Muhimmiya

Muhimmiya Media/News Company
(1)

Allah ya jiƙan sa, ya kyautata makwancinsa. Wani bawan Allah ne da ya gamu da iftilain gobara a cikin mota, wanda ya jan...
15/09/2025

Allah ya jiƙan sa, ya kyautata makwancinsa.

Wani bawan Allah ne da ya gamu da iftilain gobara a cikin mota, wanda ya janyo masa mummunan rauni har ya rasa ransa kwana guda bayan da hukumar NEMA ta taimaka masa.

Mun ziyarci kauyensu da ke cikin ƙaramar hukumar Sumaila dake jihar Kano,inda muka kai wa iyalansa tallafin kayan abinci domin rage musu ɗan radadin rashin da s**a yi.

Insha Allahu, Aikawa Charity Foundation za ta ɗauki nauyin karatun ɗa/’ya da ya bari tare da ci gaba da tallafa musu lokaci zuwa lokaci.

Muna roƙon Allah Madaukakin Sarki ya gafarta masa, ya rahamce shi, ya sanya shi cikin rahamarSa.

✍️✍️✍️ Aikawa Charity Foundation










“An Nada Shi Sarkin Makara a Kankiya!” Idan aka ce hidima ga al’umma tana da lada, to ga shaida! Wannan bawan Allah an n...
14/09/2025

“An Nada Shi Sarkin Makara a Kankiya!”

Idan aka ce hidima ga al’umma tana da lada, to ga shaida! Wannan bawan Allah an nada shi Sarkin Makaran Kankiya saboda aikin da ya ɗauka a matsayin nasa Aikin ladar: dauko makara idan aka yi rasuwa, kuma bayan an gama ya mayar da ita gida.

Ko da nisan gari, ko da ruwan sama, babu abin da zai hana shi zuwa ya cika wannan aiki. Wannan jajircewa ta sa aka karrama shi da wannan muƙami na musamman.

Shin ku fa, kun taɓa ganin sarauta irin wannan? Kuma kuna ganin ya dace a ƙara masa wani lada dabam?

Ku faɗa mana ra’ayin ku👇

ALLAH MUN TUBA😭😭😭😭.Wata baiwar Allah tsakar daren jiya ta aikomin da kudi naira dubu dari biyar tace in bayar duk inda n...
13/09/2025

ALLAH MUN TUBA😭😭😭😭.

Wata baiwar Allah tsakar daren jiya ta aikomin da kudi naira dubu dari biyar tace in bayar duk inda nags dama.

Da farko nayi tunanin mu siyo kayan abinci mu rabawa iyayen marayu, kawai sai na fasa.

Naira dubu 20 na ware sau 25. Na shiga shiga lunguna da bakin t**i.

Yammata na samu masu sanaaar awara da kosai da dankali.

Kowacce na bata dubu 20.

Kaf acikin wadanda na baiwa babu wacce bata zubar da hawayen murna da farin ciki ba.

Da yawansu marayune rayuwace ta galabaitar dasu babu mai taimakonsu sai Allah.

Da yawansu suna cikin musibar rayuwa, wallahi wata jarinta ko naira dubu biyar bai kai ba, a haka suke.

Wata yarinya da na jira man da take suyar gwangwani dayan ina bata ta zube a ƙasa tana kuka da godiya.

Wata budurwa kuwa kafata ta rike tana zubarda hawaye.

Don Allah idan mun sami dama mu dinga agaxawa irin wadannan yaran suna cikin musibar rayuwa.

Idan bamuda abinda zamu tallafa musu kada mu cutar dasu.

✍️✍️✍️✍️

SANI ROGO AIKAWA

CEO AIKAWA CHARITY FOUNDATION.
08082744019

TIRKASHISababbin hotunan mawaki Soja Boy tare da shahararriyar jarumar kafar sanarwar Zamani wato Rahama Sa’idu sun taya...
12/09/2025

TIRKASHI

Sababbin hotunan mawaki Soja Boy tare da shahararriyar jarumar kafar sanarwar Zamani wato Rahama Sa’idu sun tayar da kura a kafafen sada zumunta.

An hango su suna musabaha tare da rungumar juna abin da ya haddasa rarrabuwar ra’ayi tsakanin masoya da masu s**a.

Wasu na cewa: "Ba komai bane, zumunci da soyayya ce kawai.” Amma wasu kuma sun yi tir da cewa: "Wannan ya saba da tarbiyya da mutuncin al’ada!"

Yanzu haka Facebook, Instagram da TikTok sun cika da cece-kuce wasu na dariya, wasu kuma suna tsinewa .

Me kuke gani?
- Shin rungumar ta dace ne a bainar jama’a?
- Ko kuwa kawai ana neman jan hankali ne don a tada jijiyar wuya?

- Kuna goyon baya ko adawa?

Ku bar mana ra’ayoyinku👇

Tsakanin Uwa da Danta Sai Allah 😭 Wannan da kuke gani kwance a gadon asibiti shi ne babban ɗan wannan uwa mai rauni. Ya ...
12/09/2025

Tsakanin Uwa da Danta Sai Allah 😭

Wannan da kuke gani kwance a gadon asibiti shi ne babban ɗan wannan uwa mai rauni. Ya fita neman abinci domin iyalinsa, amma tsautsayi ya same shi kashin bayansa ya karye, lakarsa ta tsinke.

Tsawon watanni biyu ana neman kuɗin aikin tiyata har naira Miliyan uku da rabu (₦3.5m), babu. Sai ranar da muka same shi a asibiti, a ranar muka biya kudin aikin.

Amma kalubale bai tsaya nan ba zuwa yanzu jinyarsa ta kai kusan Miliyan 5. Sai kuma aka nemi kuɗin kujera, gashi, magani da abinci kusan Dubu 700k, babu!

Mun tashi tsaye muka biya, aka siyo kujerar tare da kayan abinci Yaron ya cika da murna da farin ciki, mahaifiyarsa kuma ta fashe da kukan murna.

Allah Ya bashi lafiya, Ya hadamu a cikin ladar baki ɗaya.

✍️ Aikawa Charity Foundation

RASHIN KAYAN ƊAKI YASA ANATA ƊAGA BIKIN YARA UKKU Daga:  Aminu KabirAllah ya sani, kullum ana kawo koke kan rashin kayan...
12/09/2025

RASHIN KAYAN ƊAKI YASA ANATA ƊAGA BIKIN YARA UKKU

Daga: Aminu Kabir

Allah ya sani, kullum ana kawo koke kan rashin kayan ɗaki ga ’yan mata da za a aurar, amma saboda yanayin rayuwar yau sai mutum ya kasa sanin yadda zai yi.

Yanzu haka yara guda uku lokacin aurensu ya yi, iyayensu sun yi iya bakin ƙoƙarinsu amma abin ya ci tura.

Daya daga cikinsu saura sati biyu bikin aurensa, kuma ango ya ce idan aka ƙara ɗagawa, shi zai hakura gaba ɗaya.

Yan uwa don Allah, kar mu bari wannan auren ya faskara saboda ƙaramin kayan ɗaki. Ku taimaka da abin da Allah ya h**e muku.

Idan ana buƙatar magana kai tsaye da iyayen yaran, a tuntube ni zan bada contact ɗin su kai tsaye.

Allah Ya sa taimakonku ya zame muku gatari a duniya da lahira.


😁🙏

YADDA IYALIN WANI LADANIN MASALLACI S**A SAMU KANSU BAYAN RASUWARSA 😭😭😭 Ina tsaye a wata majalisa sai na hango yarinya ƙ...
12/09/2025

YADDA IYALIN WANI LADANIN MASALLACI S**A SAMU KANSU BAYAN RASUWARSA 😭😭😭

Ina tsaye a wata majalisa sai na hango yarinya ƙarama yar shekara 9 zuwa 10 tana tallar mangwaro tana kuka, tana tafiya da kyar.

Na tambayi mutane a wurin me ya sa yarinyar ke kuka? S**a ce wai ba ta da kirki, duk lokacin da aka ɗora mata tallah haka take kuka.

Amma zuciyata ta ce “Bari inji dalili.” Na kusanto ta, sai na tambaye ta farashin mangwaron. Ta ce guda ɗaya ₦50 ne. Duk da haka, fuskarta babu annuri sai kuka kawai.

Na sayi dukkan mangwaron da kudinsa ya k**a ₦2,300. Nan take fuskarta ta chanza. Mun jima muna hira, sai ta ce min ba tallah ke sata kuka ba, ciwon ciki ne da take fama da shi tsawon watanni uku.

Na tambaye ta inda iyayenta suke. Ta ce mahaifinta ya rasu, mahaifiyarta kuma tana kwance a gida babu lafiya.

Na ce mu tafi gidan su. A mintuna kaɗan muka isa. Ashe uwar ma tana kwance tsawon lokaci, ba lafiya, gidan kuma k**ar bola ga kazanta, babu katanga.

An ce mahaifinsu mutumin kirki ne mai kiran Sallah. Amma duk da haka babu wanda ya taɓa kula da iyalansa ko kai musu taimako.

Na ɗauke su zuwa asibiti. Bayan gwaje-gwaje aka gano cewa hanjin yarinyar ya lalace saboda rashin kula da typhoid, ita kuma uwar tana da fibroid mai tsanani.

Aka yi musu aiki da kuɗi ₦560,000, cikin kwana biyu aka kammala. Bayan mako guda aka sallame su daga asibiti, aka ci gaba da basu abinci da magani har s**a murmure.

Bayan haka aka gyara gidan su gaba ɗaya ya koma sabo, aka saka yaran makaranta, aka kawo musu kayan sana’a don kada su sake komawa tallah.

Amma abin takaici, sai na ji maganganun mutanen gari wai dan majalisa ne ya turoni na yi musu taimako. 😔 Alhali basu taɓa zuwa ko kai musu magani ko bulo don rufe katangar gida ba.

Yarinya da aka ce “ba ta da kirki”, ashe rashin lafiya ce ke damunta. Mahaifiyar da take kwance a gida, babu wanda ya taɓa tunanin kai ta asibiti.

Rayuwa ta lalace idan har zuciyar mutane ta bushe da tausayi haka. Allah ya kyauta.

✍🏽Sani Rogo Aikawa

CEO/ Aikawa Charity Foundation
08082744019

SANARWA MAI MUHIMMANCI Jama’a don Allah muna cigiyar Khadija Ibrahim Abdullahi, ’yar Chairman Ibrahim Dan Amarya Yakasai...
11/09/2025

SANARWA MAI MUHIMMANCI

Jama’a don Allah muna cigiyar Khadija Ibrahim Abdullahi, ’yar Chairman Ibrahim Dan Amarya Yakasai (Haure Gidan Radio).

Ta bar gida ne yau da safe da niyyar zuwa School of Technology (SOT) Kano, amma har yanzu ba ta dawo ba.

Duk wanda ya ganta ko ya ji wani labari game da ita, don Allah ya sanar da hukuma mafi kusa, ko kuma ya tuntube mu a wadannan lambobin: 08035577850 / 08050300213

Yan uwa ku sanya ta cikin addu’a, Allah ya bayyana ta lafiya cikin aminci. Ameen.

🌊 Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje, Gonakai da Makaranta a wasu kauyukan Jihar Katsina Rahotanni daga karamar hukumar Bat...
11/09/2025

🌊 Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje, Gonakai da Makaranta a wasu kauyukan Jihar Katsina

Rahotanni daga karamar hukumar Batsari da ke Jihar Katsina , sun bayyana cewar mamakon ruwan sama ya jawo mummunan iftila’i na rushewar gidaje da dama, asarar dukiya, lalacewar gonakai da kuma rushewar makarantar Islamiyya a ƙauyukan Baƙon Zabo da Salihawa Daƙamna.

Wani mazaunin garin ya bayyana cewa wannan ambaliyar ta tilasta gomman mutane barin muhallansu, tare da barin maƙabartu a cikin yanayin zaizayewa.

Wannan lamari dai ya sanya al’ummar yankin cikin halin matsi da fargaba, inda suke roƙon gwamnatin jihar da masu hannu da shuni da su gaggauta kai masu ɗauki.

Al’ummar na ci gaba da addu’ar neman sauƙin wannan jarabawa, tare da fatan Allah Ya kawo mafita.

Daga: Mansur Musa Salihawa

INA BUƘATAR TAIMAKO, FISABILILLAHI! 🙏Jiya na je aiki wani ƙauye a jihar Kano. A can na haɗu da wata uwa da ta kawo ɗanta...
11/09/2025

INA BUƘATAR TAIMAKO, FISABILILLAHI! 🙏

Jiya na je aiki wani ƙauye a jihar Kano. A can na haɗu da wata uwa da ta kawo ɗanta ƙarami (ba ya wuce watanni 6) domin rigakafi, amma lamarin ya girgiza ni ƙwarai.

Cikin ikon Allah, an haifi yaron da kaciyarsa (shayinsa). Amma akwai matsala: a ƙasan zakarinsa, tsakanin marainansa, akwai wani tsagi inda fitsarinsa ke fita ta ciki.

Na tambayi mahaifiyar, sai ta fashe da kuka. Ta ce mijinta ya ƙi ɗaukar mataki, duk da roƙon da ita da ‘yan uwanta s**a yi masa. Ta ƙara da cewa matarsa ta biyu ke hana shi kula da su.

Yaron da kansa ya bayyana rashin lafiya da ƙarancin abinci. Kuma wannan matsala idan ba a gaggauta ba, ka iya janyo mummunar cuta ta hanyar kamuwa da infection.

Na ba mahaifiyar shawarar ta cigaba da lallashin mijin, ko a barta ta kai yaron Asibitin Mallam Aminu Kano, domin samun kulawa. Amma zuciyata na ji ba lallai ta samu nasara ba.

Don haka nake roƙo: idan akwai ƙungiya ko mutane masu ƙwarewa da sha’awar taimakon irin wannan lamari, ku haɗa ni da su. Zan iya kai su ƙauyen domin a taimaka wa wannan uwa da jaririnta.

UPDATE:

An ba da shawarar mu tara kuɗi domin ganin mun kai wa wannan mata ɗauki. Don haka, don Allah, kowa mai sisin ƙwari ya taimaka ta wannan account:

Bank: Opay
Account Number: 7036231033
Account Name: MISBAHU L. HAMZA

Allah Ya saka da alheri, Ya sa mu dace da ladan taimakon marasa ƙarfi.

✍🏽 Misbahu El-Hamza

September, 2025

Fisabilillah: An raba Naman shanu da Wani Bawan Allah ya baiwa Marayu Alhamdulillah! An gudanar da rabon naman shanu gud...
11/09/2025

Fisabilillah: An raba Naman shanu da Wani Bawan Allah ya baiwa Marayu

Alhamdulillah! An gudanar da rabon naman shanu guda 4 tare da kudin mota ga iyayen marayu fiye da 200.

Wannan aiki na alheri ya zo ne domin rage musu radadin rayuwa da kuma nuna kulawa ga waɗanda s**a fi bukata.

Idan ba a manta ba, a satin da ya gabata ne wani bawan Allah ya bayar da manyan shanu guda 4 domin rabawa ga iyayen marayu 200 fisabilillah, ba tare da son a san sunansa ba.

Don Allah ku yi masa addu’ar samun nasara a rayuwa, Allah ya saka masa da alheri mai yawa.

📌 *Aikawa Charity Foundation* 📞 08082744019

2027: Wanne ne gwaninka a Kano? Zabi wanda kake ganin ya fi dacewa da tafiyar Kano: 🔹 A Barau Jibrin🔹 B Abba Kabir  Ku n...
11/09/2025

2027: Wanne ne gwaninka a Kano?

Zabi wanda kake ganin ya fi dacewa da tafiyar Kano:

🔹 A Barau Jibrin
🔹 B Abba Kabir

Ku nuna ra’ayinku domin a san wane ne yafi amincewar jama’a

Address

Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muhimmiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share