Luguden Wuta

Luguden Wuta Luguden Wuta — The Voice of War and Truth. We uncover the hidden battles shaping our world — from Africa to the Middle East. Real conflicts. Real consequences.

Real stories.

Sak**akon Luguden Wutar da Amurka tayi a Venuzuela, shugan Amurkan ya tabbatar da k**a shugaban kasar Venuzuela Nicolas ...
03/01/2026

Sak**akon Luguden Wutar da Amurka tayi a Venuzuela, shugan Amurkan ya tabbatar da k**a shugaban kasar Venuzuela Nicolas Maduro

Breaking: Kasar Amurka Na Ta Zuba Luguden Wuta A Babban Birnin Kasar Venuzuela.
03/01/2026

Breaking: Kasar Amurka Na Ta Zuba Luguden Wuta A Babban Birnin Kasar Venuzuela.

An Samu Tabbacin Rasuwa Mutum Goma A Wani Harin Bomb Da Aka Kai A Masallacin Juma'a Dake Garin Maiduguri.
24/12/2025

An Samu Tabbacin Rasuwa Mutum Goma A Wani Harin Bomb Da Aka Kai A Masallacin Juma'a Dake Garin Maiduguri.

Babban Hafsan Rundunar Sojin Kasar Libya Mohammed Ali Ahmed al-Haddad Ya Mutu A Hatsarin Jirgin Sama, Yayin Da Yake Dawo...
24/12/2025

Babban Hafsan Rundunar Sojin Kasar Libya Mohammed Ali Ahmed al-Haddad Ya Mutu A Hatsarin Jirgin Sama, Yayin Da Yake Dawowa Daga Kasar Turkiye.

DA ƊUMI-ƊUMI: Ministan Tsaro Badaru Ya Ajiye MuƙamiMinistan Tsaron Najeriya, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, ya yi mura...
01/12/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Ministan Tsaro Badaru Ya Ajiye Muƙami

Ministan Tsaron Najeriya, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, ya yi murabus ba zato ba tsammani, yana mai danganta hakan da dalilan lafiyar sa.

Fadar Shugaban Kasa ta tabbatar da cewa Badaru ya miƙa wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu wasikar murabus dinsa mai kwanan watan 1 ga Disamba. Shugaban kasar ya karɓa tare da gode masa bisa hidimar da ya yi wa ƙasa, inda ya bayyana cewa za a mika sunan sabon minista ga Majalisar Dattawa cikin mako.

A gefe guda kuma, tsohon Shugaban Sojoji, Janar Christopher Musa, ya gana da Shugaba Tinubu a fadar Villa da yammacin Litinin. Ba a bayyana cikakken bayanin tattaunawar ba, amma majiyoyi sun ce ganawar na iya zama tana da alaƙa da sabuwar kujerar Ministan Tsaro, musamman a wannan lokaci da ƙasar ke fama da ƙarin kalubalen tsaro.

LABARI'Yan Shi’a a Jihar Kano Sun Kalubalanci Donald TrumpMabiya mazhabar Shi’a a Jihar Kano sun gudanar da wani gagarum...
08/11/2025

LABARI

'Yan Shi’a a Jihar Kano Sun Kalubalanci Donald Trump

Mabiya mazhabar Shi’a a Jihar Kano sun gudanar da wani gagarumin jerin gwano mai taken “Ƙaryarka Ta Sha Ƙarya”, domin nuna adawarsu ga barazanar da shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump, ya yi na kawo hari a Najeriya.

Masu zanga-zangar sun bayyana cewa wannan barazana ta Trump ba abinda zasu ɗauka da wasa bane, tare da yin kira ga gwamnatin Najeriya da ta tsaya tsayin daka wajen kare martabar ƙasar da mutuncin ‘yan ƙasa.

An gudanar da zanga-zangar cikin natsuwa da lumana, yayin da jami’an tsaro s**a kasance a wurin don tabbatar da zaman lafiya.

Luguden Wuta

KASAR RUSSIA TA KAFA DOKA MAI TSAURI DON KARE MARTABAR MANZON ALLAH.Shugaban Rasha, Vladimir Putin, ya rattaba hannu kan...
07/11/2025

KASAR RUSSIA TA KAFA DOKA MAI TSAURI DON KARE MARTABAR MANZON ALLAH.

Shugaban Rasha, Vladimir Putin, ya rattaba hannu kan wata doka da ta tanadi hukunci mai tsanani ga duk wanda aka k**a da laifin zagin Annabi Muhammadu (SAW) ko ƙona Alƙur’ani Mai Tsarki.

Shugaba Putin ya bayyana cewa, a ƙasar Rasha, laifi ne mai tsanani ƙona Alƙur’ani ko yin magana ta raini game da Annabi Muhammadu (SAW).

Hukumar Zabe ta ayyana Samia Suluhu Hassan, a matsayin wadda ta  lashe zaben shugaban kasar Tanzania a karo na biyu, ta ...
01/11/2025

Hukumar Zabe ta ayyana Samia Suluhu Hassan, a matsayin wadda ta lashe zaben shugaban kasar Tanzania a karo na biyu, ta lashe zaben da kaso 97.66 na kuri'un da aka kaɗa.

Domingo, Bawan da ya dirkawa matar megidansa da ƴaƴan ta biyu ciki a kasar Spain 1803.
28/10/2025

Domingo, Bawan da ya dirkawa matar megidansa da ƴaƴan ta biyu ciki a kasar Spain 1803.

Shugabar Tanzania mace  ta farko, Samia Suluhu, wacce ta tasaya takara a karo na biyu don neman zarcewa, a zaben da za'a...
24/10/2025

Shugabar Tanzania mace ta farko, Samia Suluhu, wacce ta tasaya takara a karo na biyu don neman zarcewa, a zaben da za'ayi a ranar 29 ga Oktoba. Dayawa daga abokan hamayyarta ta garkame su a gidan yar,i wasu kuma an dakatar dasu daga karawa da ita.
A halin yanzu, adadi mai yawa na yan adawar ta sun bace bat babu amo babu labarin su.

Toh idan mace tayi haka ga yan adawa, me kake tsammani daga maza da s**a saba murza siyasa?😆

Address

Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Luguden Wuta posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Luguden Wuta:

Share