JKD Media

JKD Media Home of JKD Media. Official page of JKD TV DSTV channel 391 and Hamada 91.3FM Kaduna !

Malam Lawan Triumph ya musanta zargin batanci ga Annabi (SAW) a gaban Majalisar Shura ta KanoShahararren malamin addinin...
13/10/2025

Malam Lawan Triumph ya musanta zargin batanci ga Annabi (SAW) a gaban Majalisar Shura ta Kano

Shahararren malamin addinin Musulunci a Kano, Sheikh Lawan Shuaibu Abubakar, wanda aka fi sani da Lawan Triumph, ya musanta zargin yin batanci ga Annabi Muhammad (SAW) kan wasu kalaman da ya yi a cikin wa’azinsa da s**a jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta.

Shehin malamin ya bayyana hakan ne a lokacin da ya gurfana a gaban Majalisar Shura ta Jihar Kano inda ya ce an fassara kalamansa ba daidai ba tare da daukar su daga wasu faifan bidiyo da aka yanke, abin da ya janyo rudani a tsakanin jama’a.

Triumph ya ce: “Na yi imani da Annabi da koyarwarsa, kuma shi ne jagora na mai cetonmu. Duk wanda ya yi kuskure wajen fahimtar kalamaina ya nemi cikakken bidiyon sannan ya yafe mani, domin ba da gangan na yi hakan ba.”

Rahotanni sun nuna cewa, zargin da aka yi masa sun shafi wasu maganganu da aka alakanta da siffar Annabi (SAW), haihuwarsa da kuma iyayensa, lamarin da ya tayar da hankali a tsakanin malamai da kungiyoyin addini a jihar.

Shugaban Majalisar Shura na jihar Kano, Malam Sa’ad Gidado, ya gargadi malamin da ya rika kula da kalamansa musamman a wuraren jama’a, tare da jan hankalinsa da cewa yana da alhakin tabbatar da hadin kai da zaman lafiya a cikin al’umma.

Ya ce: “Ka guji kalaman da za su iya kawo rabuwar kai a tsakanin al’ummar Musulmi. Ka tsaya a kan koyarwar Annabi Muhammad (SAW) domin tabbatar da gaskiya da zaman lafiya.”

Wasu daga cikin malaman da s**a halarci zaman sun shawarci Sheikh Lawan Triumph da ya kasance mai taka tsantsan a cikin wa’azozinsa, tare da duba illar da kalamansa ka iya haifarwa ga jama’a.

Majalisar Shura ta Kano ta ce nan gaba za ta fitar da shawarwari domin tabbatar da zaman lafiya da daidaituwar fahimta a jihar.

1 Tarar Miliyan 9.52 Kwashe  musu Maki 3 da kwallo uku3 Rufe Filin Wasa na Sani Abacha 4 Mayar dasu Katsina Wasa Babu Ya...
13/10/2025

1 Tarar Miliyan 9.5
2 Kwashe musu Maki 3 da kwallo uku
3 Rufe Filin Wasa na Sani Abacha
4 Mayar dasu Katsina Wasa Babu Yan Kallo kar Karshen kaka ko zuwa Wasa 10

Yaya kuka kalli wannan Hukunci?

JKDTv

13/10/2025

Labaran Duniya 13/10/2025

13/10/2025

Shugaban Kungiyar, Dr Murtala Kwara ya bayyana hakan a yayin hirar sa da manema labarai a Katsina.

13/10/2025

Mu leka gari

CONUA: Ba Mu A Cikin Yajin Aikin ASUUKungiyar malaman jami’a ta CONUA (Congress of University Academics) ta bayyana cewa...
13/10/2025

CONUA: Ba Mu A Cikin Yajin Aikin ASUU

Kungiyar malaman jami’a ta CONUA (Congress of University Academics) ta bayyana cewa ba ta shiga yajin aikin da kungiyar ASUU ke yi a halin yanzu.

Shugaban kungiyar, Dr. Niyi Sunmonu, ya fitar da sanarwa inda ya karyata rahotannin da ke cewa CONUA ta shiga yajin aikin.

Ya ce kungiyar tana da burin ganin zaman lafiya da cigaban harkokin jami’a ta hanyar tattaunawa da fahimtar juna tsakaninsu da gwamnati da sauran bangarori.

“Muhimmi ne mu fayyace cewa, a wannan lokaci, CONUA ba ta da wani dalili da zai sa ta ayyana takaddama da gwamnatu ko ta shiga yajin aiki,” in ji shi.

Sunmonu ya umarci mambobin kungiyar da su ci gaba da gudanar da ayyukan koyarwa da gudanarwa yadda ya kamata.

Kungiyar ta bayyana cewa ta gabatar da korafin rashin saka ta a cikin kwamitin tattaunawa kan yarjejeniyar 2009 tsakanin malaman jami’a da gwamnatin tarayya. An kafa kwamitin ne a Oktoban 2024 ba tare da sunan CONUA ba.

Sanarwar ta ce hakan ya kai ga ganawa da ministan ilimi a ranar 11 ga Satumba 2025, kuma daga baya ma’aikatar ta faɗaɗa kwamitin don haɗa CONUA, kamar yadda aka yi alkawari.

Bayan taron na Satumba, CONUA ta gudanar da tarukan jihohi daga 18 zuwa 24 ga Satumba 2025, inda mambobi s**a jaddada matsayinsu na kin shiga yajin aiki, suna masu cewa tattaunawa ce mafita, ba katse karatu ba.

Sunmonu ya roƙi shugabannin jami’o’i su kare mambobin CONUA yayin da suke ci gaba da aiki, tare da kwantar wa dalibai hankali cewa karatu zai ci gaba ba tare da tangarda ba.

CONUA, wacce aka kafa a 2018 bayan rabuwar kai da ASUU, ta dade tana adawa da amfani da yajin aiki a matsayin hanyar gwagwarmaya.

ASUU ta ayyana yajin aikin gargadi na makonni biyu daga ranar 13 ga Oktoba, tana zargin gwamnati da kin cika alkawurra.

Gwamnatin tarayya ta mayar da martani da barazanar aiwatar da ka’idar “ba aiki, ba albashi”, tana jaddada cewa tattaunawa ita ce hanya mafi dacewa.

Ma’aikatar ilimi tana zargin ASUU da rashin sassauci a tattaunawar baya-bayan nan.

Ni, Ahmed Musa, Manajan Janar na Kano Pillars Football Club, ina miƙa gundarin haƙuri da neman afuwa mai zurfi ga duk wa...
13/10/2025

Ni, Ahmed Musa, Manajan Janar na Kano Pillars Football Club, ina miƙa gundarin haƙuri da neman afuwa mai zurfi ga duk wanda abin ya shafa kan abin takaici, abin zafi, kuma abin kunya da ya faru yayin wasanmu da Shooting Stars Sports Club a daren Lahadi.

Abin da ya faru a wannan wasa abin bakin ciki ne, abin kunya ne, kuma abin da ba za a taɓa yarda da shi ba. Wannan ba shi ne ainihin halayenmu, kimar mu, ko tarihin girmar Kano Pillars ba. Wannan kulob ya taɓa zama abin alfahari da mutunci, haɗin kai, da girmamawa — waɗannan dabi’un dole ne su ci gaba da zama ginshiƙai na kulob ɗinmu, ba a maye gurbinsu da tashin hankali ko rashin ladabi ba.

A matsayina na Manajan Janar, ina miƙa haƙuri mara iyaka ga ‘yan wasa, masu horo, jami’ai, da magoya bayan Shooting Stars Sports Club; ga alkalai da jami’an wasa waɗanda abin ya rutsa da su; ga Hukumar Nigeria Premier Football League (NPFL) da abokan huldarta na GTI; ga masu shirya gasar; da kuma duk masoya wasan ƙwallon ƙafa a Najeriya da wajen ƙasar da s**a kalli abin da ya faru cikin ɓacin rai da takaici.

Na san yadda abin ya zame muku zafi ganin abin da ya bata hoton wannan kyakkyawan wasa. Don haka, ina miƙa gaskataccen haƙurina daga zuciyata.

Tashin hankali ba shi da wurin zama a cikin wasan ƙwallon ƙafa. Abin da bai dace ba ne, ba a yarda da shi ba, kuma yana sabawa manufar wannan wasa mai ɗauke da farin ciki. Ƙwallon ƙafa wasa ne na haɗin kai, ƙauna, da nishaɗi. Idan ta zama abin tashin hankali, dole mu fuskance ta da gaskiya, ba mu rufe ido ba.

Ina tabbatar wa kowa cewa Kano Pillars FC za ta yi aiki tare da hukumomin da s**a dace domin gano waɗanda s**a haddasa wannan abin kunya, kuma za su fuskanci sakamakon abin da s**a aikata bisa ƙa’ida.

Mun fahimci cewa neman afuwa kaɗai bai isa ba. Bayan magana, dole ne mu bi ta da aiki. Don haka, kulob ɗin zai ɗauki matakai na ciki masu tsauri domin tabbatar da cewa irin wannan lamari ba zai sake faruwa ba a nan gaba.

Ga magoya bayanmu masu ƙauna, zan so in yi magana da ku kai tsaye: Kano Pillars kulob ne mai tarihi da ɗaukaka, kuma ku ne zuciyar kulob ɗin. Amma ku sani, gaskatacciyar goyon baya ba ta cikin tashin hankali, tana cikin mutunci, ladabi, da natsuwa. Wannan lokaci ne da ya kamata mu gyara. Mu nuna wa duniya cewa ƙaunar da muke yi wa kulob ɗinmu na iya zama ƙarfi da ɗaukaka ba tare da ta zama lalacewa ba.

A karo na ƙarshe, a madadin Kano Pillars Football Club, ina sake miƙa godiya da neman afuwa mai zurfi ga duk wanda abin ya shafa — ga NPFL, ga Shooting Stars, ga alkalai, ga magoya bayan ƙwallon ƙafa a Najeriya, da ga duk wanda yake gaskata da ruhin wasa.

Ahmed Musa, MON, OON
Manajan Janar, Kano Pillars FC

An samu hargitsi a filin wasa na Sani Abacha da ke Kano, inda magoya bayan kungiyar Kano Pillars s**a mamaye fili suna b...
12/10/2025

An samu hargitsi a filin wasa na Sani Abacha da ke Kano, inda magoya bayan kungiyar Kano Pillars s**a mamaye fili suna bin alkalin wasa da ‘yan wasa bayan kungiyar Shooting Stars ta zura kwallo a minti na 94 inda wasan ya tashi 1-1.

Masana harkokin wasanni na ganin cewa ana bukatar a ci gaba da wayar da kan magoya baya kan illar tashin hankali da mamaye fili yayin wasanni.

Rashin Tsaro: Mazauna Sokoto sun bukaci a basu damar kare kansu yayin da harin 'yan ta'adda ya ta'azzaraHafsat Ukissa Us...
12/10/2025

Rashin Tsaro: Mazauna Sokoto sun bukaci a basu damar kare kansu yayin da harin 'yan ta'adda ya ta'azzara

Hafsat Ukissa Usman

Al’ummar Karamar Hukumar Kebbe ta Jihar Sokoto sun bukaci gwamantin tarayya ta basu ikon mallakar makamai domin kare kansu daga hare-haren ‘yan bindiga da s**a addabe su.

Jama’ar yankin sun ce sun gaji da yadda ‘yan bindigar ke ci gaba da kai masu hari, da kashe masu mutane da kuma garkuwa da wasu, lamarin da ya sanya au cikin tsoro.

Sun ce daga cikin garuruwa 17 da Karamar Hukumar Kebbe ke da su, a yanzu ‘yan bindiga sun kori mutane daga garuruwa akalla 11, saboda yawaitar hare-hare.

Tukur Muhammad Fakum, daya daga cikin jagororin al’ummar ya shaida wa manema labarai cewa an riga an kai makura, don haka a yanzu fatan su kawai bai wuce neman wa kai mafita ba.

Ya ce ”Mu yanzu muna nan muna gangami, mai ‘yar karamar gona ya sayar, mai dan karamin gida ya sayar, in muka sayi bindigogi a ba matasa su ma su yi kokari su kare mu.

”Gwamnati ta ba mu kariya, idan kuma ba ta iyawa to ta bamu makamai a ba matasa, su matasa na iya kare rayukansu da garuruwan su,” in ji Tukur Muhammad Fakum.

Dangane da halin da irin barnar da ‘yan bindigar s**a yi masu kuwa, Tukur Muhammad Fakum ya ce ”Babu dai abinci, wanda bai taba kwana masallaci ba ya yi, ka tashi ka tafi garin da ba ka taba kwana ba, ka kwana dole. Bala’in ya baci.”

Ya kuma ce lamarin ya rusa kusan duk wata harkar tattalin arziki a yankin.

Jihar Sokoto na daga cikin jihohin da matsalar ‘yan bindiga ta addaba sosai a shekarun nan, inda suke aikata barna, musamman a kananan hukumomin Isa da Sabon Birni da kuma Kebbe.

Address

Gidan Daji
Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when JKD Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to JKD Media:

Share