21/09/2025
BAYA TA HAIHU: Jami'ar European American University Ta Karyata Labarin Bawa Rarara Digirin Girmamawa Na Dakta
Daga Ahmad Nagudu
Jami'ar European American University, ta fito ta karyata tare da nesanta kan ta da labarin da ke yawo na aninin Dakta da aka ce ta bawa fitaccen mawakin Siyasar nan a Najeriya wato Rarara da wasu mutane a wani bikin bayar da Digirin Girmamawa bisa ficen su da gudummowar da su ke bayarwa a cikin al'umma.
A wata sanarwa da Jami'ar ta wallafa a shafin ta na Yanar Gizo a Hukumance, jami'ar ta bayyana labarin da ke rewadi na bikin da ta gudanar a dakin taro na NICON Luxury Hotel da Abuja a matsayin karya da yaudara wadda kafafen yada labarai a Najeriya ke ta yayatawa wadda ba haka ya ke ba.
A cewar sanarwar, Jami'ar UAU ba ta da masaniya ko hannu a wannan taron da ya gudana a ranar Asabar, 20 ga watan Satumbar 2025 a in da aka ayyana an gudanar da shi, don haka ta ke yekuwar nesanta kan ta da shi da waɗanda su ka jagoranci gudanar da shi a madadin ta.
Ta kuma kara da cewa, Jami'ar European American Universities ba ta bayar ko karrama mutanen da aka bayyana da su ka hada da Dauda Kahutu Rarara da Alhaji Ahmed Saleh jnr. da Mustapha Abdullahi Bujawa da Tarela Boroh da Digirin Girmamawa na "doctorate degrees" ba. Domin duk wadda Jami'ar ta karrama da irin wannan aninin girmamawar ta kan wallafa su ne a shafin ta na Yanar Gizo a https://europeanamerican.university/about/register-of-graduates wadda su kuma waɗannan sunaye da ke sama duka babu su a cikin shafin na ta.
Bugu da ƙari, wadda ya bayyana a matsayin wakilin Jami'ar na Arewacin Najeriya a wajen taron, wato Musari Audu Isiyaku, makaryaci ne kuma mayaudari wadda ba shi da hurumin magana ko wakiltar Jami'ar a Hukumance.
Sannan wadda aka bayyana a matsayin memba na Majalisar Gudanarwa na Jami'ar wato Idris Aliyu, wadda har ya wakilci shugaban Jami'ar, shima ba gaskiya ba ne, domin babu wata Majalisar Gudanarwa a Jami'ar ballantana har ya wakilci shugaban ta.
Jami'ar ta nada Idris Aliyu ne a matsayin Kwararre a fagen Gudanar da Kudi tun shekarar 2024, wadda kuma ta soke wannan nadin yanzu saboda hada kai da shi wajen yin wannan yaudara da damfara da sunan Jami'ar ba tare da izini ba.
A kan haka, Jami'ar ta ci alwashin tuntubar Hukumomin Shari'a na Najeriya don daukar mataki akan masu bayar da shaidar takardun Jami'o'i na bogi ga wasu mutane da daukar matakin doka a kan su.
Nagudu TV ta lura da cewar, a jiya Asabar ne dai labari ya bulla tare da yawo a kafafen Sada Zumunta na zamani kan bawa Mawaki Rarara aninin Dakta kan ficen da ya yi a fagen waka da kuma taimakawa mutane, wadda batun ya yi matukar jawo cece-ku-ce a tsakanin al'umma. Tsakanin masu ganin dacewar bawa Rararan aninin Daktan da kuma masu sukar hakan, duk da masana a fagen ilmi sun yi ta kokarin fahimtar da mutane iri da matsayi da bambancin kalmomin Dr. na ilmi a aikace da kuma na karramawa a kan wani abu da mutum ya shahara da shi.
Ahmad Nagudu
Nagudu TV
21-09-2025