24/11/2025
TSARO: Ban san 'yan bindiga ba kuma ban taɓa ganin su ba karya Nasir El-Rufai Yake min da yace na biya biliyan ɗaya 1bn ga 'yan bindiga -Gwamna Uba Sani
Gwamnatin Jihar Kaduna karkashin jagorancin Gwamna Uba Sani ta ce batu da tsohon gwamna Nasir El-Rufa’i ya yi kwanakin baya na kan wai an biya Biliyan ɗaya 1bn ga ’yan bindiga, ba gaskiya ba ne ko kaɗan. Wannan na cikin hirarsa da Channels TV – wacce gwamnati ta kira magana marar tushe da nufin tayar da hankali.
A sanarwar da Kwamishinan Tsaro, Dr. Sule Shu’aibu, ya fitar:
Ya ce gwamnatin Gwamna Uba Sani ba ta taɓa biyan kuɗi ga ’yan bindiga ba, kuma ba za ta taɓa yi ba.
Ya ce Gwamna Uba Sani ba ya saduwa ko tattaunawa da ’yan bindiga, b***e ya basu ko sisi.
Ya kara da cewa ONSA, ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan tsaro, ma ya taba karyata irin wannan zargi, ya kira shi jita-jita maras tushe.
Gwamnatin Kaduna ta dauki sabuwar dabarar tsaro: aiki da al’umma, karfafawa wajen ilimi da lafiya, da yaki da talauci amma ba biyan kuɗi ga masu laifi ba.
Haka zalika, kungiyoyin tsaro na ƙasa musamman Birnin-Gwari Vanguard, wadanda s**a sha wahala a zamanin El-Rufa’i, sun fito fili s**a ce maganarsa ba ta da gaskiya.
Sanarwar ta kuma tuna cewa ma wasu daga cikin jami’an da s**a yi aiki a gwamnatinsa sun taba zarginsa da yin sulhu da wasu gungun masu laifi, abin da ya sa sabon korafin nasa ya zama abin mamaki.
Gwamnati ta ce tun zuwan Gwamna Uba Sani:
Makarantu sun koma aiki,
Kasuwanni An bude,
Manoma sun koma gona,
Kuma hadin kai tsakanin jami’an tsaro da jama’a ya karu.
A ƙarshe, gwamnatin ta umurci El-Rufa’i da ya janye maganarsa ya nemi afuwar jama’a cikin mako guda, in ba haka ba za a dauki matakin doka.