Mai Aiki TV

Mai Aiki TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Mai Aiki TV, .

Wannan Kamfani Ne Da Aka Kafa Shi Don Sada Masu Ciniki Da Masu Kasuwanci, Gami Da
Labaran Nishaɗi, Wasanni, Da Kuma Sanin Muhimman Mutane Da Muhimman Batutuwa Da Suka Shafi Ƙasar Hausa Da Hausawa✓

KANO TA DABO CI GARI.SARKIN KANO WARISI DAN BAGAUDA (1063-1095) SARKIN KANO NA BIYU.Bayan mutuwar Bagauda sai dansa Wari...
19/07/2025

KANO TA DABO CI GARI.
SARKIN KANO WARISI DAN BAGAUDA (1063-1095) SARKIN KANO NA BIYU.

Bayan mutuwar Bagauda sai dansa Warisi ya dauki ragamar mulki. A wannan lokaci ne aka ba Warisi shawarar ya matsa lamba a kan Gazarzawa in dai har yana son ya mallaki kasa duka. An ce akwai wani babban gunki a Gazarzawa wanda mutanen wurin ke bautawa. Idan an ruguje gunkin, za a mallaki mutanen wurin da nasarori masu yawa wurin kafa Kano. Duk da haka Warisi bai wani yunkuri ba saboda manyanci na shekaru. Warisi ya mutu a nan Sheme bayan ya yi shekaru talatin da uku (33) a kan mulki.

SARKIN KANO GAJIMASU DAN WARISI (1095-1134) SARKIN NA UKU.

Ko da Gajimasu ya zama Sarki sai ya bar Sheme ya tafi Gazarzawa ya gina gida a wurin inda ya zauna da iyalansa. A wannan lokaci ne ya yaudari mazauna wurin da kyaututtuka wurin kokarinsa na sanin sirrin da s**a boye game da Tsumburbura. Da ya fara fahimtar abubuwa da ke lullube sai ya shammaci jama'a ya fara gina ganuwar Kano daga kofar Mazugal zuwa kofar Ruwa, sunnan ya dauko gini daga kofar Adama zuwa kofar Gadon kaya. Daga nan sai ya kara daukan gini daga kofar kansa Kali zuwa kofar Tuji inda ya zarce har zuwa kawankari da kofar Tuji.

A wannan lokaci ne aka fara gina harsashin Birnin Kano. A wannan lokaci ne kuma Gajimas ya fara kokarin fadada kasar Kano inda ya mallaki Gano da Dabai da Ringim da Kuma Danbakon Yaki. An ce ya sami nasaran mallakar al'ummomi da ke Dala da wadansu da ke gewaye da ita. A wannan lokaci ne alamun kafuwar Birnin ya kanama inda baki s**a fara shiga Kano. Ya yi shekaru arba'in (40) a kan mulki ya mutu

SARAKUNAN KANO NAWATA DA GAWATA (1134-1136) SARAKUNAN KANO NA HUDU.

Nawata da Gawata tagwayen 'ya'ya NE ga Sarkin Kano Gajimasu wadanda s**a yi Sarautar a lokacin guda. Babu wani bayani a rubuce yanda aka yi mutane biyu s**a yi Sarauta a lokaci guda amma tarihi ya tabbatar da hawa mulkinsa a lokaci daya. An tabbatar da cewa kowane guda daga cikinsu yana rike mashi idan zai fito Fada. Wadannan masu guda biyu su ne aka game su wuri guda a Zamanin mulkin Sarkin Kano Abdullahi Bayero (1926-1953), aka sami Tagwayen Masu. An ce daya daga cikin Tagwayen ya mutu bayan sun hau Sarauta da watanni goma Sha daya. Daga bisani kuma sai dayan ya mutu bayan ya yi shekara biyu akan karagar mulki.

17/07/2025

TASKAR WASANNI

Muhimmancin kakar ɗan wasan Barcelona Lamine Yamal yasa ya ƙi zuwa sanya hannu kan sabon kwantragi bayan ya cika shekara 18, saida ta dawo daga tafiya

KANO TA DABO CI GARI.SARAKUNAN HABE.SARKIN KANO BAGAUDA (999-1073).Masani tarihi sun bayyana cewa Bagauda wanda asalin s...
17/07/2025

KANO TA DABO CI GARI.
SARAKUNAN HABE.

SARKIN KANO BAGAUDA (999-1073).

Masani tarihi sun bayyana cewa Bagauda wanda asalin sunan shi shine Dauda ya yi shirin yaki a lokacin da ya bar Daura zuwa Kano. A wannan lokacin, babu garin Kano sai dai tsoffin mazaunai a Dala da Gwauron Dutse da Fanisau da Magwan da wadansu mazaunai kusa da nesa da inda Kano take a yanzu. A kan hanyarsu ta zuwa sai ya yada zango a Gaya wanda ba ta da nisa da inda Kano ta ke a yanzu. A nan a Gaya sai Bagauda ya kafa mazauni inda ya zauna tare da dakarunsa. Mutanen Gaya na ambaton wirin da Bagauda ya zauna da sunan Gidan Bagauda. Daga nan ne Bagauda ya wuce wurin Karbar al'amuran mulki daga hannun Abagayawa da suke Dala.

Ga dukkan alamu, Bagauda ya sami turjiya daga mutanen Dala wadanda s**a zurfafa wurin bautar Tsumburbura. A wannan lokaci akwai ragowar fadawan Barbushe k**ar su Jankare da dai sauransu wadanda s**a nuna rashin amincewarsu. An ce Bagauda ya kashe Jankare. Ko da Bagauda ya iso Dala, ya iske tsoffin mazaunai na kusa da nesa a yankin wadanda s**a hada da Gazarzawa wanda take tsakanin Jakara zuwa Santolo da Fangon wanda take tsakanin Santolo zuwa Burkun da Zaura wanda take tsakanin Bomfai zuwa Wase da Dunduruzu wanda take tsakanin Watari zuwa Dutsen Karya (Karaye) da Shari'a wanda take tsakanin Santolo zuwa Kazaure da Gande take tsakanin Burkum zuwa Kera da kuma Tokarawa wanda take tsakanin Karmami zuwa Ringim.

Ganin turjiyar da Bagauda ke fuskantan daga wadannan al'ummomi sai ya tafi Dirani ya gina gida inda ya zauna shekara biyu (2). Daga nan sai ya koma Burka ya gina wani alkarya wanda aka rika ambatonsa da sunan Talautawa inda ya shekara biyu (2). Daga nan ne sai Bagauda ya tafi Sheme inda ya iske mashahuran matsafa a wurin. Duk da haka Bagauda ya mallake su inda ya gina farfajiyar mulkinsa a nan Sheme. Bagauda ya sami shekaru sittin da shida (66) a matsayin Sarkin Kano amma bai mallaki mutanen da s**a tattaru s**a haifar da Kano ba har ya mutu. Ga dukkan alamu, Bagauda ya dauki lokaci mai tsawo yana yake-yake da ahalin Barbushe wadanda s**a ki amincewa da shi a matsayin shugabansu.

DA ƊUMI-ƊUMITsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya bayyana ficewar sa daga jam'iyyar PDP
16/07/2025

DA ƊUMI-ƊUMI

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya bayyana ficewar sa daga jam'iyyar PDP

KANO TA DABO CI GARI.BAYYANAR MULKIN HABE.Mulki mihimminan al'amari ne wanda yake tsirowa cikin al'umma sannu a hankali....
16/07/2025

KANO TA DABO CI GARI.

BAYYANAR MULKIN HABE.

Mulki mihimminan al'amari ne wanda yake tsirowa cikin al'umma sannu a hankali. A wanchan lokaci, kafin bayyanar mulkin Habe, Mai karfi shine ya kan zama shugaba ko jagoran mutanen da ke yankin. Ana cikin haka sai aka fara samun masu fifiko na karfi da wurin bautan iskokai suna zama shugannin jama'a. A Kano, alamun mulki ya fara bayyana ne a lokacin da jama'a s**a fara tattaruwar a Dala domin neman Tama da kuma gudanar da baututtukansu na iskokai. A wannan lokaci ne Barbushe ya bayyana a matsayin shugaba inda ya ke da mataimaka a sauran mazaunan da ke gewaye da Dala k**ar yanda muka ambata a sama. Baya ga karfin da Barbushe ya ke da shi a wurin bautar iskokai, an ce mutum ne baki, dogo, kakkarfa wanda yakan kashe giwa da hanunsa sannan ya duniya ta a kansa ya yi tafiyar mil tara (9) ba tare da ya gaji ba.

Wannan ya tabbatar da cewa alamun mulki ya fara bayyana a Kano tun kafin bayyanar Sarkin Habe na farko wato Bagauda (999-1063). Bayan mutuwar Barbushe, an sami lokacin mai tsawo a Dala babu kwakkwaran shugaba mai karfi da zai hana masu karfi aikata zalunci. A wannan lokaci ne k**a karya da danniya s**a addabi jama'a. Ganin haka sai jama'a s**a Kai kukansu Daura domin a taimaka musu da shugaba wanda zai daidaita al'amuransu ta fuskan shugabanci. A dalilin haka aka turo Bagauda dan Bawo dan Bayajidda Kano domin ya mulki jama'a k**ar yadda za mu gani cikin wannan Babi.

Tarihi ya tabbatar da an sami Sarakunan Habe a Kano guda arbain da uku (43) a Kano. Sarkin Kano na farko shi ne Bagauda dan Bawo dan Bayajidda wanda ya fara sarauta daga shekarar 999-1063, Sarautar Habe ta zo karshe a zamanin Sarkin Kano Muhammadu AlkaliII wanda ya fara sarauta daga shekarar 1781-1805 sak**akon jihadin Shehu Usumanu Dan Fodiyo. A nazarin da muka yi mun fahimci an sami gaba uku a Sarautar Habe na Kano. A gaba ta farko, Sarautar Kano ta fara daga Bagauda inda ta kare a zamanin mulkin Yakubu Dan Abdullahi Burja 1452-1463. Ana ambaton Sarakunan da s**a fara mulkin tun daga Bagauda har zuwa Abdullahi Burja da sunan Bagaudawa. A gaba ta biyu, Sarautar da Kano ta ci gaba ne daga mulkin Sarkin Kano Muhammadu Rumfa 1463-1499, zuwa Sarkin Kano Muhammadu Nazaki 1618-1623. An rika ambaton Sarakunan da s**a yi mulki daga Muhammadu Rumfa zuwa Muhammadu Nazaki da sunan Rumfawa. Gaba na uku wanda ita ce ta karshe ta fara ne daga kan Sarkin Kano Muhammadu Alwali I 1623-1648, wanda aka fi sani da Kutumbi zuwa Sarkin Kano Muhammadu Alwali II 1781-1805. Ana ambaton wadannan Sarakuna tun daga Kutumbi har zuwa Alwali II da sunan Kutumbawa. Babi na gaba zaiyi maganane akan sarakunan Habe.

KANO TA DABO CI GARI.KAFA BIRNIN KANO.Birnin Kano daddden gari ne wanda ya bayyana sannu a hankali har ya habbaka ya zam...
14/07/2025

KANO TA DABO CI GARI.

KAFA BIRNIN KANO.

Birnin Kano daddden gari ne wanda ya bayyana sannu a hankali har ya habbaka ya zama babbar alkarya k**ar yadda muke ganin da a yanzu. Bincike da nazarin da muka gudanar ya tabbatar mana da cewa Kano ta tattara al'umomi daban -daban daga sassan duniya wadanda a jimlace aka rika ambatonsu da sunan Kanawa. Akwai bayanai mabanbanta a kan yadda jama'a s**a fara tattaruwar a mazaunin Dutsen Dala wanda hakan ya zama harsashin kafa Birnin Kano. Akwai wadanda s**a ce ayarin wadansu mafarauta s**a fara zama a Dutsen Dala da Dutsen Magwan da Kuma tsibirin da ke Fanisau tun a shekarar 635 miladiyya. Wadannan mafarauta sun rika gudanar da sana'oinsu a wurin tabkin Jakara wanda aka fi Ambato wurin da sunan bakin ruwa inda s**a rika farautar manyan namun daji.

Akwai Kuma wadanda s**a ambata cewa wani mutumin Gaya mai suna Kanno ya zo da ayarinsa yankin da ta zamo kano domin neman Tama a karni na shida (6) zuwa karni na bakwai (7). Wadannan mutane makera ne Kuma mafarauta. Sun ci gaba da neman Tama har zuwa Dutsen Dala inda s**a samu s**a koma Gaya. Daga bisani sai mutane daga wasu wurare s**a rika ziyartar wadannan makera a Dala wanda hakan ya yi sanadiyar kafa wadansu mazaunai kusa da Dala. Akasarin wadannan baki sun yin kaure ne daga gaba shin Sudan da Gabas ta Tsakiya sak**akon yake-yake da ya addabe su. Daga cikin wadannan al'umomi aka rika kera mak**an da ake yin farauta da su. Daga wannan zama ne aka rika samun wadansu masu basira a wasu sana'oi k**ar noma saka, da rini da kuma jima.

Masana tarihi da ke garin Gaya sun bayyana cewa Kanno dan Wabadin dan-uwa ne ga Gayya. Sun tabbatar da cewa shi ne ya assasa zaman jama'a yankin da ya zama garin Kano. Sun ce tun asali, Kanno ya fara gano Dutsen Dala da albarkatun Tama da ke jibge a kan dutsen. An ce Kanno ya mulki jama'a da ke yankin Dala tare da Barbushe har zuwa lokacin mai tsawo.

Ko ma dai mene ne tarihin kafuwar Kano, akasarin masana tarihi sun yi matsaya a kan cewa mutanen Gaya wadanda ake ambatonsu da sunan Abagayawa sun taka mihimmin rawa wurin kafa kano. Kamar yadda muka ambata a sama, babu wani kokwanto Gaya ta samarwa Kano da suna. Duwatsun da ke gewaye da Dala k**ar su Gwauron Dutse da Panisau da Tanagar da Magwan da Santolo sun rika janye hankulan jama'a suna zama wuraren wadanda daga bisani s**a tattaru aka gina zama a wuraren wadanda daga bisani s**a tattaru aka gina kano tare da su. An ce akwai jinsin baki na biyu wadanda s**a shigo yankin da ta zama Kano daga bisani inda s**a kafa Madatai. Ana hasashen wadannan baki sun fito ne daga kasar Ya man (Yemen). Bincike ya nuna cewar tun kafin bayyanar Kano, mutane sun zauna a dake wurare daban -daban da s**a hada da jama'an da ke Arewacin Kogin Chalawa da kuma tsofaffin mazaunai wadanda s**a hada da Gaya da Rano da karaye da Sheme. Akasarin wadannan mutane sune s**a tattaru s**a samar da Birnin Kano.

Masana tarihi sun tabbatar da cewa Sarkin Kano na farko a jerin Sarakunan Habe wato Bagauda (999-1063) bai zauna a Kano ba. Bagauda ya ci gaba da zarya tare da dakarunsa, ya sauka nan, ya tashi can. Ya kasa gina Birnin Kano domin mayar da ita farfajiyar mulkinsa. Wannan al'ada ta zarya ta ci gaba a zamanin Sarkin Kano na biyu wato Sarkin Kano Warisi (1063-1095). An ce daga cikin wadanda s**a mulki Kano a jerin Sarakunan Habe Sarkin Kano na uku, Gajimasu dan Wasiri (1095-1134), shine ya fara gina gani war Birnin Kano ta farko wanda dansa, Sarkin Kano Naguji dan Wasiri (1194-1247), ya kammala. Wannan sune bayanan yanda aka gina Birnin Kano wanda ta zama farfajiyar masarautar Kano, inda ta ci gaba da bunkasa sannu a hankali har ta kawo yanzu.

Rubutunmu na gaba zaiyi magana ne akan bayanan mulki Habe suwanene Habe?

KANO TA DABO CI GARI.BAIYANAR ADDININ MUSULUNCI A KANO.Tarihi ya nuna cewa addinin Musulunci ya fara shiga Kano ta hanya...
13/07/2025

KANO TA DABO CI GARI.

BAIYANAR ADDININ MUSULUNCI A KANO.

Tarihi ya nuna cewa addinin Musulunci ya fara shiga Kano ta hanyar baki fatake tun a zamanin Sarkin Kano na Habe, Usman Zamna Gawa (1343-1349), wato tun kafin zuwan Wangarawa. Ga dukkan alamu, Kanawa ba su yi na'am da shi ba. Musulumci ya fara karbuwa ne a Zamanin mulkin Sarkin Kano Ali Yaji (1349-1385), a lokacin da Malaman Wangarawa s**a shiga Kano karkashin jagorancin Abdurrahman Zaite. A wannan lokaci ne s**a sanya Yaji ya kiyaye Salloli da sauran ibadu. Daga nan ne, Yaji ya umurci jama'a arsa su rungumi addinin Musulunci. KO da Yaji ya rasu, wanda ya gaje shi kai tsaye wato Sarkin Kano Bugayya (1385-1390), ya yi kokarin rike addinin Musulunci inda ya umurci a sallace shi idan ya mutu, sannan a bizne shi a makabartar Madatai k**ar yadda addinin Musulunci ya tanada. Duk da haka, wadansu daga cikin Sarakunan Kano da s**a biyo bayan Bugayya sun bijire ma addinin Musulunci inda s**a koma tafarkin bautar Tsumburbura da tsafe-tsafensu.

An ci gaba da tafiya haka har lokacin da Muhammadu Rumfa (1463-1499), ya zama Sarkin Kano. A wannan lokaci ne Shaihu Abu Muhammad Al-Maghili ya ziyarci Kano da jama'sa. Al Maghili ya umurci Muhammadu Rumfa ya gina Masallacin Juma'a da Kuma aiwatar da shari'a wanda ya amince da duk abin da ya shawarce shi. A Zamanin Sarkin Kano Muhammadu Kisoke (1509-1565), an kara samun ziyarar wadansu Malamai daga Tunisiya wanda s**a hada da Shehu Atunashe da Shehu Abdussalam. Akwai ma wadansu Malamai da s**a shiga kano a wannan tsakani wadanda s**a hada da Shehu Kursiki da Kabi da Tama da Buduru da Dan-Gwauron Duma da Shehu Magumi wadanda sun taimaka wurin yada addinin Musulunci. Duk da yumkurin da Malamai s**a rika yi, akasarin wadanda ke ikirarin sun karbi addinin Musulunci sun ci gaba da surka shi da baututtukan iskokai har zuwa lokacin da aka kaddamar da jihadin Shehu Usumanu Dan Fodiyo a shekarar 1804 k**ar yadda za mu gani nan gaba.

Babinmu na gaba zaiyi maganane akan kafa kanon ita kanta.

"JANYE TALLAFIN MAI DA TINUBU YAYI NE YA JEFA NAJERIYA CIKIN YUNWA"ATIKU ABUBAKAR
13/07/2025

"JANYE TALLAFIN MAI DA TINUBU YAYI NE YA JEFA NAJERIYA CIKIN YUNWA"

ATIKU ABUBAKAR

GA DALILIN DA YASA AKA K**A 'GOSSIMA'A ranar juma'a ne ƴansanda s**a tare Gossima a garin Kafin Hausa dake Bulangun Jiha...
13/07/2025

GA DALILIN DA YASA AKA K**A 'GOSSIMA'

A ranar juma'a ne ƴansanda s**a tare Gossima a garin Kafin Hausa dake Bulangun Jihar Jigawa. Sannan kuma s**a garzaya da shi Abuja. Ƴansanda sun ƙi bayyana dalilin k**a shi, amma wani abokin sa mai suna Mustapha ya ce an k**a shi ne a dalilin comment da yayi a social media Kan wani mai neman shiga majalisar wakilai ta ƙasa.

"We are not so politically backwards that we will warrant voting for that irresponsible boy as our member in the House of Representatives"

"Siyasar mu bata yi lalacewar da zamu zaɓi wani shashan yaro ya wakilce mu a majalisar wakilai ba"

A Yau, Wole Soyinka ya cika shekara 91
13/07/2025

A Yau, Wole Soyinka ya cika shekara 91

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mai Aiki TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mai Aiki TV:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share