunnah (JIBWIS) na karamar Ƙanƙara ta Jihar Katsina, Malam Surajo Kamilu.

Rahotanni sun ce an kashe Malam Surajo Kamilu ne a wani hari da ƴan bindiga s**a kai a lokacin da yake aiki a gonarsa, lamarin da ya jefa al'ummar yankin cikin jimami.

Da fatan Allah ya gafarta masa.

An kashe direban tankar mai, an ƙone motarsa a harin 'yan bindiga a ZamfaraWasu 'yan bindiga sun kashe wani direban tank...
12/07/2026

An kashe direban tankar mai, an ƙone motarsa a harin 'yan bindiga a Zamfara

Wasu 'yan bindiga sun kashe wani direban tankar mai mai suna Abubakar N.D.A tare da ƙona tankar man da yake tukawa a wani hari da s**a kai a kan hanyar Gurusu zuwa Anka, a kusa da Gadar Manya da ke Jihar Zamfara.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Lahadi, inda maharan s**a tare hanyar kafin su buɗe wa direban wuta, lamarin da ya yi sanadin mutuwarsa nan take.

Majiyoyi sun ce marigayin na cikin direbobin Alhaji Siddi Ɗaki Takwas.

Wannan yaron da kuke gani a hoton ɗan marigayin ne, tsaye kusa da gawarsa, abin da ya jawo alhini a tsakanin jama'a.

Har zuwa lokacin wallafa wannan rahoto, jami'an tsaro ba su fitar da wata sanarwa kan harin ba.

Allah Ya jiƙan marigayin, Ya ba iyalansa da sauran al'umma haƙurin jure wannan rashi.

-Anas Villa

Address

Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muhimmiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share