30/05/2026
BABBAN LABARI: Ma’aikata Sun Cancanci Albashin N100,000 — Shugaban NGF Ya Shaida Wa Tinubu
Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF), AbdulRahman AbdulRazaq, ya buƙaci Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya yi la’akari da ƙara mafi ƙarancin albashi daga N70,000 zuwa N100,000.
Da yake jawabi a wani taro da gwamnoni s**a yi da shugaban ƙasa a Legas, AbdulRazaq ya ce ƙarin kuɗaɗen shiga da jihohi ke samu bayan cire tallafin man fetur ya sa akwai damar inganta walwalar ma’aikata.
Ya kuma yabawa gwamnatin Tinubu kan cire tallafin mai, yana mai bayyana matakin a matsayin ɗaya daga cikin manyan sauye-sauyen tattalin arziki da s**a buƙaci jajircewa da ƙarfin hali.
Me ra’ayinku yake? Shin lokaci ya yi da za a ƙara mafi ƙarancin albashi zuwa N100,000?