Jamhuriyya

Jamhuriyya Domin samun ingantattun kuma sahihan labaran kasa dana ketare hadi da labaran wasanni kasance da jar

Yadda Wani Matashi Dan Kabilar Ibò Ya Taimaki Wata Bahaushiya Ta Haifi 'Yan Biyu A Garin Malumfashi Wannan lamarin ya fa...
24/08/2024

Yadda Wani Matashi Dan Kabilar Ibò Ya Taimaki Wata Bahaushiya Ta Haifi 'Yan Biyu A Garin Malumfashi

Wannan lamarin ya faru ne da gaske a cikin kasuwar garin Malumfashi dake jihar Katsina.

Wata mata mai juna biyu ta shigo kasuwa da niyyar yin siyayya, sai kwatsam kuma Allah ya kawo mata lalurar haihuwa a cikin kasuwar, inda ta nemi agaji a wurin wani mutum bahaushe ɗan uwanta, amma ya ƙi ya taimaka mata, ya yi banza da ita duk da ganin irin halin neman tamakon gaugawa da take.

Ba ta samu wani taimako daga wajen duk sauran jama'a ba sai shi wannan matashi mai suna CHIJIOKE duk da ya kasance akwai bambamcin ƙabila da addini tsakanin su da wannan mata amman hakan bai hana daya lura cewa matar nan tana bukatar taimako akan haifuwar da zatai ba ya taimaka mata.

Alokacin da Allah Ya sa CHIJIOKE ya lura da alamun cewa cewa wannan mata tana buƙatar taimako haifuwa za ta yi, nan take ya ruɗe ya nufo kanta ya je ya nemi mai baro aka saka ta ya ɗauko ta ya fito da ita bakin kasuwa, sannan kuma ya kara zuwa ya samo mai Keke Napep ya ɗauke ta a ciki s**a hanzarta da ita zuwa asibiti.

Allah Sarki! CHIJIOKE koda s**a je asibitin gwamnati sai s**a tarar a dukka asibitin gaba ɗaya ko ina babu gado, sai ya juya ya nufi asibitin kudi da ita (private), inda suna isa aka ce tana bukatar jini, a nan take ya bada jininsa aka sa mata, yanzu haka maganar da ake matar tana nan ta haihu ta haifi ƴaƴa biyu lafiya.

Wane darasi kuka samu a cikin wannan labari?

Daga It'z Kamalancy

Ganduje zai mika mulki ranar Lahadi domin halartar bikin rantsar da zababben shugaban kasa TinubuGwamnan jihar Kano mai ...
28/05/2023

Ganduje zai mika mulki ranar Lahadi domin halartar bikin rantsar da zababben shugaban kasa Tinubu

Gwamnan jihar Kano mai barin gado, Dr. Abdullahi Umar Ganduje zai gudanar da aikin mika ayyukan jihar a hukumance ga zababben gwamnan, Engr. Abba Kabir Yusuf. Inji Muhammad Garba

Malam Garba ya yi nuni da cewa kwamitocin mika mulkin guda biyu sun gana a cikin satin da ya gabata inda aka gabatar da takardar mikawa kwamitin da aka zaba na gwamna tare da aiwatar da ajandar da ta dace kan bikin mika mulki.

Kwamishinan ya bayyana cewa Gwamna Ganduje zai tafi Abuja a matsayin shugaban tawagar Kano don kaddamar da zababben shugaban kasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a ranar Litinin, 29 ga watan Mayu.

Ya ce tafiyar gwamnan ta kuma zama tilas ne don kaucewa wa’adin rufe filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe Internation Abuja domin bikin rantsuwar.

Sanarwar ta yi kira ga jama’a da su ci gaba da yi wa jihar addu’ar zaman lafiya da ci gaba.

Thiago Silva a kan dalilin da ya sa ya tsawaita kwantiraginsa a watan Fabrairu:  "Ba don kudi ba ne, Saboda soyayyar da ...
28/05/2023

Thiago Silva a kan dalilin da ya sa ya tsawaita kwantiraginsa a watan Fabrairu:

"Ba don kudi ba ne, Saboda soyayyar da nake yi wa kulob din, na yi imanin kulob din yana bukatata a wannan lokacin, a ciki da wajen fili, don sake gina fasalin kulob din, Ina ganin tsantsar soyayyar magoya bayan Chelsea.”

Fagen Wasanni

Yanzu yanzu:Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kara wa'adin ci gaba da amfani da tsaffin kudi har zuwa ranar 10 ga watan ...
16/02/2023

Yanzu yanzu:
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kara wa'adin ci gaba da amfani da tsaffin kudi har zuwa ranar 10 ga watan Afrelu, 2023.

Sai dai, shugaban kasar ya ce iya tsohuwar Naira dari ce ne kawai bankuna za su ci gaba da ba 'yan Nigeria, banda N500 da N1,000.

A Daure Duk Dan Kasuwar Da Ke Shigo Da Tufafi Daga Kasar Waje: DangoteA jawabinsa:“Ga masana’antar saƙar tufafi, na yi i...
10/02/2023

A Daure Duk Dan Kasuwar Da Ke Shigo Da Tufafi Daga Kasar Waje: Dangote

A jawabinsa:

“Ga masana’antar saƙar tufafi, na yi imanin ya kamata gwamnati ta tsara doka a Majalisar Dokoki ta ƙasa da za ta sa duk wanda ya sayar da kayan saƙar tufafi na ƙasashen ƙetare da aka haramta, dole ne ya fuskanci zaman gidan yari ba tare da ba shi zaɓin biyan tara ba. Don haka za a ɗaure shi ne kawai, ko da na shekara biyu ne kawai.

"Ainihin da ke faruwa a masana'antar saƙar tufafi ba tsadar wutar lantarki ba ne. Harkar saƙar tufafi ba za ta yiwu ba idan kuka ba su wuta mai rahusa amma ana ci gaba da fasa ƙwauri."

"Abin da ke faruwa shi ne, kamfanonin ƙasashen waje suna hankaɗo da kayayyakinsu Najeriya.

"Shi ya sa ba na son shigo da kayayyaki daga kasashen waje. Lokacin da kuke shigo da kaya, kuna shigo da talauci ne tare da fitar da wadata da guraben aikin yi."

Kasashe a duk fadin duniya na aika wa kasar Turkiyya da Syria kayan agaji bayan da s**a fuskanci girgizar kasa mai tsana...
09/02/2023

Kasashe a duk fadin duniya na aika wa kasar Turkiyya da Syria kayan agaji bayan da s**a fuskanci girgizar kasa mai tsanani.

A cikin kayan akwai ruwan sha da barguna da kayan abinci da kayan sawa, da dai sauransu.

Ƙalubalen da ƴaƴa mata suke fuskanta a yayin da suke son ci gaba da karatu a makarantar gaba da sakandare.Wasu daga ciki...
05/02/2023

Ƙalubalen da ƴaƴa mata suke fuskanta a yayin da suke son ci gaba da karatu a makarantar gaba da sakandare.

Wasu daga cikin iyayen su na da dabi'ar nan ta yayansu ci gaba da karatu musamman a yankin arewacin Najeriya, bayan Yara. Sun kammala malarantun sikandire.

Wasu iyayen kan Yi togaciya da cewa aure yaran za su yi, ba karatu ba, Koda kuwa a lokacin yarinya Bata da wani tsayayye.

ƴan mata da yawa na fuskantar barazana a yayin da iyayensu ke dakile musu ci gaba da karatu saboda maganar aure.

Hakan na nufin bayan mace ta gama sakandare sai ta ci gaba da zama a gida babu karatu babu sana'a, kuma suna da burin yin karatu a rayuwar su amma babu hali kasancewar iyayensu basa son karatun.

Hakan na jefa rayuwar matan a cikin garari, saboda saboda zama waje daya, babu wani abin yi ga bukatun rayuwa daban daban babu mai iya daukar nauyin yi su, sanadin hakan ƴan mata dayawa sun zaɓi su bayar da kansu domin abasu kudi su biyawa kansu bukatar gaban su.

Wasu iyayen suna kallo yarinyar su na kashe kashen kudi ko Siyan sutura masu tsada amma ba za su tambayi inda ta samu kudin ba.

Sakamakon rashin sanin makomar su a rayuwa babu tsayayyen saurayi bare suyi tunanin aure,suna da burin suyi karatu mai zurfi domin cimma wani buri da suke son cimma a rayuwa, Hakan ya gagara daga bangaren iyayen su.

Wani Karin ƙalubalen shine yadda wasu daga cikin iyaye s**an hana ƴar su tayi aiki yayin da tayi karatu mai zurfi amma su ce baza tayi aiki ba ta zauna a gida har sai ta samu miji tayi aure, alhalin wasu ko saurayi basu dashi sun gama karatu sun karɓi sakamako mai kyau amma iyayen su sun hana su suyi aiki gani suke barin Mace tayi aiki kamar lalacewa za tayi.

Wadannan dama wasu Taron kulabalen na Nan Jingim, Wanda hakan ke bukatar mahukunta su Kara tsayawa a tsaye wajen yaki da wannan matsala.

Za a iya cimma nasara kan hakan ta hanyar tuntubar iyayen cikin harshe na laushi, Wanda watakila a iya jawo hankalin su domin su sauka daga kan wan can ra'ayi nasu na rikau.

Daga salma Hussain Abubakar

Gwamnan CBN Karya Yake Yiwa Shugaba Buhari: Mai Magana Da Yawun Shugaban KasaBabban hadimin shugaban kasa kan lamuran ja...
05/02/2023

Gwamnan CBN Karya Yake Yiwa Shugaba Buhari: Mai Magana Da Yawun Shugaban Kasa

Babban hadimin shugaban kasa kan lamuran jama'a, Ajuri Ngelale, ya bayyana cewa karyar kawai gwamnan babban bankin Najeriya, Godwin Emefiele, ya shararawa shugaba Muhammadu Buhari. Ngelale yace maganar cewa akwai isassun kudi a cikin gari babu kamshin gaskiya ciki,

Ya bayyana hakan ne a hirar da ya gabatar a tashar TVC inda yace mutane su daina ganin laifin shugaba Buhari, bayanan da ya samu yake amfani da su.

Ya ce mutane bai zai taba yin abu don tsanantawa jama'a da gayya ba. A cewarsa: "Abinda muke yi shine tabbatar da cewa shugaban kasa na samun labaran gaskiya kuma labarin da CBN ya bada cewa an baiwa bankuna isassun kudi a fadin tarayya karyar banza ne. Wannan ya bayyana yanzu."

"Shugaban kasa na jama'a ne, labaran karya kawai yake samu daga wajen CBN, shi yasa aka kara wa'adin daga Junairu 31 zuwa 10 ga Febrairu."

Daga Salma Hussain Abubakar

Cika baki ba naka bane, ka roki Allah ya yafe maka bala’o’in da ka dirka wa mutanen Kaduna shi ya fi maka – Rundunar Pet...
05/02/2023

Cika baki ba naka bane, ka roki Allah ya yafe maka bala’o’in da ka dirka wa mutanen Kaduna shi ya fi maka – Rundunar Peter Obi ga El-Rufai

Rundunar Kamfen din dan takarar shugaban kasa na Labour Party, Peter Obi sun maida wa gwamnan Kaduna da martani cewa maimakon cika baki da yaki yi a kafafen yada labari, abinda ya fi dace masa shine ya yi gaggawar komawa ga Allah ya nemi gafarar sa kan bala’o’in da ya gallaza wa mutanen Jihar Kaduna.

Idan ba’a manta ba El-Rufai ya bayyana a hira da yayi da talbijin din Channels cewa Peter Obi yan a batya ruwa ne kawai amma ba tsairin da za suyi a zaben shugaban kasa da ya karato a kasar nan.

El-Rufai ya ce Obi na yin amfani da kabilanci da addini ne a wajen neman jama’a wanda hakan ba zai sa ya samu abinda yake so ba a zabe mai zuwa.

A martani da rundunar s**a maida wa gwamnan, Darekta janar din rundunar Kamfen din Obi Akin Osuntokun ragargaji gwamnan inda yake cewa shine gogarmar nuna kiyayya da kabilanci, domin shine ya fara yin haka a Kaduna inda ya yakice wani bangaren jihar ya kirkiro muslim-muslim.

” Ina so in sanar da El-Rufai, idan aka da sahihin zabe a kasar nan, tabbas Obi na LP ne zai yi nasara, ko shakka babu. Abu daya da na sani shine ko Obi ya yi nasara ko bai yi nasara ba ya kafa tarihi a kasar nan.

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnan Jigawa ya naɗa sabon Sarkin DutseGwamna Muhammad Badaru Abubakar na jihar Jigawa ya amince da nadi...
05/02/2023

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnan Jigawa ya naɗa sabon Sarkin Dutse

Gwamna Muhammad Badaru Abubakar na jihar Jigawa ya amince da nadin Muhammad Hameem Sanusi a matsayin sabon Sarkin Dutse daga yau Lahadi.

Hakan ya biyo bayan amincewar kwamitin mutane bakwai na masu naɗa Sarki a masarautar Dutse, inda su ka zaɓi Muhammad Hameem a matsayin sabon Sarkin Dutse da dukka kuri’u bakwai a cikin ‘yan takara uku da ke neman kujerar sarauta.

Nadin dai ya zo ne ƙasa da kwanaki bakwai da rasuwar Sarkin Dutse, Nuhu Muhammadu Sanusi.

An tattaro cewa, daga bisani an mika wannan amincewa ga majalisar Sarakunan Jihar Jigawa, wacce ita ma ta amince da matakin da masu naɗa Sarkin su ka ɗauka.

Sanarwar ta ce Majalisar Sarakunan ta aike da sunan Muhammad Hameem, wanda ɗan marigayi Sarkin Dutse ne, da sauran ’yan takara biyu zuwa wajen neman amincewa.

A cikin sakon fatan alheri ga sabon sarki, Gwamna Badaru ya taya sarkin murna tare da yi masa fatan Allah ya shiryar da shi, da hikima da kuma kariya a tafarkinsa.

🟨 Yalon katin da Vinicius Jr ya samu zai sanya Ba zai buga wasan La Liga na Real Madrid na gaba da Elche CF ba.Daga Fage...
05/02/2023

🟨 Yalon katin da Vinicius Jr ya samu zai sanya Ba zai buga wasan La Liga na Real Madrid na gaba da Elche CF ba.

Daga Fagen wasannin

Atiku Abubakar Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Wurin Al-ummar Jihar SokotoA yau Talata mai girma wazirin Adamawa Alhaji Atiku...
01/02/2023

Atiku Abubakar Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Wurin Al-ummar Jihar Sokoto

A yau Talata mai girma wazirin Adamawa Alhaji Atiku Abubakar, ya kaddamar da yakin neman zaben shi a jihar Sokoto.

Al-ummar jihar Sokoto sun yiwa Atiku Abubakar Kyakkyawar tarba tare da nuna tsantsar kauna a yayin da ya ziyarci jihar.

A yayin gudanar da taron, al'ummar jihar Sokoto sun yiwa mai girma wazirin Adamawa alkawarin kuri'un su nashi ne.

Insha'Allah Atiku Abubakar zai zama shugaban kasar Najeriya, kawai lokaci muke jira.

Saudiyya ta amincewa Ronaldo yai zaman dadiro da sahibar sa GeorginaRahotanni daga kasar Saudiyya na nuni da cewa Cristi...
08/01/2023

Saudiyya ta amincewa Ronaldo yai zaman dadiro da sahibar sa Georgina

Rahotanni daga kasar Saudiyya na nuni da cewa Cristiano Ronaldo da sahibar sa, Georgina Rodriguez za su sami takardar izinin zama tare, duk kuwa da dokar da ƙasar ta yi mai tsauri a kan zaman dadiro.

Dan wasan mai shekaru 37 ya koma Al-Nassr ta Saudiyya kan kwantiragin shekara biyu da rabi ta kimanin fam miliyan 173 a kakar wasa bayan kwantiraginsa da Manchester United ta rushe.

Sai dai kuma zaman Ronaldo tare da Georgina zai kasance karya dokar auratayya a Saudiyya.

A cewar jairdar wasanni ta Sport, Ronaldo mai ƴaƴa biyar, da kuma Georgina, wa ce ta haifa masa ƴaƴa biyu, za su samu izinin zaman ne duba da cewa ya na ɗaya daga cikin ƴan wasan da s**a fi kasuwa a duniya.

Rahoton ya ci gaba da ambato wasu lauyoyin Saudiyya biyu, wadanda ke hasashen hukumomi ba za su tsoma baki a kan lamarin ba.

Wani daga cikin lauyoyin ya ce: “Ko da yake har yanzu dokokin sun haramta zaman dadiro a Saudiyya, amma hukumomi sun fara kau da kai kuma ba za su hukunta kowa ba.

"Hakika, ana amfani da waɗannan dokokin ne lokacin da aka samu matsala ko kuma wani laifi."

Lauya na biyu ya kara da cewa: "Kawo yanzu, hukumomin Saudiyya ba su tsoma baki a cikin wannan al'amari ba (wanda ya shafi yan kasashen waje), amma doka ta ci gaba da haramta zaman dadiro a ƙasar," in ji shi.

2023: Zan ɗora a kan nasarorin Buhari -- TinubuDan takarar shugabancin kasa na jam’iyyar APC, Ahmed Tinubu, ya ce zai do...
15/11/2022

2023: Zan ɗora a kan nasarorin Buhari -- Tinubu

Dan takarar shugabancin kasa na jam’iyyar APC, Ahmed Tinubu, ya ce zai dora kan nasarorin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya samu a cikin shekaru bakwai da s**a gabata.

Tinubu ya bayyana haka ne a yau Talata a Jos a wurin ƙaddamar da yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC na 2023.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC ya bayyana cewa Buhari ya taka rawar gani a fannin samar da ababen more rayuwa tare da kafa ginshikin bunkasa noma da sauran fannoni.

“Ba mu da kwanciyar hankali, sai mu ka koma ga Janar Muhammadu Buhari mai ritaya, ya kuma fara farfadowa da kwato Najeriya.

“Ya fara ne da lalata tutocin ƴan ta’adda abisa tsari, dabara da kuma hikima, kuma a yau babu wata tuta a kananan hukumominmu a Nijeriya.

“Najeriya ta fara nutsewa amma sai Buhari ya tsamo mu ya kuma ce Najeriya ba za ta nutse ba a zamaninsa da kuma lokacin APC,” inji shi.

Ya bayyana cewa Buhari ne ya jagoranci gudanar da zaben fidda-gwani na gaskiya da inganci wanda ya samar da shi a matsayin mai rike da tuta.

Address

Kaduna

Telephone

+2348106949003

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jamhuriyya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jamhuriyya:

Share