JKD Media

JKD Media Home of JKD Media. Official page of JKD TV DSTV channel 391 and Hamada 91.3FM Kaduna !

20/08/2025

Gwamnan Jahar Katsina Mal. Dikko Umar Radda wanda yanzu haka yake hutun jinya ya tuntubi Mukaddashin Gwamna Farouk Lawal Jube cikin gaggawa dangane da bukatar a tura tawaga domin jajantawa iyalan mamata da al'ummar da akayiwa ta'addanci a unguwar Mantau a karamar hukumar Malumfashi Dake Jahar Katsina

20/08/2025

LABARAN DUNIYA NA YAU 20 08 2025 Tare da Basira Sabo Nadabo

19/08/2025

REAL MADRID VS OSASUNA

Jami’an tsaro sun kwantar da zanga-zangar lumana da aka gudanar a tsakanin Malumfashi da Marabar Ƙanƙara, biyo bayan har...
19/08/2025

Jami’an tsaro sun kwantar da zanga-zangar lumana da aka gudanar a tsakanin Malumfashi da Marabar Ƙanƙara, biyo bayan harin ’yan ta’adda a ƙauyen Gidan Mantau da ke yankin Karfi, wanda ya yi sanadin mutuwar wasu mazauna yankin.

Zanga-zangar wadda ta kasance wata hanya ta nuna damuwa da kuma buƙatar hukumomi su ɗauki tsauraran matakan kare faruwar irin wannan hari a gaba. Tuni dai aka aike da ƙarin jami’an tsaro zuwa yankin da lamarin ya afku domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali.

Rahotanni daga wuraren sun tabbatar da cewa komai ya lafa, tare da buɗe hanyar Malumfashi zuwa Maraba domin cigaba da zirga-zirgar kamar yadda aka saba.

Realmadrid vs Osasuna live commentary. Yau karfe takwas (8pm)!! Zauren Wasanni
19/08/2025

Realmadrid vs Osasuna live commentary. Yau karfe takwas (8pm)!! Zauren Wasanni

18/08/2025

LABARAN DUNIYA NA YAU 18 08 2025 Tare da Zahra Musa

Fursunoni 62 sun tsere daga hannun ’yan bindiga bayan harin jirgin sama na sojojin sama a Danmusa LGA, Jihar KatsinaGwam...
18/08/2025

Fursunoni 62 sun tsere daga hannun ’yan bindiga bayan harin jirgin sama na sojojin sama a Danmusa LGA, Jihar Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina ta tabbatar da nasarar tserewar fursunoni 62 da aka yi garkuwa da su, sakamakon harin da dakarun Sojin Sama na Najeriya s**a kai kan sansanin wani sanannen ɗan fashi, Muhammadu Fulani, da ke ƙauyen Jigawa Sawai, Karamar Hukumar Danmusa – wuri da ke iyaka da Jihar Zamfara.

Daga cikin waɗanda s**a tsere, mutum 12 na samun kulawa a Asibitin Gwamnati na Matazu, yayin da 16 ke tsugunne a sansanin sojojin ƙasa (FOB) na Kaiga Malamai.

Harin sojin sama wanda aka kai a ranar Asabar ƙarfe 5:10 na yamma, ya tilasta wa ’yan fashin barin maboyarsu, abin da ya bai wa fursunonin dama su tsere cikin taro.

A cewar waɗanda aka ceto, harin jirgin sama ya sa ’yan bindigar s**a watse, lamarin da ya ba su damar guduwa daban-daban. Yawancin waɗannan fursunoni an sace su ne daga ƙauyen Sayaya a ranar Litinin, 11 ga watan Agusta, 2025, lokacin da tawagar Fulani ta kai farmaki a daren ranar. Wannan tawaga dai ta shafe lokaci tana addabar yankunan Matazu, Kankia, Dutsinma har ma da wasu sassan Jihar Kano.

17/08/2025

LIVE FOOTBALL COMMENTARY

16/08/2025

LABARAN DUNIYA NA YAU 16 08 2025 Tare da Zahra Musa

Address

Gidan Daji
Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when JKD Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to JKD Media:

Share