29/05/2023
Ganduje Yayi Mursisi Yaki Zuwa Taron Rantsar da Sabon Gwamna, Bayan Barin Bashin N241.5b
Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje ya mika mulki ga zaɓaɓɓen gwamna, Abba Kabir Yusuf tare da barin bashin N241.5 biliyan.
Sakataren gidan gwamnatin jihar, Alhaji Usman Alhaji ne ya wakilci gwamnan mai barin madafun iko, wanda ya ki halartar bikin rantsuwa, inda ya mika mulki ga gwamna mai jiran gado da safiyar Litinin a gidan gwamnatin Kano.
Ya bada takaitaccen rahoton abubuwan da aka kashe da ya kunsa ayyukan gwamnatin jihar daga 2015 zuwa 2023, inda ya zayyana yadda aka bar bashin N241.5 biliyan ga jihar.
Kamar yadda Ganduje ya ce " Abubuwan da aka yi amfani dasu daga watan Yunin 2015 zuwa Mayun 2023 ya nuna yadda aka kashe jimillar N660.3 biliyan da jimillar N540.6b a matsayin kudin da ake juyawa, sannan an tara N1.2tiriliyan.
"Saura sun hada da Wutar Lantarkin Kano da Ruwa, wanda ke da N740m, haka zalika Wutar Lantarkin Kano da Ruwa na da N703m, kuma ana saran samun N4b Talata mai zuwa.
"Sannan akwai Hukumar Lafiya na Jihar Kano da ke da N4.3biliyan, kazalika, Kamfanin Noma na Jihar (KASCO) na da N837.7m.
"A halin yanzu, bashin da ake bin Kano na Kungiyar Amintattun Jihar ya kai N75.6b, da kuma N9.2b na jihar, tare da N66.3b na karamar hukuma, wanda hakan ya bada jimillar N75.6b.
Har ila yau, akwai kudin haraji, na Kamfanin Fansho na N4.5b. Daga nan ne jimillar bashin ciki da waje ya k**a N123.3b.
"Saboda haka, jimillar bashin da ake bin jihar daga 31 ga watan Disamba 2022, wanda ya k**a N241.5 b."
Yayin jawabi jim kadan bayan rattaba hannu kan rahoton, sabon gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana alhininsa kan yadda gwamna Ganduje ya ciwo tarin bashi ga mutanen jihar.
"Ina ake so mu nema wa jihar kudi?
" Ɗan kudin da jihar ta bari ba wani na azo a gani bane.
"Ina bada hakuri, amma dole tasa zan bayyana hakan don mutanen kwaran jihar su fahimci inda muka dosa.
"Don me ake fakewa da masu tuntuba, masu tuntuba da yawa don kawai a kwashe arzikin jihar.
"Zamu bi diddigi kan lamarin. Ban yaba ba.
"Sai dai, muna godiya ga tsohon gwamnan kan yadda ya hidimtamawa mutanen kwaran jihar k**ar yadda yake tsammani " cewarsa.