Muhimmiya

Muhimmiya Media/News Company
(1)

25/12/2025
24/12/2025
EFCC Ta Gano Kadarori 41 Masu Darajar Naira Biliyan 212 Na MalamiHukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta EFCC ta gano ka...
24/12/2025

EFCC Ta Gano Kadarori 41 Masu Darajar Naira Biliyan 212 Na Malami

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta EFCC ta gano kadarori guda 41 da ake alakanta wa Abubakar Malami, tsohon Ministan Shari’a kuma Lauyan Gwamnatin Tarayya.

Muhimmiya ta samu rahoton cewa kadarorin sun hada da otal-otal, gidajen zama, filaye, makarantu da kuma wurin buga takardu, wadanda ke fadin jihohin Kebbi, Kano da Babban Birnin Tarayya Abuja.

Darajar kadarorin da ke jihar Kebbi ta kai Naira biliyan 162 da miliyan 195, yayin da na jihar Kano s**a kai Naira biliyan 16 da miliyan 11. A bangaren Babban Birnin Tarayya kuwa, an kiyasta darajar kadarorin da Naira biliyan 34 da miliyan 685.

Muhimmiya Labarai Masu Ma'ana

Akpabio Ya garzaya Kotun Ƙoli domin kalubalantar Hukuncin Kotun Daukaka Kara Kan Dakatar da NatashaShugaban Majalisar Da...
22/12/2025

Akpabio Ya garzaya Kotun Ƙoli domin kalubalantar Hukuncin Kotun Daukaka Kara Kan Dakatar da Natasha

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya shigar da daukaka Kara a gaban Kotun Ƙoli kan hukuncin da Kotun Daukaka Ƙara (Court of Appeal), Abuja, ta yanke akan shari’ar Natasha Akpoti-Uduaghan, sanata mai wakiltar Kogi ta tsakiya.

Hakan ya biyo bayan hukuncin kotun daukaka karar da aka yanke a ranar 28 ga Nuwamba, 2025, a karar dake da lamba CA/ABJ/CV/1107/2025, inda aka soke dakatarwar da aka yiwa Sanata Natasha daga Majalisar Dattawa karkashin jagorancin Akpabio.

Me za ku Ce?

Muhimmiya – Labarai Masu Ma’ana.

Tinubu Ya Gargadi ‘Yan Najeriya Kan Shan Barasa A Lokacin KirsimetiShugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya gargaɗi ‘yan Najer...
22/12/2025

Tinubu Ya Gargadi ‘Yan Najeriya Kan Shan Barasa A Lokacin Kirsimeti

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya gargaɗi ‘yan Najeriya da su guji shan barasa a yayin bukukuwan Kirsimeti, domin kare lafiyarsu da kuma gujewa tashin hankali.

Tinubu ya yi wannan gargadi ne yayin da ya halarci taron gargajiya na “Ijade Opa Eyo” a birnin Legas, wanda ke nuna shirin fara shahararren bikin Eyo a jihar.

Ya bukaci jama’a da su gudanar da bukukuwan cikin natsuwa da ɗa’a, tare da mutunta dokoki da al’adun al’umma.

Muhimmiya – Labarai Masu Ma’ana.

An Saki Sauran Dalibai da Malaman Makarantar St. Mary’s da Aka Sace a Jihar NigerRahotanni dake fitowa na nuni da cewa a...
21/12/2025

An Saki Sauran Dalibai da Malaman Makarantar St. Mary’s da Aka Sace a Jihar Niger

Rahotanni dake fitowa na nuni da cewa an saki sauran dalibai da malamai na makarantar St. Mary’s Catholic School, Papiri, da ke karamar hukumar Rafi a jihar Niger, wadanda aka sace a kwanakin baya.

Muhimmiya ta gano cewar sakin nasu ya biyo bayan kiran gaggawa da iyayen yaran s**a yi ga gwamnatin tarayya da ta jihar Niger, inda s**a bukaci a tabbatar da ‘ya’yansu sun dawo gida kafin ranar Kirsimeti, 25 ga Disamba.

Wani jami’in tsaro da ke da masaniya kan aikin ceto ya shaida wa jaridar Premium Times cewa, dukkan mutanen da aka sace a harin yanzu sun samu ‘yanci. Sai dai ya ce ba a tantance adadin wadanda aka saki a sabon rukunin ba.

Idan ba'a manta ba ‘yan bindiga sun kai hari a makarantar da tsakar dare a ranar 21 ga Nuwamba, 2025, inda s**a shiga harabar makarantar a kan babura.

Rahotanni sun ce sun shafe kusan awanni uku suna zagaya ɗakunan kwanan dalibai kafin su tafi da wadanda s**a sace zuwa dazuzzuka da ke kusa.

Har zuwa lokacin hada wannan labari, gwamnatin tarayya da ta jihar Niger ba su fitar da wata sanarwa a hukumance ba kan batun.

Lamarin ya sake tunatar da jama’a irin hare-haren satar dalibai da s**a taba faruwa a wasu sassan Najeriya, ciki har da shahararren harin Chibok a jihar Borno.

Muhimmiya – Labarai Masu Ma’ana.

Gobara ta tashi cikin dare a kasuwar masu aiki da katako da ke Tal’udu a birnin Kano, inda ta ƙone dukiya mai yawa.Shaid...
21/12/2025

Gobara ta tashi cikin dare a kasuwar masu aiki da katako da ke Tal’udu a birnin Kano, inda ta ƙone dukiya mai yawa.

Shaidun gani da ido sun ce gobarar ta tashi da misalin ƙarfe 2:30 na dare, kuma ta ci gaba da bazuwa na tsawon awanni.

Wutar ta shafi shagunan masu furnitures da ke kusa da gidan man WAA Rano kan hanyar Goron Dutse, inda aka ce gobarar ta yi ƙamari kafin a samu nasarar shawo kanta.

Ya zuwa yanzu dai, ba a kai ga tantance yawan asarar da gobarar ta haifar ba, kuma babu rahoton rasa rai. Inda bayanai s**a nuna cewar kaso 9 cikin 10 Basu fita da komai ba.

Muhimmiya na ci gaba da bibiyar bayanai kan lamarin.

Allah shi kiyaye gaba, ya kuma mayar masu da mafi alkhairin abinda s**a rasa.

Arewa Updates

Tinubu ya karrama Sheikh Dahiru Bauchi da sauya sunan Jami’ar AzareShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya karrama marigayi f...
20/12/2025

Tinubu ya karrama Sheikh Dahiru Bauchi da sauya sunan Jami’ar Azare

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya karrama marigayi fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Dahiru Bauchi, ta hanyar sauya sunan Jami’ar Kiwon Lafiya ta Tarayya da ke Azare, Jihar Bauchi, zuwa sunansa.

Tinubu ya bayyana hakan ne a Bauchi yayin ziyarar ta’aziyya da ya kai wa iyalan marigayi malamin, inda ya yabawa gudunmawar da ya bayar wajen hidimar addini, al’umma da ƙasa.

Shugaban ya ce koyarwar Sheikh Dahiru Bauchi kan gaskiya da kyawawan ɗabi’u sun yi tasiri ga al’umma a faɗin Najeriya.

Ya kuke ganin tasirin sauya sunan ga wannan Jami'ar?

Da fatan Allah ya gafarta masa, Ameen.

Yanzu-yanzuShugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya umarci rundunar ’yansanda da ta janye dukkan ’yan sandan da ke tsaron many...
23/11/2025

Yanzu-yanzu

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya umarci rundunar ’yansanda da ta janye dukkan ’yan sandan da ke tsaron manyan mutane (VIPs), domin a mayar da su kan aikin kare rayuka da dukiyoyin jama’a a faɗin ƙasar.

Muhimmiya ta ruwaito cewa, shugaban ya bayyana cewa duk wani babban mutum da ke buƙatar tsaron kai-tsaye daga yanzu ya nemi Hukumar Civil Defence (NSCDC) ta tanadar masa da jami’anta, ba ’yan sanda ba.

Ya nanata cewa aikin ’yan sanda ya koma kan jama’a, ba VIP ba.

Majiyar: Daily Trust

Yanzu-Yanzu: Kimanin Yara 50 Sun Kuɓuta Daga Hannun Ƴan Bindiga a Jihar NejaKimanin yara hamsin daga cikin ɗaliban makar...
23/11/2025

Yanzu-Yanzu: Kimanin Yara 50 Sun Kuɓuta Daga Hannun Ƴan Bindiga a Jihar Neja

Kimanin yara hamsin daga cikin ɗaliban makarantar cocin Katolika da ke jihar Neja sun kuɓuta daga hannun ƴan bindigar da s**a yi garkuwa da su, a cewar Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen jihar Neja.

A cewar CAN, yaran na daga cikin waɗanda aka sace daga St. Mary’s Catholic Primary da Secondary School da ke garin Papiri, ƙaramar hukumar Agwara. Rahoton ya ce suna tserewa ne a tsakanin Juma’a da Asabar, inda daga bisani aka miƙa su ga iyayensu a ɓoye domin tsaron lafiyarsu.

Shugaban CAN na jihar Neja, kuma Bishop ɗin Katolika na Kontagora Diocese, Bulus Dauwa Yohanna, shi ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.

Majiya: Daily Trust

Original Ƙafar da ta Ƙi Yin Fari 😂 Lokacin da sauran jikina ya fara canza launi, sai ƙafata ta ce: “Ni gaskiya ba zan bi...
23/10/2025

Original Ƙafar da ta Ƙi Yin Fari 😂

Lokacin da sauran jikina ya fara canza launi, sai ƙafata ta ce: “Ni gaskiya ba zan biye maku domin in yi fari ba. Na fi son in zauna yadda halittata take!” 😅

Tun daga lokacin, duk jikina ya koma launin turawa, amma ita ta tsaya daram a launin ta na asali tana cewa: “Kuyi naku, ni dai original ce.” 🤣

Wani ya ce, “Ai wannan ƙafa tana da girman kai bata son farin jiki, sai farin rai!” 😂

Wanne darasi kuke ganin za a iya ɗauka daga wannan ƙaramin labari? 🤔

“Haɗin kai tsakanin gwamnati da jami’an tsaro shi ne mabuɗin zaman lafiya. Gwamna Radda ya yaba da jajircewar Sojojin Na...
23/10/2025

“Haɗin kai tsakanin gwamnati da jami’an tsaro shi ne mabuɗin zaman lafiya. Gwamna Radda ya yaba da jajircewar Sojojin Najeriya wajen kare rayukan al’umma a Katsina.”💪🇳🇬

An samo daga: HQ Nigeria Army


🟩 * — Labarai Masu Ma’ana*

Address

Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muhimmiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share