18/08/2025
Fursunoni 62 sun tsere daga hannun ’yan bindiga bayan harin jirgin sama na sojojin sama a Danmusa LGA, Jihar Katsina
Gwamnatin Jihar Katsina ta tabbatar da nasarar tserewar fursunoni 62 da aka yi garkuwa da su, sakamakon harin da dakarun Sojin Sama na Najeriya s**a kai kan sansanin wani sanannen ɗan fashi, Muhammadu Fulani, da ke ƙauyen Jigawa Sawai, Karamar Hukumar Danmusa – wuri da ke iyaka da Jihar Zamfara.
Daga cikin waɗanda s**a tsere, mutum 12 na samun kulawa a Asibitin Gwamnati na Matazu, yayin da 16 ke tsugunne a sansanin sojojin ƙasa (FOB) na Kaiga Malamai.
Harin sojin sama wanda aka kai a ranar Asabar ƙarfe 5:10 na yamma, ya tilasta wa ’yan fashin barin maboyarsu, abin da ya bai wa fursunonin dama su tsere cikin taro.
A cewar waɗanda aka ceto, harin jirgin sama ya sa ’yan bindigar s**a watse, lamarin da ya ba su damar guduwa daban-daban. Yawancin waɗannan fursunoni an sace su ne daga ƙauyen Sayaya a ranar Litinin, 11 ga watan Agusta, 2025, lokacin da tawagar Fulani ta kai farmaki a daren ranar. Wannan tawaga dai ta shafe lokaci tana addabar yankunan Matazu, Kankia, Dutsinma har ma da wasu sassan Jihar Kano.