
25/09/2025
Kungiyar Malaman Ahlussunna na jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Dr. Abdallah Gadon Kaya ta miƙa ƙorafi ga Sakataren Gwamnatin Kano (SSG) kan zargin da wasu ke yi wa Malam Lawan Triumph, cewa ya yi magana mai kausasa ga Annabi Muhammad (SAW).
A cikin rahoton da s**a gabatar, malaman sun ce:
Sun damu matuƙa da irin wannan zargi da ake yaɗawa, domin ya shafi addini da mutuncin Musulunci.
Sun roƙi gwamnatin Kano ta ɗauki matakan da s**a dace wajen bincike da tabbatar da gaskiya, tare da bin doka da oda.
Sun jaddada muhimmancin kiyaye martabar Annabi (SAW) tare da yin kira ga jama’a da su guji ɗaukar doka a hannunsu.
Dr. Gadon Kaya ya yi nuni da cewa, Ahlussunna ba za su taɓa lamuntar duk wani abu da zai iya zubar da mutuncin Manzon Allah (SAW) ba, amma a lokaci guda ya yi kira ga hukumomi da su tabbatar da adalci wajen gudanar da bincike.
ATP Hausa