AREWA GIDA MEDIA

AREWA GIDA MEDIA Newspapers

DA DUMI DUMI : Daren Jiya layin Sadarwa na MTN ya Sauke Wa dukkan Wanda ake Bi Bashi A cikin layin Shi Shin an Sauke muk...
11/11/2023

DA DUMI DUMI : Daren Jiya layin Sadarwa na MTN ya Sauke Wa dukkan Wanda ake Bi Bashi A cikin layin Shi

Shin an Sauke muku naku Bashin ?

FARILLAN ALWALA GUDA BAKWAI NE DON ALLAH KARKA WUCE BAKA TSAYA KA KARANTA BA.           FARILLAN ALWALA GUDA 7 NEH:1. Ni...
05/11/2023

FARILLAN ALWALA GUDA BAKWAI NE DON ALLAH KARKA WUCE BAKA TSAYA KA KARANTA BA.

FARILLAN ALWALA GUDA 7 NEH:
1. Niyya
2. Wanke Fuska
3. Wanke hannaye zuwa gwiwar hannu
4. Shafar kai
5. Wanke kafafuwa
6. Cuccudawa
7. Gaggautawa

SUNNONIN ALWALA

• Wanke hannaye zuwa wuyan hannu
• Kurkure baki
• Shaka ruwa
• Fyacewa
• Juyo da shafar kai
• Shafar kunnuwa
• Sabunta ruwa agaresu
• Jeranta tsakanin farillah

MUSTAHABBAN ALWALA

• Yin bismillah
• Goga asuwaki
• Kari akan wankewa ta farko a fuska da hannaye
• Farawa daga goshi
• Jeranta sunnoni
• Qaranta ruwa a nisa gabobi
• Gabatar da dama kafin hau.

AKAN FASALIN ALWALA

• Wanda ya manta da wata farilla daga gabobinsa, idan ya tuno sai ya aikata ta da abunda ke bayanta, idan kuma yayi nisa sai ya aikata ta ita kadai, ya kuma sake abunda ya sallata bayan faruwar abun.

• Idan kuma ya bar sunna, to saiya aikata ta ita kadai bazai sake sallah ba.

• Wanda kuma ya mance lam'a sai ya wanke ta ita kadai da niyya, in kuma har yayi sallah by an faruwar hakan toh sai ya sake ta

• Wanda ya tuna da kurkurar baki ko shaqa ruwa bayan ya rigaya ya fara wanke fuska, to bazai dawo gare su ba har sai ya gama alwalarsa, sannan sai yayi su

• Tsettsefe 'yan yatsu hannuwa yana wajaba, an so a tsettsefe 'yan yatsun qafafuwa, tsefe gemu mara dubu yana wajaba acikin alwala, tsefe gemu yana wajaba acikin wanka koh da mai duhu neh.

AKAN FASALIN ALWALA (2)

• Babu yana halatta ga wanda bashi da alwala yayi sallah, koh dawafi, koh ya taba al qur'ani koda acikin gafakarsa neh, bada hannunsa ba saidai idan *juzu'i* neh ga mai neman ilimi acikinsa.

• Yaro a wajen taba al qur'ani k**ar babba yake, amma laifin yana wuyan wanda ya bashi al qur'anin ya taba.

• Wanda yayi sallah da gangan ba tare da alwala ba toh shi kafiri neh. Allah yakiya she mu.

RA’AYI: Duk Wanda Ka Ga Yana Adawa Da Abinda 'Yan Hizbah Suke Yi A Kano A Bincike Shi, Kila Yana Daga Cikin Mazan Da Suk...
04/11/2023

RA’AYI: Duk Wanda Ka Ga Yana Adawa Da Abinda 'Yan Hizbah Suke Yi A Kano A Bincike Shi, Kila Yana Daga Cikin Mazan Da Suke Neman Matan Da Ake Kamawa, Cewar Wannan Matashiyar

Me zakù cè ?

MARTANI: Duk lalacewar da ƴaƴa mata suke yi wallahi laifin maza ne. ƴan iská kawai, Cewar ƴar gwagwarmaya Zainab Nasir A...
04/11/2023

MARTANI: Duk lalacewar da ƴaƴa mata suke yi wallahi laifin maza ne. ƴan iská kawai, Cewar ƴar gwagwarmaya Zainab Nasir Ahmad

Me zakù cè ?

GYARA KO BARNA ??Hotuna Yanda Yan Hisba S**a Faffasa Wasu Dakuna A Sarina Hotel Dake Kano AREWA GIDA MEDIA
31/10/2023

GYARA KO BARNA ??
Hotuna Yanda Yan Hisba S**a Faffasa Wasu Dakuna A Sarina Hotel Dake Kano
AREWA GIDA MEDIA

MUHIMMIN SAƘO ZUWA GA MUTANEN AREWA.🚨Wannan Saƙon yana da matukar muhimmanci ina baku shawara kuyi ajiye shi a cikin way...
30/10/2023

MUHIMMIN SAƘO ZUWA GA MUTANEN AREWA.🚨

Wannan Saƙon yana da matukar muhimmanci ina baku shawara kuyi ajiye shi a cikin wayoyin ku na sadarwa, sannan kuyi sharing domin saƙon yakai ga sauran al'umma, baku san adadin rayukan mutanen da zaku ceta ba. Kuma bai kai darajar Naira 10 ba don kunyi sharing.

Wannan lambobin sadarwar sashin iko ne, na ƴan Sandan Nijeriya nayi ƙoƙari na samo domin taimakawa wajen yaƙi da matsalolin tsaro da muke fama da ita.

Ina kira ga ƴan uwa masu kishin al'ummar Arewa dama Nijeriya baki ɗaya kuzo mu haɗa kai domin tsaftace Arewa daga matsalolin da take ciki.

Allah ya bamu zaman lafiya mai ɗorewa ya jiƙan waɗan da s**a rasa rayukansu.

Amin summa Amin
AAREWA GIDA MEDIAGAREWA GIDA MEDIAMAREWA GIDA MEDIA

WATA SABUWA: Jarumar Kannywood Maryam Ahmed, wacce aka fi sani da Maryam KK ta bayyana yanda aka kawar mata da dudurcint...
25/10/2023

WATA SABUWA: Jarumar Kannywood Maryam Ahmed, wacce aka fi sani da Maryam KK ta bayyana yanda aka kawar mata da dudurcinta da lemon Fanta, a cikin wata hira da akayi da ita a Freedom Radio.

Minene ra'ayinku?

AREWA GIDA MEDIA

Da dumi'dumi: Gwamna Uba sani Yabi sahun Gwamna Abba Gida-Gida na kano zai tura dalibai karatu Jami'ar Mewar dake kasar ...
21/10/2023

Da dumi'dumi: Gwamna Uba sani Yabi sahun Gwamna Abba Gida-Gida na kano zai tura dalibai karatu Jami'ar Mewar dake kasar India.

Gwamnatin Uba Sani a jihar Kaduna ta dauki nauyin karatun dalibai 50 ‘yan asalin jihar domin karatun kwasakwasan kimiyyar ICT kyauta a Jami’ar Mewar.

Mewar jami’an ce da kasar India ta bude a Afrika ta Yamma kuma Jami’ar ta zama daya daga cikin manyan jami’o’in dake horas da dalibai kwasakwasan ICT da komfuta a Afrika.

A zaman da ta yi da daliban da Iyayen su a dakin taron ‘Sir Kashim Ibrahim House’ mataimakiyar gwamnan jihar Kaduna Hadiza Balarabe ta yi kira ga daliban da su mai da hankali a karatunsu sannan ta yi addu’a Allah ya kai su lafiya a duk lokacin da s**a shirya tafiya jami’ar a jihar Nasarawa.

Jami’ar Mewar ta bada damar daukan dalibai 100 daga jihar Kaduna tare da Bada ƙarfi wajen ganin an fi daukan mata daga cikin yawan da za tura karatu.

An zabo dalibai daga kananan hukumomi 23 kuma wadanda s**a yi kokari a jarabawar JAMB inda daga ciki 50 ne aka dauka.

Daga cikin dalibai 50 akwai mata 33 da maza 16.

‘Yan fansho da tsofaffin sojojin da su ka dade da yin ritaya za su samu kudin da za a rabaDomin ganin babu wuru-wuru a t...
21/10/2023

‘Yan fansho da tsofaffin sojojin da su ka dade da yin ritaya za su samu kudin da za a raba

Domin ganin babu wuru-wuru a tsarin, sai akwai BVN & NIN sannan za a biya mutum kudi

Daga mako mai zuwa kudi za su rika shiga asusun mutane kai tsaye daga babban bankin CBN

Inna Lillahi...Tsananin bulala har sai da s**a kashe...Yau Juma'a 20 October, 2023 na samu labarin wani mummunar hukunci...
20/10/2023

Inna Lillahi...
Tsananin bulala har sai da s**a kashe...

Yau Juma'a 20 October, 2023 na samu labarin wani mummunar hukunci da hukumar makarantar Al-Azhar Academy dake bayan Kofar Gayan Zariya s**a yi wa wani dalibinsu mai suna Marwanu Nuhu Sambo, dan JS3 (Basic 9), wanda a yayin wannan hukuncin sai da s**a aika shi har lahira, saboda tsananin hukunci.

Bayan kisan wannan yaro da s**a yi, ba su sanar da iyayensa ba har sai da iyayen yaron s**a rika jin rade-radin cewa an kai yaron asibitin Al-Ridha Clinic, inda s**a garzaya can domin tabbatar da labarin da suke samu game da dan nasu, amma bayan sun samu likitan, sai ya fada masu cewa, shi ba mara lafiya aka kawo masa ba; gawa ce aka kawo masa.

Na tafi da kafafuwana har wannan makaranta domin tabbatar da wannan labarin, a inda na zanta da wasu dalibai 2 da kuma wani yaro mai sayar da abinci a makarantar, tare da wata mata aure duka s**a tabbatar man da faruwar wannan al'amari.

Daga nan, na garzaya zuwa gidan da dalibin da aka kashe yake, na tattauna da wasu iyayensa guda biyu, duka s**a tabbatar man da faruwar abin, har s**a kai ni inda ake yi wa gawar yaron wanka.

Bayan nan, na sake zuwa wurin wasu daliban makarantar, inda na zanta da su, daya daga cikin yaran ajinsu daya da dalibin da aka kashe. Sannan ya labarta man yadda malaman s**a aikata wannan hukunci. Yaron ya ce, mataimakin shugaban makarantar (vice principal) shi ya zo da yaron gaban assembly, inda s**a rika yi masa bulala babu kakkautawa tare da shugaban makarantar (Principal), tun suna iya kirga bulalar har s**a bata lissafi, inda yaron ya tabbatar man da kansa ya kirga bulala akalla 105 wanda aka yi wa yaron a gaban assembly, daga nan kuma s**a wuce da shi office, s**a cire masa riga, s**a bar shi da gajeren wando kawai s**a ci gaba da dukan sa har yaron ya yi yunkurin gudu, amma aka sa zabaniyawa (prefects) na makarantar s**a rike shi s**a koma da shi, s**a ci gaba da dukan sa har sai da s**a cire masa hakora, s**a kashe shi. Inji JAMILU S. BIZARA.

Iyaye na kaɗai ke ganin mutuncina a kaduna amma tunda na dawo kaduna matasan su maza da mata wulaƙanta ni suke yi sai ya...
20/10/2023

Iyaye na kaɗai ke ganin mutuncina a kaduna amma tunda na dawo kaduna matasan su maza da mata wulaƙanta ni suke yi sai yasa na zaɓi na ƙare rayuna na a Kano - A Zango

20/10/2023

BARKA DA SAFIYAR JUMA'A
DAGA INA KUKE BIBIYAR SHAFIN MU??

Ƙasar faransa na shirin soke lambar yabo na zinare data baiwa ‘Karim Benzama’ tare da soke lasisin data bashi na zama ci...
20/10/2023

Ƙasar faransa na shirin soke lambar yabo na zinare data baiwa ‘Karim Benzama’ tare da soke lasisin data bashi na zama cikakken ɗan ƙasar ta saboda ya goyi bayan al'ummar yankin falastinu.

SÒ GAMÒN JINI: Ko Da A Ce Zan Kai Har Tsawon Karshen Rayuwata Ban Yi Aure Ba, Zan Iya Jira Har Lokacin Da Adam A. Zango ...
20/10/2023

SÒ GAMÒN JINI: Ko Da A Ce Zan Kai Har Tsawon Karshen Rayuwata Ban Yi Aure Ba, Zan Iya Jira Har Lokacin Da Adam A. Zango Zai Aure Ni, Saboda Kaunar Da Nake Yi Masa, Cewar Wannan Budurwa

Wanne fata zakù yi mata ?

KAYI BACCI A BIYAKAA Amurka an bude wani shagon bacci, inda zaka so kayi bacci a kan gado a biyaka, wanda tuni wasu muta...
05/10/2023

KAYI BACCI A BIYAKA

A Amurka an bude wani shagon bacci, inda zaka so kayi bacci a kan gado a biyaka, wanda tuni wasu mutane sun fara tururuwa zuwa shagon baccin.

AREWA GIDA MEDIA

ZAƁI GWANÍNKA: Daga Lokacin Da Aka Rantsar Dasu Zuwa Yanzu Shin Wanné Gwamna Né Yafí Ƙoƙarí Da Kawó Wa Jìhar Sa Cigaba, ...
02/10/2023

ZAƁI GWANÍNKA: Daga Lokacin Da Aka Rantsar Dasu Zuwa Yanzu Shin Wanné Gwamna Né Yafí Ƙoƙarí Da Kawó Wa Jìhar Sa Cigaba, A Cìkìn Gwamnonin Nàjeriya Gaba Daya ?

ALLURÁ CIKIŃ RUWÁ: Sayyada Murja Ibrahim Kunya Ta Sáki Wasú Zafafań Hotuna Da S**a Tada Ƙúra A Kafafeń Sadarwa Na Zamaní...
01/10/2023

ALLURÁ CIKIŃ RUWÁ: Sayyada Murja Ibrahim Kunya Ta Sáki Wasú Zafafań Hotuna Da S**a Tada Ƙúra A Kafafeń Sadarwa Na Zamaní.

Wanne fata zakú yi mata?

Shugabar Karamar Hukuma A Jihar Yobe Ta Jagoranci Rusa Gidaje 39 Na Karuwai, Giya Da Ƴan Gala Shugabar karamar hukumar F...
01/10/2023

Shugabar Karamar Hukuma A Jihar Yobe Ta Jagoranci Rusa Gidaje 39 Na Karuwai, Giya Da Ƴan Gala

Shugabar karamar hukumar Fika a jihar Yobe, Hajiya Halima Kyari Joda ta jagoranci rushe gidajen karuwai, gidajen giya da gidajen ƴan gala har 39 a garin Ngalda dake karamar hukumar Fika.

Kwanakin baya, Hajiya Joda tare da hadin gwiwar sarakunan gargajiya ta jagoranci jami'an tsaro da hukumar Hizba wajen k**a masu sana'ar giya, masu gidajen Gala da Gidajen karuwai a garin Ngalda.

Bayan an gurfanar dasu a gaban hukuma, yau kuma cikin ikon Allah ta jagoranci rushe musu gidaje 39 masu dauke da adadin ɗakuna 140.

Hakan ya biyo bayan illar da gidajen suke yiwa Al'umma musamman wajen lalata tarbiya, safarar miyagun kwayoyi da sauran munanan ɗabi'u da suke haddasawa a cikin al'umma.kucigaba da bibiyar jaridar AREWA GIDA MEDIA domin samun ingantattun labarai nagida dana waje.

Address

Kaduna

Telephone

+2348140710678

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AREWA GIDA MEDIA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AREWA GIDA MEDIA:

Share