13/10/2025
Malam Lawan Triumph ya musanta zargin batanci ga Annabi (SAW) a gaban Majalisar Shura ta Kano
Shahararren malamin addinin Musulunci a Kano, Sheikh Lawan Shuaibu Abubakar, wanda aka fi sani da Lawan Triumph, ya musanta zargin yin batanci ga Annabi Muhammad (SAW) kan wasu kalaman da ya yi a cikin wa’azinsa da s**a jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta.
Shehin malamin ya bayyana hakan ne a lokacin da ya gurfana a gaban Majalisar Shura ta Jihar Kano inda ya ce an fassara kalamansa ba daidai ba tare da daukar su daga wasu faifan bidiyo da aka yanke, abin da ya janyo rudani a tsakanin jama’a.
Triumph ya ce: “Na yi imani da Annabi da koyarwarsa, kuma shi ne jagora na mai cetonmu. Duk wanda ya yi kuskure wajen fahimtar kalamaina ya nemi cikakken bidiyon sannan ya yafe mani, domin ba da gangan na yi hakan ba.”
Rahotanni sun nuna cewa, zargin da aka yi masa sun shafi wasu maganganu da aka alakanta da siffar Annabi (SAW), haihuwarsa da kuma iyayensa, lamarin da ya tayar da hankali a tsakanin malamai da kungiyoyin addini a jihar.
Shugaban Majalisar Shura na jihar Kano, Malam Sa’ad Gidado, ya gargadi malamin da ya rika kula da kalamansa musamman a wuraren jama’a, tare da jan hankalinsa da cewa yana da alhakin tabbatar da hadin kai da zaman lafiya a cikin al’umma.
Ya ce: “Ka guji kalaman da za su iya kawo rabuwar kai a tsakanin al’ummar Musulmi. Ka tsaya a kan koyarwar Annabi Muhammad (SAW) domin tabbatar da gaskiya da zaman lafiya.”
Wasu daga cikin malaman da s**a halarci zaman sun shawarci Sheikh Lawan Triumph da ya kasance mai taka tsantsan a cikin wa’azozinsa, tare da duba illar da kalamansa ka iya haifarwa ga jama’a.
Majalisar Shura ta Kano ta ce nan gaba za ta fitar da shawarwari domin tabbatar da zaman lafiya da daidaituwar fahimta a jihar.