DMCV News Hausa

DMCV News Hausa Sss

04/08/2026

WAKILIYAR NAJERIYA A KASAR YAHUDU TA K**A AIKI

DMCV News Hausa

Sabuwar Wakiliyar NAJERIYA a Kasar Yahudu Uwargida Nkechi Linda Ufochukwu ta K**a Aiki.

Ufochukwu wadda ta mika takardunta ga shugaban kasar ta Israel Youzorg ta Kuma isar da sakon fatan Alkhairi na shugaba Tinubu ga kasar.

menene ra'ayinku?

A YANZU DAI A JIHAR KATSINA BA DANTAKARA K**AR DIKKO _Wata Sabuwar KungiyaDMCV News HausaAn bayyana cewa a halin da ake ...
02/08/2026

A YANZU DAI A JIHAR KATSINA BA DANTAKARA K**AR DIKKO _Wata Sabuwar Kungiya

DMCV News Hausa

An bayyana cewa a halin da ake ciki dai babu tsayayyen Dan takarar Gwamna a Jihar Katsina kamar Gwamna Malam Dikko Umar Radda.

Shugaban wata Sabuwar Kungiya ta siyasa a Karamar Hukumar Malumfashi Mai suna "Mafita Daya Ce Dikkon Dai" Aliyu S. Mohd shine ya Sanar da haka yayin da ziyarci sabon office din DMCV MEDIA a Malumfashi.

Aliyu Mohd ya ce tabbas akwai Yan takara uku aJam'iyyu uku da s**a hada da APC, ADC da PDP Amma Jamiyyyun biyu na ADC da PDP sun kasa warware rigingimun su na cikin gida.

Ya Kara da cewa a daidai lokacin da Jamiyyyar APC ta shirya dan fara campaign su sauran jam'iyyun sun kasa tabbatar da sahihanci mutum guda a matsayin Dan takara.

Shugaban Kungiyar ta MAFITA DAYA CE, DIKKON NE yace a lokacin da har yanzu wasu jagororin ADC s**a ki yadda su Mara ma Babban Kaita baya, Sai ga Shi a PDP ma ana maganar Bangaren Wike da naTanimu Turaki Kuma duk suna da Yan takara.

Ya shawarci al'ummar Malumfashi da ma jihar Katsina da su bude idonsu su baiwa Dikko dama ya idasa shekarun Shi 4 kamar yadda marigay Umaru Musa, Shema da Masari su ka yi.

23/07/2026
DMCV MEDIA SUN YI SABON  OFFICE A MALUMFASHIDMCV News HausaA ranar Laraba 22 ga watan Yulin 2026 da misalin 4:30 na yamm...
23/07/2026

DMCV MEDIA SUN YI SABON OFFICE A MALUMFASHI

DMCV News Hausa

A ranar Laraba 22 ga watan Yulin 2026 da misalin 4:30 na yamma Yan uwa da abokan arzikin Surajo Danlami Aliyu Danjinkau Babban Edita na kamfanin DMCV MEDIA su ka taru Dan bude sabon office a Mahaifar shi Garin Malumfashin jihar Katsina.

An gabatar da jawabai da fatan Alkhairi tare da yaba ma Dan jaridar Kan irin kwazo da Fadi Tashin shi.

Malam Sabitu Lawal jami'i Mai duba makarantu a Hukumar Ilimi Day A C Bashir Adamu daga Hukumar Hana Sha da fataucin kwayoyi NDLEA Na daga cikin wadanda su ka gabatar da jawabai.

A nashi gajeren jawabin Surajo Danlami Aliyu Danjinkau ya ce sun bude office din ne dan Kara fadada aikin su da Kai Shi kusa da al'umma.

Mataimakin shugaban kwamitin Amintattu na DMCV Kuma Marubuci na musamman Malam Atiku Hashimu ya jagoranci addu'o'i da aka gudanar a wurin taron.

S Mohd

‎'AN YI KIRA GA YAN SOCIAL MEDIA NA M/FASHI DMCV News HausaAn yi kira ga Yan Social Media Na Ƙaramar Hukumar Malumfashi ...
21/07/2026

‎'AN YI KIRA GA YAN SOCIAL MEDIA NA M/FASHI

DMCV News Hausa

An yi kira ga Yan Social Media Na Ƙaramar Hukumar Malumfashi da su kyauta a ayyukan su ta hanyar Mutunta hakkin Al'umma.

Wani jigo a siyasar Karamar Hukumar Kuma tsohon babban sakatare a Gwamnati tsohon Gwamna Malam Aminu Bello Masari, Dr. Aminu Garba Waziri ne yayi wannan kiran a lokacin da ya gudanar da wani muhimmin zamai domin tattauna hanyoyin inganta yadda suke gudanar da aikinsu na yaɗa labarai da amfani da kafafen sada zumunta wajen bunƙasa al'umma.

Dr. Aminu Waziri ya yi kira ga masu amfani da kafafen sada zumunta da su riƙa kiyaye mutunci da martabar mutane yayin gudanar da aikinsu.

‎Ya kuma jaddada muhimmancin yabawa da bayyana duk wani aikin alheri da gwamnati ko masu ruwa da tsaki s**a aiwatar domin ci gaban gari, yana mai cewa hakan na ƙara ƙarfafa gwiwar masu yin ayyukan alheri su ci gaba da hidimtawa al'umma.

Abokin aiki K**ala Bala K**alancy ya ruwaito cewa ‎taron ya samu halartar ɗimbin masu amfani da kafafen sada zumunta daga sassa daban-daban na Ƙaramar Hukumar Malumfashi, Kuma Mahalarta taron sun bayyana matuƙar farin cikinsu da godiyarsu ga Dr. Aminu Waziri bisa wannan gayyata da kuma irin shawarwari da ƙarfafawar da ya ba su.

‎Sun bayyana cewa wannan zama ya nuna yana daraja gudummawar da suke bayarwa wajen wayar da kan al'umma da yaɗa labarai, tare da nuna cewa Dr. Aminu Waziri ya fahimci muhimmanci da matsayin da suke da shi a cikin al'umma.

K**alancy/DMCV

BABBAR MAGANA
08/07/2026

BABBAR MAGANA

FATAN ALKHAIRI DA TAYA MURNAMujallar Yam-MakarantaHukumar Gudanarwa ta DMCV Media mail su buga Mujallar Yam-Makaranta na...
30/06/2026

FATAN ALKHAIRI DA TAYA MURNA
Mujallar Yam-Makaranta

Hukumar Gudanarwa ta DMCV Media mail su buga Mujallar Yam-Makaranta na taya Hedimistress ta Makarantar Firamare ta Dr. Asma'u Dodo Girls Day da ke Malumfashi Hajiya Iyatu murnar kammala aikin koyarwa bayan ta shafe tsawon shekaru 35 tana yi wa gwamnati hidima
Haka nan Kuma tana shima Malam Sa'adu Sani dake LEA malumfashi shima murnar kammala aiki a tsawon shekaru 35 Allah ya yi masu jagora a sauran al'amuransu na rayuwa..

Address

Kaduna

Telephone

+2348036411514

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DMCV News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share