JKD Media

JKD Media Home of JKD Media. Official page of JKD TV DSTV channel 391 and Hamada 91.3FM Kaduna !
(5)

03/08/2026

Yadda Matasa Ke Sauya Duniya Ta Hanyar Fasaha da Jinkai.

01/08/2026

Kadamar da sabon ofishin sojojin sama na Nigeria a umahia.

31/07/2026

A KALLA MUTANE 30 S**A RASA RAYUKANSU A KAUYEN NARIDOM A KARAMAR HUKUMAR KAURU, JAHAR KADUNA.

Shugaba Tinubu Ya Yi Alhinin Rasuwar Tsohon Ministan Kuɗi, Alhaji Abubakar AlhajiShugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ba...
30/07/2026

Shugaba Tinubu Ya Yi Alhinin Rasuwar Tsohon Ministan Kuɗi, Alhaji Abubakar Alhaji

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana alhini kan rasuwar tsohon Ministan Kuɗi kuma fitaccen ɗan siyasa, kuma jami'in gwamnati, Alhaji Abubakar Alhaji, wanda ya rasu yana da shekaru 85.

A cikin wata sanarwa da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar a ranar Alhamis, Tinubu ya bayyana marigayin a matsayin ɗaya daga cikin fitattun masu hidimar ƙasa, wanda ya shafe shekaru da dama yana aiki a manyan muƙaman gwamnati.

Shugaban ya ce marigayi Sardaunan Sakkwato ya yi fice a fannin gudanar da mulki, tare da nuna ƙwarewa wajen tafiyar da harkokin kuɗi da kuma diflomasiyya, lamarin da ya ba da gagarumar gudummawa ga ci gaban tattalin arziki da siyasar Najeriya.

Tinubu ya miƙa ta'aziyyarsa ga Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa'ad Abubakar III, Majalisar Masarautar Sakkwato da daukacin iyalan gidan sarautar bisa wannan babban rashi.

Haka kuma, ya jajanta wa Gwamnatin Jihar Sakkwato, al'ummar jihar, da abokan hulɗa da ɗaliban da marigayin ya koyar tare da jagoranta a sassa daban-daban na ƙasar.

Shugaban ya yi addu'ar Allah Ya gafarta wa Alhaji Abubakar Alhaji, Ya saka masa da Aljannatul Firdausi saboda hidimomin da ya yi wa ƙasa da al'umma, sannan Ya bai wa iyalansa da al'ummar Sakkwato haƙurin jure wannan babban rashi.

30/07/2026

Kasance tare da mu domin
kallon Tataunawa ta Musamman Tare da Kanar Sani Bello (rtd)
Ku biyo mu domin samun kashi na gaba!

A duba shafinmu na Youtube domin samun cikakken tattaunawar.

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Kashe Naira Biliyan 46 Domin Gyaran Filin Jirgin Sama na KanoDaga Aliyu SambaGwamnatin Ta...
30/07/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Kashe Naira Biliyan 46 Domin Gyaran Filin Jirgin Sama na Kano

Daga Aliyu Samba

Gwamnatin Tarayya ta amince da ware Naira biliyan 46 domin gudanar da aikin gyaran manyan filayen sauka da tashin jiragen sama (runways) na Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa na Mallam Aminu Kano (MAKIA), a wani yunƙuri na inganta tsaro da ingancin harkokin sufurin jiragen sama a ƙasar nan.

Ministan Harkokin Sufurin Jiragen Sama da Bunƙasa Sararin Samaniya, Festus Keyamo, ne ya bayyana hakan a ranar Laraba yayin ƙaddamar da sabon ginin tashar jiragen sama ta cikin gida ta Muhammadu Adamu Dankabo da aka kammala gyaranta a filin jirgin saman na Kano.

Keyamo ya ce aikin gyaran manyan filayen jiragen saman zai ƙara tabbatar da tsaron zirga-zirgar jirage, sauƙaƙe gudanar da ayyukan sufurin sama tare da inganta jin daɗin fasinjoji. Ya ƙara da cewa hakan zai ƙara ɗaga matsayin Kano a matsayin babbar cibiyar harkokin jiragen sama a Arewacin Najeriya.

Ya bayyana cewa amincewar da gwamnatin ta bayar na cikin shirinta na ci gaba da inganta ababen more rayuwa a fannin sufurin jiragen sama, domin ƙara inganci, tsaro da bunƙasa ayyukan wannan fanni a faɗin ƙasar.

A yayin ziyarar tasa, Ministan ya kuma ƙaddamar da tashar cikin gida ta Muhammadu Adamu Dankabo da aka sabunta, wadda aka gyara domin inganta ayyukan karɓar fasinjoji da samar da ingantattun kayayyakin more rayuwa a filin jirgin saman.

Shugaba Tinubu Ya Ba da Umarnin Farautar Maharan Kaduna Tare Da Ceto Wadanda Aka SaceShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ...
28/07/2026

Shugaba Tinubu Ya Ba da Umarnin Farautar Maharan Kaduna Tare Da Ceto Wadanda Aka Sace

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi Allah-wadai da harin da aka kai ƙauyen Naridon da ke Ƙaramar Hukumar Kauru a Jihar Kaduna, inda ya umarci rundunonin tsaro su gaggauta farautar maharan tare da kuɓutar da mutanen da aka yi garkuwa da su.

Harin da aka kai da sanyin safiyar Litinin a unguwar Kamaru ya yi sanadin mutuwar kimanin mutum 30, ciki har da mata da yara, yayin da aka ƙone gidaje da dama. Shugaba Tinubu ya bayyana harin a matsayin dabbanci da rashin tausayi da aka aikata kan fararen hula marasa laifi.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Talata a Abuja, shugaban ya ce ya bai wa rundunar soji, 'yan sanda da hukumomin leƙen asiri umarnin ƙara zafafa sintiri da ayyukan tsaro domin kamo masu laifin cikin gaggawa, ceto waɗanda aka sace da kuma dawo da zaman lafiya a yankin.

Tinubu ya kuma gargaɗi masu ƙoƙarin tarwatsa zaman lafiyar da ake samu a Kaduna cewa ba za su tsere wa hukunci ba. Ya miƙa ta'aziyyarsa ga iyalan waɗanda s**a rasu, da Gwamna Uba Sani, da Gwamnatin Jihar Kaduna, tare da al'ummar jihar baki ɗaya.

Shugaban ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da bai wa Kaduna cikakken goyon baya wajen yaƙi da matsalolin tsaro, yana mai jaddada ƙudirin gwamnatinsa na ƙarfafa kayan aikin tsaro da murƙushe ƙungiyoyin masu aikata laifuka. Haka kuma ya buƙaci al'umma su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai domin dakile hare-hare tun kafin su faru.

27/07/2026

60th Anniversary of 29th July Counter Coup.Before and After with Col.Sani Bello Rtd ADC to the Supreme Commander Major General JTU Aguiyi Ironsi

27/07/2026

🔥 AREWA, KU SHIRYA! 🔥🎶

Mun samu damar tattaunawa da fitattun mawakan Arewa guda biyu, Rumerh da Mr442, a wata gajeriyar hira ta musamman game da sabon aikin da suke shirin fitarwa a ranar 1 ga Agusta. 🎤🎬

Me suke shiryawa? 👀🔥
Me ya sa aka zabi ranar 1 ga Agusta? 🤔
Kuma mene ne ya kamata masoya su yi tsammani? 😍🎶

Ku biyo mu domin jin cikakken bayani daga bakin mawakan da kansu! ❤️🔥

Address

Gidan Daji
Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when JKD Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to JKD Media:

Shortcuts

Share