04/06/2026
KADA KI ZAMA UWA KAWAI...
Ki kula da tsabtar tunanin ɗanki daga munanan kalmomi da maganganu marasa kyau, kamar yadda k**e kula da tsabtar tufafinsa a kowace rana.
Ki ciyar da hankalinsa da ingantacciyar aƙida kamar yadda k**e ciyar da jikinsa da abinci.
Ki kula ya riƙa yin sallolinsa a kan lokaci, kamar yadda k**e kula da jadawalin cin abincinsa.
Ki kula da zuwa Masallaci da kuma haddar Alƙur’ani, kamar yadda k**e kula da zuwa Makarantarsa.
Maimakon ki riƙa ba shi labaran ƙarya da tatsuniyoyi kowane dare, ki riƙa ba shi labaran Annabawa, Sahabbai, Tabi’ai, da salihai, domin ya ƙaunace su kuma ya yi koyi da su.
Ki koya masa ma’anar “La ilaha illallah” kafin ki koya masa haruffan baƙaƙe.
Ki riƙa gaya masa labarin Aljannah kafin ki riƙa gaya masa labarin duniya.
Ki sa ya so Lahira tun yana ƙarami, kafin ya girma ya fara jin tsoronta.
Ki koya masa girmama manya, da ladubban cin abinci, da kuma sada zumunci.
Ki koya masa kyawawan halaye da ɗabi’u.
Ki zama uwa mai girma, ki yi niyyar tarbiyyarsu domin Allah, domin Allah Ya sanya albarka a cikinsu.
Ki tashe su cikin ingantacciyar tarbiyya, har idan sun shiga shagulgulan rayuwa, su riƙa ɗaukar masallaci a matsayin hanya, abokai na gari a matsayin mafaka, Alƙur’ani a matsayin aboki, Aljannah kuma a matsayin buri.
Ki zama uwa abin koyi a tarbiyya.
Ki zama abokiya, masoyiya, kuma kusa da su, ba uwa kawai ba.
Al’umma tana buƙatar mazaje masu ƙarfi, waɗanda ba sa jin tsoron zargin kowa a cikin abin da ya shafi Allah, kuma duniya ba ta shagaltar da su daga Lahira.
Saboda haka, ki zama ke ce wadda za ta gina su.
Allah Yasa mu amfana.