Managarchi TV

Managarchi TV ALHAMDULLILAH WANNAN GROUP NE WANDA YAN UWA S**A HADU S**A BUDE DOMIN SAMUN KARATUTTUKAN MALAMAI HADEDA SANAR DA YAN'UWA ABINDA KE FARUWA NA ADDININ ISLAM.

CIKIN HOTUNA: Yadda Aka Gudanar da Sallar Jana'izar Babban Malamin Addinin Musulunci Sheikh Dokta Ahmad Umar Hashim, yau...
07/10/2025

CIKIN HOTUNA: Yadda Aka Gudanar da Sallar Jana'izar Babban Malamin Addinin Musulunci Sheikh Dokta Ahmad Umar Hashim, yau Talata 07/10/2025

07/10/2025
HANYAR SHEIKH YAHYA MASASS**A. A hakikanin gaskiya, ya wajaba  a gare mu musamman mabiya darikun Sufaye musamman darikar...
07/10/2025

HANYAR SHEIKH YAHYA MASASS**A.

A hakikanin gaskiya, ya wajaba a gare mu musamman mabiya darikun Sufaye musamman darikar Tijjaniyya, Mu farka a kan wannan lamarin mu dawo cikin hayyacinmu kada mu manta da manhajin da Shehu Tijjani ya doramu da shi da babban Halifansa Shehul Islam Alhaji Ibrahim Niass Allah ya kara musu yarda..

Akwai wani lamari mai tayar da hankali a zamanin nan: Shugaban wata da’awa mai taken Alƙur'ani zalla da ake kira Sheikh Yahya Masuss**a ya zama abin kwaikwayo da kafa hujja da shi ga wasu ba'ari na biyan buƙatar wasu daga cikinmu. Da yawa daga cikinmu mabiya ɗariƙa muna murna da shi saboda yana tsananta wa ‘yan Izala/Wahabiyya, muna ganin tamkar yana kare mutuncinmu. Wannan ra’ayin kuskure ne.

"Mai hankali ba ya rungumar kuskure saboda ya ga yana cutar da abokin adawarsa; domin kuskuren nan zai dawo ya cutar da shi da kansa."

~Hikimar Malaman Sufaye)

1. Matsalar Da’awar Masuss**a

Da’awar da Masus**a yake yadawa tana da hatsari sosai, ba iya ga ‘yan Izala kadai ba, har ma ga mabiya Sufaye. Tabbas Ya kauce daga tafarkin Annabi yana yaki da kalaman da suke sabawa ilimin Ahlus-Sunnah wal-Jama’ah.

Babban hatsarin da ke tattare da da’awarsa shi ne:Yana wulakanta ko ƙaryata wasu daga cikin hadisai da a ka tabbatar da ingancinsu. Ko kuma karyata hadisai dukka. Amman na ga wani gajaren bidiyo da yake cewa karyata hadisain sunfi ga nauin guda uku Hadisin da ya taɓa darajar Annabi da kuma hadisin da ya karyata ayar Alƙur'ani, da kuma hadisin da yake koya ta'addanci.

Idan karyata hadisin iya haka ya tsaya muma a kan wannan Layin muke domin ba ma bukatar duk hadisin da yake munana ladabi ga Annabi ko kuma yake cin karo da ayoyin Alƙur'ani da hadisin da karara yake koya ta'addanci duk da bana tunanin tun asalin ma akwai irin wadanna Hadisan..

Ina ganin tafiyar Masass**a tana k**a da irin fikirar irin wadanda suke kafa sabuwar da'awa suke da ita duk da tsohuwar da'awa ce amman tasa tafi daukar hankali fiye da sauran wadanda s**a gabace shi sai ya nake ganinta k**ar ta fito a matsayin sabuwar fikira ko sabuwar da'awa.

1. ASALIN SABON MANHAJI DA DALILANSA

Masu kirkirar da’awa galibi ba sa fitowa don neman gaskiya, sai dai saboda wasu kwakwara dalilai k**ar:

1. Sha’awar iko da mulki:
Suna neman rinjayar jama’a domin mallake zukata dan neman kuɗi da shugabanci.

2. Rashin ilimi da zurfin fahimtar addini:
Jahilci kan kai mutum ya ɗauka cewa yana gyara addini.

3. Hassada da kyashi:
Wasu s**an tashi domin rusa mutuncin malamai da jagororin da jama’a ke bi.

4. Zuga ta siyasa ko bukatar duniya:
Sau da yawa ana yin amfani da addini domin cika wasu manufofin siyasa.

Wannan yanayi ya kasance tun zamanin farko bayan Annabi, k**ar yadda aka gani wajen Musailamah al-Kadhdhab da wasu ƙungiyoyin irin nasa.

2. HANYOYIN DA SUKE BI WAJEN WAWANTAR DA JAMA’A

Akwai dabaru da s**a kusan zama gama-gari a duk lokacin da aka tashi kirkirar sabuwar da’awa:

Ruguza amincin malamai da tsarin da ake bi

i) Suna fara bayyana cewa malamai da shugabannin addini sun ɓace ko suna amfani da addini ne domin neman kudi.
Da wannan, jama’a suke fara ƙyamatar malamai su rabu da su.

ii) Kirkirar matsala ta ƙarya

Suna fakewa da cewa akwai wata babbar illa a cikin tafarkin da aka gada, wadda su za su gyara. Suna amfani da kalmomi irin su: “Ku dawo zuwa ga asali” ko “Addinin da kuke bi an gurbata shi”.

iii) Sake fasalta tarihi da nassosi

Suna rage darajar malamai da sahabbai ta hanyar zaben nassosi da suke taya kafa akidar domin su taya su zama hujja, ko ƙaryata sahihan hadisai da tafsirin malaman baya.

iv) Ƙarfafa kai da kiran juyin juya hali

Suna ɗaga kansu zuwa matsayin tsarkaka.
Suna cewa su ne masu ceton al’umma, s**an kira sauran musulmi da ƴan bidi’a ko jahilai.

v) Amfani da dabarun motsa zuciya (psychological manipulation)

Yin wa’azi mai motsa, matasa da kuma kawo zargi. Tsoratar da jama’a da cewa idan ba a bi su ba za a hallaka. Yin amfani da harshen da yake ƙone zuciya.

3. MATSAYIN SHEHU TIJJANI ABUL ABBAS A KAN DA'AWAR IRIN SU MASASS**A.

Shehu Tijjani ya yi tsayayyen gargadi game da kowane irin harshe da ya ke rage darajar Annabi Sallalahu alaihi wa Salam
Ya ce:

“Duk wanda ya rage girmar Annabi da magana ko da’awa, Allah zai toshe masa hanyoyin alheri kuma ya ruguza abin da yake nema.”
(Jawāhir al-Ma’ānī, Babi na farko)

Shehu Tijjani ya karanta dukkan wadannan littattafan na Hadisi a kansu ya ginu kuma a kansu ya kafa darikarmu ta Tijjaniyya.

4. Tasirin Irin Wannan da'awar ta su Musass**a a kan al'ummarmu

1. Ruguza amincewa da malamai da gadon tafarkinsu – jama’a su bar tushen shari’a.

2. Rarrabuwar kai da tashin hankali – mabiyan sabon manhaji su yi adawa da sauran musulmi.

3. Sauke darajar Annabi a zukatan mutane – su daina girmama sunnah da ibadu.

4. Rashin zaman lafiya da fitina a al’umma – tashin hankali da rikice-rikice.

Al’ummar Musulmi, musamman mabiya ɗariƙa, su tsare kansu daga bin kowane harshe da ya kauce daga wannan tafarki, su tsaya a kan girmama Annabi da jagorancin malamai na gaskiya.

Ku jira yi Massus**a idan ya yiwa Wahabiyya ritaya dole lallai kanmu zai fado.

Mujaheed M Muh'd
07/10/2025

YANZU YANZU: Babban Malamin Addinin Musulunci Sheikh Dokta Ahmad Umar Hashim, Allah Yayi Masa RasuwaCikakken Tarihin Dr....
07/10/2025

YANZU YANZU: Babban Malamin Addinin Musulunci Sheikh Dokta Ahmad Umar Hashim, Allah Yayi Masa Rasuwa

Cikakken Tarihin Dr. Ahmad Omar Hashim (1941 – 2025)

--- Asalin Rayuwa

An haifi Dr. Ahmad Omar Hashim a shekara ta 1941 a ƙauyen Bani Amer, garin Zagazig, a yankin Sharqiyyah, ƙasar Masar (Egypt).

Ya tashi cikin gida mai tsananin kishin addini, inda ya haddace Al-Qur’ān tun yana ƙarami.

--- Ilimi da Karatu

Ya karanci Shari’a da Hadisi a Jami’ar Al-Azhar, cibiyar da ta fi tsufa kuma mafi daraja a ilimin addinin Musulunci.

Ya sami digiri na farko (B.A.) a fannin Hadisi a 1967, digirin Masters a 1969, sannan digirin PhD a 1973.

Ya zama malami (Professor) a fannin Hadisi da Ulum al-Hadith a shekarar 1983.

--- Ayyuka da Muk**ai

Shugaban Jami’ar Al-Azhar daga 1995 zuwa 2003 — inda ya taimaka wajen buɗe sababbin cibiyoyi na nazarin Hadisi da Tafsiri.

Memba na Majalisar Manyan Malamai (Majma’ al-Kibar al-Ulama) ta Al-Azhar.

Memba a Majalisar Wakilai (Egyptian Parliament), inda ya kare darajar malamai da tsarin addini a cikin dokokin ƙasa.

Shugaban Majalisar Malamai ta Duniya don Ginin Zaman Lafiya da Taimakon Addinai.

Ya wakilci Al-Azhar a tarurruka da dama a duniya — Saudiyya, Pakistan, Indonesia, Morocco, Sudan, da sauran ƙasashe.

--- Littattafai Masu Tasiri da Rubuce-Rubuce

Dr. Ahmad Omar Hashim ya rubuta fiye da littattafai 40 da s**a shafi Hadisi, Akida, Da’awah, da Harshe. Ga wasu daga cikin shahararrun ayyukansa:

1. “Nūr min Sunnat al-Nabī ﷺ” – Hasken daga Sunnan Annabi.

2. “Al-Tarbiyyah al-Rūhiyyah fī al-Islām” – Tarbiyyar Ruhaniya a Musulunci.

3. “Al-Islām wa al-Da’wah al-Hadīthah” – Addinin Musulunci da Da’awah a zamani.

4. “Al-Sabr wa Fadhluh” – Juriya da falalarsa.

5. “Al-Hadīth Nabawiyy wa ‘Ulūmuh” – Nazarin Hadisi da ka’idojinsa.

6. “Al-Tasamuh fī al-Islām” – Haƙuri da fahimtar juna a Musulunci.

--- Gudummawarsa ga Al-Ummah

Ya yi wa’azi a gidajen talabijin da radiyo na Masar fiye da shekaru 40.

An san shi da murya mai nutsuwa da hikima wajen bayyana Hadisi da fassarar Sunnah.

Ya taka rawa wajen ƙarfafa haɗin kai tsakanin mazhabobi da yaki da tsatsauran ra’ayi.

A 2023, an ba shi lambar yabo ta “Islamic Personality of the Year” a Dubai International Holy Qur’an Award, saboda irin gudummawarsa ga addini da ilimi.

--- Rasuwa

Ya rasu a ranar 6 ga Oktoba, 2025 (2 Rabīʿ al-Thānī, 1447 AH).

An yi masa Sallar Jana’iza a Al-Azhar Mosque, inda dubban mutane s**a halarta daga sassa daban-daban na duniya.

Ana fatan Allah Ya ba shi Al-Jannah al-Firdaws, tare da Annabi Muhammad ﷺ da Salihin.

--- Maganarsa ta Ƙarshe da aka fi tunawa da ita:

> “Manzon Allah ﷺ ya bar mana hanyar gaskiya. Duk wanda ya bi ta da sadaukarwa, Allah zai haskaka rayuwarsa da ilimi da imani.”

©️ Abubakar Ayisalaty

MUSAN MALAMANMU PART 12: Tarihin Sheikh Modibbo Aliyu Jobbo, Babban Malamin Addinin Musulunci Ne Kuma Shehi a Ɗariqar Ti...
07/10/2025

MUSAN MALAMANMU PART 12: Tarihin Sheikh Modibbo Aliyu Jobbo, Babban Malamin Addinin Musulunci Ne Kuma Shehi a Ɗariqar Tijjaniyya

TAKAITACCEN TARIHIN MAULANMU SHEIKH MODIBBO ALIYU JOBBO GOMBE ALLAH YA ƘARA YARDA A GARE SHI.

Na samu wannan rubutun daga zuriyarsa mai albarka kuma su ne su kai izinin da a ƙara yaɗawa ƴan uwa domin mu ƙara amfana da ƙasaitaciyar rayuwar Maulana Sheikh Madibo Aliyu Jobbo.

Sunansa Modibbo Aliyu Jobbo ɗan Modibbo Abbdullahi (Shetiman Dukku) ɗan Modibbo Ardo Haruna jikan Modibbo Ardo Sambo Bodejo Sarkin Fulani na farko a kasar Dukku.

Sun zo ƙasar Dukku tun kafin jihadin Shehu Usman dan Fodiyo a shekarar ta 1804, k**ar yadda ya zo a tarihi sun zo ne daga yammaci kasar Sudan wato yankin Kurdufan yankin yana maƙotaka da ƙasar Tchadi, sun biyo ta yankin Kanem Borno sun tsaya a Ƙatar kalam Dukku a yanzu wasun su kuma s**a wuce garin Mama'are, wasu kuma garin Shira duk a jihadin garin Bauchi wasu kuma sun wuce yankin Jahun na jahar Jigawa.

An haifi Maulana Modibbo Jobbo a garin Dukku na jihar Gombe a yanzu a shekarar 1895 ko 1898 wanda tai daidai da 1315 ko da 1316 Hijiriyya....

Ya ta so cikin kullawar mahaifinsa Modibbo Abdullahi Allah ya ƙara yarda a gare shi, wanda ya kasance shi ma shahararren waliyin ne. Sunan mahaifiyarsa Sayyada Fadima. Ya fara karatun Alkur'ani mai girma a wajen mahaifansa ya fara karatun Ilimomin addinin musulunci duka a wajen mahaifinsa k**ar irin su Fikihu, Luga, da Nahawu.

Ya cigaba da zama a gaban yayan mahaifinsa a lokacin shi ne sarkin Dukku na ana kiran sa da suna Sarki Haruna Rashid, mai rubutun tarihin ya ci gaba da cewa Sarki ya tura mahaifin Maulana zuwa wani yanki don ya ci gaba da gudanar da karantarwar addinin musulunci k**ar yadda s**a gada iyaye da Kakani.

Maulana ya ci gaba da zama a garin Dukku, bai bi mahaifinsa ba sak**akon Sarki Haruna Rashidi ya ce yana son zama da Maulana saboda kiyaye faɗin wani baƙon Malami da ya zo wucewa ta ƙasar Dukku ya ke cewa "Wannan matashin zai taka matsayi mai girma awilaya.

Maulana Modibbo Aliyu Jobbo ya shiga garin Gombe, wajen shahararren malami Alkalin gari Wazirin gari Shehu Ahmad Tijjani Ibn Abubakar
wanda Shehu Ibrahim ya ke yabonsa a cikin Rihla Hijaziyya.

Maulana har sai da ya kai matsayin dukkan babu k**arsa Shehin yana cewa "Duk wanda ya yi karatu a wurina to ya maimaita a wajen Modibbo Jobbo" Sauda dama ya kan ce musu Ku dinga daukan karatu a wajensa.

Sannan ana cewa faɗin girman shaharar wannan makaranta ta Waziri Tijjani ta kai ba'a inda ake samun irin ta sai Irin ƙasar Kano, da ƙasar Zazzau a faɗin ƙasar Najeriya ta yanzu.

Makarantar ta fitar da shahararun waliyi irin su.

Modibbo Jailani Yola
Modibbo Umar Jarkasa
Modibbo Tukur Gombe
Modibbo Muhammadu Kagadama Jigawa Shehu Manzon Gombe
Modibbo Ali Gombejo

Da akwai da yawansu.

Mai rubutun tarihin Allah ya saka masa da mafificin alheri, ya cigaba da kawo tarihin ya rubuta cewa: Waɗanda su kayi karatu s**a zama manyan Malamai sunfi mutum ɗari Uku (300) daga wurare daban-daban a cikin ƙasar Najeriya, Jamhuriyar Nijar, Kamaru Jamhuriyar Tsakiyar Afirka (Central Afrika) da sauransu.

Bayan komawa Sheikh Waziri Tijjani Allah ya ƙara yarda a gare shi, zuwa rahmar Ubangiji a garin Makka, bayan komawarsa aikin Hajji. almajiran Shehi gaba ɗayan su sun dawo zawiyyar Maulana Modibbo Jobbo, ya zamanto malami kuma jagora ga dukkan almajiran Shehu Ibrahim Niasee, Allah ya ƙara yarda a gare shi, na kasar Gombe da kewaye kuma zawiyyarsa ta zamo cibiyar Faira bayan bayyanar Faira, domin dukkan abin da Shehu Ibrahim Niasee Allah ya ƙara yarda a gare shi, zai aiko daga Kaulaha zuwa ga mukaddamai da muridai na al'ummar ƙasar Gombe da kewaye shi ya ke aikowa ya sannan ya tara muƙaddamai ya faɗa musu.

Akwai alaƙa mai karfi tsakaninsa da Shehu Ibrahim Niasee Allah ya ƙara yarda a gare shi .

Modibbo Jobbo yana da Ijazozi daban daban daga Shehunai mabanbanta k**ar su Shehinsa Shehu Waziri Tijjani, Sheikh Ibn Umar Ainamali, Sheikh Adamu Badamagare Azare, Shekhul Hadis Sheikh Isma'il Ibn Ali daga Makkatul Mukarram, Shehul Hadi Murtaniya, da kuma shakundum wato Shehul Islam Alhaji Ibrahim Niasee Allah ya ƙara yarda a gare shi.

Maulana Modibbo Jobbo yana da tarin almajirai da dama k**ar yadda ya gabata a baya kusan dukkan almajiran Sheikh Waziri Tijjani almajiransa ne.

Akwai daga fitattun almajiransa akwai:

Maulana Shehu Dahiru Usman Bauchi

Maulana Shehu Manzo Gombe.

Maulana Modibbo Tukur Gombe

Maulana Shehu Ibrahim Bogo

Maulana Modibbo Muhammad Ali Garuza

Shugaban alƙalai Yahya Ahmad (Grand Khadi)

Maulana Halifa Sheikh Bashir Modibbo Jobbo
Sheikh Habibu Modibbo Jobbo

Maulana Sheikh Modibbo jelani Yola

Maulana Modibbo Jobbo yana da ƴaƴa masu albarka k**ar haka:

Halifa Sheikh Bashir Modibbo Jobbo, Sheikh Habibu, Sheikh Mustafa , Sheikh Ahmad Tijjani akwai Sayyada Balkisu, Sayyada Asma'u, Sayyada Rukayya da Sayyada Rabi'atu

Ya koma zuwa rahmar Ubangiji a shekarar 1973 wanda ya ci gaba jagorancin almajirai da ƴaya shi ne Halifa Sheikh Bashir Modibbo.

Zawiyyar tana kan Titin Jankai Dawaki yamma da a birnin Gombe.

Na samu rubutun daga zuriyar Maulana na ƙara wasu batutuwan kadan a rubutun saboda na shigar da shi cikin jerin waɗanda nake kilacewa.

Godiya ta musamman ga Adamu Habibu Jobbo Allah ya saka masa da mafificin alheri.

✍️ Mujaheed M Muh'd

©️ Abubakar Ayisalaty

07/10/2025

Karatun zaure Tareda malam abubakar Adam alfullaty rigasa kaduna

YANZU YANZU: Matashin Malamin Addinin Musulunci Sheikh Suleiman Sheikh Gambo Sufi , Kenan a Cikin Birnin Madina da yamma...
06/10/2025

YANZU YANZU: Matashin Malamin Addinin Musulunci Sheikh Suleiman Sheikh Gambo Sufi , Kenan a Cikin Birnin Madina da yammacin yau Litinin 06/10/2025

06/10/2025

Mal Ibrahim Mai Ashifa

06/10/2025

Shirin MUSAN MALAMANMU PART 12 gobe 7:00am Insha Allah
Tarihin Sheikh Modibbo Aliyu Jobbo Gombe

YANZU YANZU: Sectary Gwamnatin Jihar Yobe, Baba Mallam Wali Mni, Ya bayar da Gudunmar Tirela Daya ta Cementi, ga Khalifa...
06/10/2025

YANZU YANZU: Sectary Gwamnatin Jihar Yobe, Baba Mallam Wali Mni, Ya bayar da Gudunmar Tirela Daya ta Cementi, ga Khalifa Sheikh Muhammadu Fatihu Sheikh Gibirima Nguru, Yau Litinin 06/10/2025

A yammacin Wannan Rana ne ta Litinin Hon. Baba Mallam Wali Mni ya turo da Tirela Daya ta Cementi a Matsayin Gudunmarsa ga Halarar Sheikh Muhammadu Gibirima,

Wanna Kyauta Tazo ne Hannun Hatsinkin Matashin Nan, Babagana Muh'd Shettima Bms

Muna Rokon Allah Yasaka Masa da Alkhairi Allah Yabiya masa dukkanin Bukatunsa Alfarmar Manzon Allah sallallahu Alaihi Wasallam 🤲

©️ Abubakar Ayisalaty

KAJI RABO: Ni Babban Abunda Yake Sakani Farin Ciki, Naga Ana Karanta Alqur'ani Mai Girma.Sayyada Ummuhani Sheikh Ibrahim...
06/10/2025

KAJI RABO: Ni Babban Abunda Yake Sakani Farin Ciki, Naga Ana Karanta Alqur'ani Mai Girma.

Sayyada Ummuhani Sheikh Ibrahim Inyass

Address

Kaduna
MANAGARCHICOMMUNICATIONS

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Managarchi TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share