JKD Media

JKD Media Home of JKD Media. Official page of JKD TV DSTV channel 391 and Hamada 91.3FM Kaduna !

Rundunar Sojin Amurka da ke kula da Afirka (AFRICOM) ta tabbatar da cewa ta kai farmaki ne bisa roƙon hukumomin Najeriya...
26/12/2025

Rundunar Sojin Amurka da ke kula da Afirka (AFRICOM) ta tabbatar da cewa ta kai farmaki ne bisa roƙon hukumomin Najeriya a Jihar Sokoto, inda aka kashe ’yan ta’addar ISIS da dama.
Rundunar ta ce hare-haren sun nuna ƙarfinta da kuma jajircewarta wajen kawar da barazanar ’yan ta’adda da ke barazana ga ’yan Amurka a cikin ƙasar da kuma a ƙetare.

“Amurka ta kaddamar da hare-hare masu ƙarfi kan ’yan ta’adda a Arewacin Najeriya,” in ji Trump.
25/12/2025

“Amurka ta kaddamar da hare-hare masu ƙarfi kan ’yan ta’adda a Arewacin Najeriya,” in ji Trump.

Ba a maye gurbin Gbajabiamila da Muri-Okunola ba — Fadar Shugaban ƘasaFadar Shugaban Ƙasa ta musanta wani labari na ƙary...
25/12/2025

Ba a maye gurbin Gbajabiamila da Muri-Okunola ba — Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta wani labari na ƙarya da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sauya Shugaban Ma’aikatan Fadarsa (Chief of Staff), Hon. Femi Gbajabiamila, da Babban Sakataren Sirrinsa (Principal Private Secretary), Hakeem Muri-Okunola.

A cikin wata sanarwa da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar a ranar Alhamis, ta bayyana cewa babu wata gaskiya ko kaɗan a cikin wannan ikirari, tare da kira ga ’yan Najeriya da su yi watsi da labarin gaba ɗaya.

Sanarwar ta jaddada cewa Hon. Femi Gbajabiamila na nan daram a matsayin Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, yayin da Hakeem Muri-Okunola shi ma ke ci gaba da gudanar da aikinsa a matsayin Babban Sakataren Sirri. Ta ce babu wani sauyi da aka yi a wadannan muk**ai.

Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa labarin da ke yawo ƙirƙirarre ne daga wasu masu yaɗa labaran ƙarya da nufinsu shi ne tayar da zaune tsaye da rashin jituwa a cikin gwamnati.

Haka kuma, ta sake jan hankalin kafafen yaɗa labarai da masu amfani da kafafen sada zumunta da su rika tantance sahihancin duk wani bayani kafin wallafawa ko yadawa.

Sanarwar ta samu sa hannun Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, a ranar 25 ga Disamba, 2025.

An ja hankalin shugabannin addinai,suyi amfani da mumbarinsu wajen yada wa’azin zaman lafiyaZahra MusaJagoran Chochin Ka...
25/12/2025

An ja hankalin shugabannin addinai,suyi amfani da mumbarinsu wajen yada wa’azin zaman lafiya

Zahra Musa
Jagoran Chochin Katolika ta Jihar Katsina, Most Reverend Gerald Mamman Musa, ya yi kira ga malaman addinai a Najeriya da su guji amfani da mumbarinsu wajen hura wutar gaba da kiyayya a tsakanin al'umma.

Bishop Musa wanda ya bayyana haka a cikin sakon sa na goron Kirsimeti, ya ce Yesu kan sa ya yi kira da su zama tsintsiya madaurinki daya.

A cewar sa, haihuwar yesu kira ce ga al'umma da su ki duk yunkurin da zai raba yan Najeriya bisa addini ko kabila.

Ya kara da cewa, shugabanci amana ce mai tsarki da yak**ata duk Shugabannni su san da haka, sannan abin bakin ciki ne wasu sun mayar da kansu kayan aikin shaidan ta hanyar sata da garkuwa da mutane da taaddanci.

Ya yi Allah wadai da kisan kiyashin da akewa al'umma da tashin hankali wanda ya ce yanzu sun zamo kasuwanci mai riba a tsaganin wasu yan tsirarun mutane.

Bunkasa Tsaro: Gwamnatin Jihar Kebbi ta kara Baiwa 'yan sandan ko-ta-Kwana Motoci 4 domin kula da Tsaro na cikin Gari.Ba...
25/12/2025

Bunkasa Tsaro: Gwamnatin Jihar Kebbi ta kara Baiwa 'yan sandan ko-ta-Kwana Motoci 4 domin kula da Tsaro na cikin Gari.

Bashar Muhammad

Da yake Gabatar da Motoci ga Jami'an Mai kula rundunar 'yansanda Masu Shirin ko-ta-Kwana wato MOPOL, a madadin gwamnan jihar Kebbi, Sakataran gwamnatin jihar kebbi , Yakubu Bala Tafida, ya bayyana cewa wannan Karin taimako ne k**ar yadda Gwamnan ya saba yi ga Jami'an Tsaro a kowane lokaci, domin kula da dukiyoyi da lafiyar jama'a da mutuncin Gwamnati.

Track up..SSG Tafida

Da yake bayyana godiya da wannan taimako da Gwamnati Tayi Masu na samun saukin gudanar da aikin su, jami'i Mai kula da MOPOL na Jihar Kebbi, Abubakar Jega ya bayyana jin dadinsu da kulawa da wannan gwamnatin take Baiwa bangaran Tsaro.
Ya Baiwa gwamnati tabbacin yin amfani da wadannan Motoci domin Kare Lafiya da dukiyoyin jama'ar Jihar.

Track up.. MOPOL

Gwamnatin jihar Kebbi ta K**a Mutun 16 ta K**a Buhun Gawayi 50,000 da Katako 7,400.Muhammad BasharMa'aikatar Kula da Gan...
25/12/2025

Gwamnatin jihar Kebbi ta K**a Mutun 16 ta K**a Buhun Gawayi 50,000 da Katako 7,400.

Muhammad Bashar
Ma'aikatar Kula da Gandun daji ta jihar Kebbi, ta bada sanarwar k**a Masu sana'ar Sai da Gawayi Mutun 16 a Jihar, da laifin Karya doka na kona gandun daji bada izini ba, kuma ta k**a buhu 50,000 da kuma Katakaye 7,400 Wanda aka debosu daga dajin Ka'oje, a Cikin Karamar hukumar Bagudu.
Da yake bayani ga manema labarai a Birnin Kebbi, Kwamishinan Ma'aikatar Gandun daji ta jihar Kebbi, Musa Tungulawa Yaja kunnen Masu wannan Sana'a ba bisa ka'ida ba, dasu dinga bin Dokokin Gwamnati domin Cin nasara a Sana'ar tasu dan gudun asara.
Tungulawa Yayi nuni da cewa, sare bishiyu a ko’ina ba bisa ka'ida ba na haifar da samun mummunan chanjin yanayi marar dadi, a dan haka dole masu wannan sana'ar sayar da Katako da Gawayi dasu dinga bin doka da oda domin kaucewa fushin hukuma.
Kwamishinan Yace, Kayan da aka k**a an debo su ne ba bisa ka'ida ba , saboda haka Gwamnati zata sayar da Kayan ga duk mai bukata, saboda haka doka ta tanada, a karkashin Kwamitin da Gwamnati ta kafa karkashin jagorancin Babban Sakataran Ma'aikatar.
Ya kara jan kunnen Masu sana'ar Katakaye da sare bishiyu ba bisa ka'ida ba,cewa yin hakan haramun ne a Jihar Kebbi dama Kasa Nigeria baki Daya, Dan haka su kiyaye doka
Kuma ya bayyana, Gwamnan jihar Kebbi Nasir Idris ya sanya Hannu a kan dokar Kare gandun daji da filaye da sare bishiyu ba bisa ka'ida ba da sunan a sami katako.
Daga Karshe ya nemi duk Mai bukatar Wadannan kaya daya tuntubi Ma'aikatar Kare gandun daji ta Jihar Kebbi domin Karin bayani, Yace Dan haka doka ta tanada.

25/12/2025
Shugaba Tinubu ya kafa kwamitin warware rikice-rikice da dabarun tunkarar zaɓen 2027 a APCShugaban ƙasa Bola Ahmed Tinub...
24/12/2025

Shugaba Tinubu ya kafa kwamitin warware rikice-rikice da dabarun tunkarar zaɓen 2027 a APC

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da wani kwamiti na Dabaru, Warware Rikice-rikice da Wayar da Kai domin magance sabani a cikin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) yayin da jam’iyyar ke shirin tunkarar babban zaɓen 2027.

An ƙaddamar da kwamitin ne a ranar Laraba a birnin Lagos, inda ya ƙunshi gwamnoni na jam’iyyar, mambobin Majalisar Zartarwa ta Tarayya da sauran manyan masu ruwa da tsaki. Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, shi ne Shugaban kwamitin, yayin da tsohon Mai Ba da Shawara kan Shari’a na APC, Muiz Banire, ke matsayin Mamba/Sakatare.

Sauran mambobin kwamitin sun haɗa da Sanata Adamu Aliero, Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya kuma Gwamnan Kwara, Abdulrahman AbdulRazaq, Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jam’iyyar APC kuma Gwamnan Imo, Hope Uzodimma, da gwamnoni Hyacinth Alia (Benue), Umar Namadi (Jigawa), Bassey Otu (Cross River), Abiodun Oyebanji (Ekiti) da Sheriff Oborevwori (Delta).

Haka kuma, gwamna Uba Sani (Kaduna) da Siminalayi Fubara (Rivers), Ministan Harkokin Teku da Tattalin Arzikin Ruwa, Adegboyega Oyetola, Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, da tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, na cikin mambobin kwamitin.

Da yake jawabi a wajen ƙaddamarwar, Mai Mala Buni ya gode wa jam’iyya bisa amincewa da shi da sauran mambobi, yana mai cewa kwamitin zai gudanar da aikinsa cikin ƙwarewa da jajircewa. Ya ce za su yi shawarwari da tattaunawa domin samar da dabaru masu faɗi, nagarta da ɗorewa, tare da samar da tsarin da zai bai wa kowa, musamman masu ƙorafi damar jin ana damawa da su.

Buni ya ƙara da cewa kwamitin zai yi la’akari da matakan kariya da hanyoyin magance barazana tun kafin ta taso, yana mai kira ga mambobi da su guji fifita son rai ko ra’ayin kashin kai a kan muradun jam’iyya.

Tun a ranar Juma’a, 19 ga Disamba, a taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na APC da aka gudanar a Abuja, Shugaba Tinubu ya jaddada muhimmancin haɗin kai a jam’iyya. Ya bayyana wa shugabannin jam’iyyar cewa APC ta ginu ne a kan akidar siyasar ci gaba, faɗaɗa shigar kowa da girmama bambancin ra’ayi.

A cewarsa, dole ne dimokuraɗiyyar Najeriya ta dore, kuma hakan zai samu ne kawai ta hanyar juriya, haƙuri da bai wa kowa wuri a cikin tafiyar siyasa.

Rahotanni daga Jihar Borno sun bayyana cewa wasu mabiya addinin sun rasu sak**akon harin bam da wani mai tayar da bam ya...
24/12/2025

Rahotanni daga Jihar Borno sun bayyana cewa wasu mabiya addinin sun rasu sak**akon harin bam da wani mai tayar da bam ya kai a masallacin Gambarou Jumu’at da ke Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

Kabiru Tukur
Wasu daga cikin mabiya addinin da s**a tsira daga wannan mummunan hari sun bayyana cewa, wadanda s**a kai harin sun shigo cikin masallacin a lokacin sallar Maghrib, inda s**a tashi bam din.
"Bam din ya tashi ne lokacin da ake gudanar da raka'a ta farko na sallar Maghrib. Wasu mabiya addinin sun rasu, wasu kuma sun samu raunuka daban-daban," in ji wani daga cikin wadanda s**a tsira.
Ba a bayyana wanda ya dauki alhakin wannan harin ba, amma daga cikin wadanda ake zargi akwai kungiyar Boko Haram, wadda ta rika kai hare-hare da tayar da bam a wannan yanki cikin watannin da s**a gabata.

Wata gobara ta tashi a daren Talata a Kasuwar Terminus da ke Jos, babban birnin Jihar Filato, inda ta lalata kusan shagu...
24/12/2025

Wata gobara ta tashi a daren Talata a Kasuwar Terminus da ke Jos, babban birnin Jihar Filato, inda ta lalata kusan shaguna 25, k**ar yadda 'yan kasuwa da jami'an kasuwa s**a tabbatar.
Shaidu sun bayyana cewa, jami'an aikin kashe gobara daga Hukumar Wutar Lantarki ta Tarayya da ta Jihar Filato sun yi gaggawar kai dauki kuma sun samu nasarar dakile wutar kafin ta bazu zuwa wasu sassan kasuwar.
Sakataren kasuwar, Zakari Sale, ya shaida wa wakilinmu cewa gobarar ta faru tsakanin karfe 8 na dare zuwa 9 na dare, yana mai cewa lahani ya zama kadan idan aka kwatanta da gobarar da ta faru a baya.
"Kokarin jami'an kashe gobara tare da hadin kai da wasu mutane masu sha'awar taimakawa, ya hana wutar bazuwa da lalata wasu kayan kasuwa. Daga bincikenmu, an gano cewa kusan shaguna 25 ne s**a kone," in ji Sale.
Wannan sabuwar gobara na zuwa ne bayan wata gobara mai girma da ta faru a watan Afrilu 2025, wadda ta lalata sama da shaguna 500, tare da hasarar da aka kiyasta a kan fiye da naira biliyan 1, k**ar yadda jami'an kasuwa s**a bayyana.
Kasuwar Terminus ta sha fuskantar gobara a baya, ciki har da wata gobara a watan Fabrairu na shekarar 2001 da ta lalata manyan sassa na kasuwar, inda ta bar 'yan kasuwa da dama cikin halin kunci na kudi.
A yayin martani ga wannan sabon lamari, Hukumar Kasuwar Jos Main, ta fitar da sanarwa a ranar Laraba, inda ta tabbatar da aukuwar gobarar, amma ta ce binciken farko bai gano musabbabin gobarar ba.
Hukumar ta bayyana cewa, jami'an tsaro sun kulle yankin da gobarar ta shafa don kiyaye dukiyoyin 'yan kasuwa da tabbatar da tsaro kafin 'yan kasuwa su isa kasuwar.

Endrick ya koma kungiyar kwallon kafa ta Lyon daga Real Madrid a matsayin aro
23/12/2025

Endrick ya koma kungiyar kwallon kafa ta Lyon daga Real Madrid a matsayin aro

23/12/2025

Nigeria vs Tanzania Live Commentary

Address

Gidan Daji
Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when JKD Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to JKD Media:

Share