DMCV News Hausa

DMCV News Hausa Sss

24/07/2025
DMCV MEDIA NA NEMAN WAKILAI A KANO, KATSINA, JIGAWA, ZAMFARA DA ZARIAWannan kafar yada labarai Mai buga Mujallun DMCV Ne...
24/07/2025

DMCV MEDIA NA NEMAN WAKILAI A KANO, KATSINA, JIGAWA, ZAMFARA DA ZARIA

Wannan kafar yada labarai Mai buga Mujallun DMCV News Hausa, Yam-Makaranta, Tijjaniya-Ibrahimiyya da Kuma Mujallar Yar-Talla na neman wakilai a wadannan Jihohi.
Akin su
_Nemo sahihan labarai
_Nemo Talla da Sanarwa
_Yada/Raba mana Mujallun
_Zama Jakadu, Idanuwanmu a wannan jiha
_Su kasance suna da Mu'amala da Malamai, Yan siyasa da Yan Kasuwa.

Contact/Tuntubi 07086935640

Management

22/07/2025

JAGORAN NNPC YA GANA DA SHUGABA TINUBU

DMCV NEWS HAUSA

Rahotanni sun nu na cewa jagoran jam'iyyar NNPP Kuma tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya gana da Shugaba Bola Tinubu a ranar Litinin a fadar shugaban kasa.

Wannan ganawar da aka gudanar ta sirri ta biyo bayan halartar Kwankwaso taron Nigeria Forest Economy Summit 2025 da aka gudanar a dakin taro na fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Wannan shi ne karo na biyu da aka samu yin ganawa tsakanin Kwankwaso da Tinubu a cikin sama da shekaru biyu da s**a gabata.

In za a iya tunawa a ranar 9 ga Yuni, 2023, kwana kadan bayan rantsar da Tinubu a matsayin shugaban ƙasa. Wannan ya sa Kwankwaso ya zama ɗan takarar shugaban ƙasa na farko da ya kai ziyara ga sabon shugaban ƙasar.

Bayan wancan ganawar, Kwankwaso ya shaida wa manema labarai cewa sun tattauna batutuwa masu nasaba da siyasa da mulki, kuma yana iya yin aiki tare da Shugaba Tinubu, duk da cewa bai fayyace yadda hakan zai kasance ba.

A yanzu dai wasu 'yan adawa sun hadu a jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) dan wani sabon haɗin gwiwa da nufin kalubalantar jam’iyyar mai mulki ta APC a zaɓen shekarar 2027.

Kwankwaso, wanda ya yi gwamna a Kano a sau biyu (1999–2003 da 2011–2015), ya kasance ministan tsaro a lokacin Shugaba Olusegun Obasanjo, kuma ya tsaya takarar shugaban ƙasa a 2023 a ƙarƙashin jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) inda ya zo na huɗu, amma ya samu nasara mai girma a Jihar Kano.

Jam’iyyarsa ta NNPP ta lashe kujerar gwamna da kuma mafi yawan kujerun majalisar dokokin jihar, abin da ke nuna har yanzu yana da karfi da tasiri a siyasar jihar da ma Arewa baki ɗaya.

Duk da cewa NNPP ba ta cikin jam’iyyun da s**a shiga cikin ADC-led coalition, wasu fitattun ‘yan adawa suna ci gaba da jawo Kwankwaso domin hada kai da sauran jam’iyyu kafin zaben shugaban kasa na 2027.

Wata majiya daga fadar shugaban kasa ta bayyana cewa ba zai iya tabbatar da abin da s**a tattauna ba, saboda ganawar ta gudana ne a masaukin Shugaban Kasa,

GWAMNA RADDA NA CIKIN KOSHIN LAFIYA _Gwamnatin KatsinaDMCV NEWS HAUSAGwamnatin jihar Katsina ta yi ƙarin haske kan halin...
21/07/2025

GWAMNA RADDA NA CIKIN KOSHIN LAFIYA _Gwamnatin Katsina

DMCV NEWS HAUSA

Gwamnatin jihar Katsina ta yi ƙarin haske kan halin da gwamnan jihar, Malam Dikko Umar Radda ke ciki bayan bayan wani hatsarin mota da ya yi a kan hanyar Katsina zuwa Daura a jiya Lahadi.

Bayanin da gwamnatin ta fitar game da hatsarin ya ce lamarin ya faru ne a lokacin da gwamna Radda ke kan hanyarsa ta zuwa Daura, inda wata mota ƙirar Golf ta kauce hanyarta, kuma ta faɗa wa motar da gwamnan ke ciki.

Daraktan yaɗa labaran gwamnan jihar Katsina, Maiwada Dammallam ya tabbatar wa BBC cewa bayan abin ya faru, an kwashe su an kai su asibitin Daura inda aka ba su taimakon gaggawa na farko, daga nan kuma ya taho nan Asibitin kwararrun ta Katsina inda ƙwararrun likitoci s**a sake duba shi domin tabbatar da cewa babu wata matsala kamar yadda yake a tsari kiwon lafiya,''

A cewar Gamnatin jihar Katsina daga gwaje-gwajen da likitoci s**a yi, gwamna Dikko Umaru Radda yana cikin ƙoshin lafiya.

''Maiwada Dammallam ya Gwamnan na tare da chief of staff ɗin shi, Alhaji Abdulkadir Mamman Nasir da hakimin Kuraye da kuma Alhaji Shamsu Funtua. To dukkan su babu wani wanda ke da mummunan rauni, akwai dai wanda ke buƙatar dinki an yi, duk ma sun baro Daura, suna Katsina yanzu haka.

Daraktan yaɗa labaran gwamnan jihar Katsinan ya ce gwamnan ya ɗauki matakin rage yawan jerin gwanon motocin da ke yi masa rakiya zuwa Daura tun bayan rasuwar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, saboda yana yawan zuwa garin na Daura da kuma komawa Katsina daga lokaci zuwa lokaci saboda mutuwar.

Ya ce ''Kamar mota uku ne a cikin tafiyar saboda tun da aka yi rasuwar nan yana ta zirga-zirga zuwa Daura, to don ya rage tsadar tafiye-tafiyen shi ne ya ke rage motocin da ake amfani da su tunda ana rugawa ne a je, a dawo.''

DMCV ta gano cewa wannan bayani na gwamnatin ya musanta rade-raɗin da wasu ke yaɗawa a kafafen sada zumunta game da halin da gwamna Dikko Umar Radda ke ciki bayan hatsarin motar da ya ritsa da shi a ranLahadi.

KA JI UBA NAGARI:Mahaifin mu yayi mana Nasiha kan Cin Haram _Hadiza BuhariDMCV NEWS HAUSA Daya daga cikin 'ya'yan mariga...
16/07/2025

KA JI UBA NAGARI:
Mahaifin mu yayi mana Nasiha kan Cin Haram _Hadiza Buhari

DMCV NEWS HAUSA

Daya daga cikin 'ya'yan marigayi Shugaban kasa Muhammadu Buhari, Hadiza Buhari, ta ce mahaifinta ya koya mata da sauran ‘yan’uwanta su kasance masu kyawawan dabi’u, kada su dauki abin da ba nasu ba.

Hadiza Wacce aka fi sani da Nana, wacce ta yi magana da manema labarai a yau ranar Laraba a gidan mahaifinta da ke garin Daura, jihar Katsina, ta tuno da wani lamari da ya makale a zuciyarta kan koyarwar mahaifinta game da kyawawan halaye.

“Ba zan manta ba a shekarun baya muna yara, Baba ya umarce mu da mu je siyan littattafan motsa jiki, bayan mun yi haka sai aka samu saura Naira 15.

“Maimakon mu mayar wa Babanmu kudin, sai muka yanke shawarar kashe kudin, muka tsaya a wani shago muka yi amfani da kudin wajen siyan alawa.

“Da muka dawo gidan Baba ya tambaye mu sauran kuɗin, muka ce masa mun kashe.

Ya ce mana, 'Ya kamata ku dawo ku ba ni canjin, ya rage a gare ni in zaɓi in ba ku damar kashewa ko a'a.

“Sai ya ce mana kada mu ‘ci abin mutane, ko kuma mu dauki abin wasu’, kuma muna gode wa Allah da irin tarbiyyar da Baba ya yi mana.”

JAWABIN MINISTAN YADA LABARU GAME DA SHIRIN JANA'IZAR MARIGAYI BUHARIDMCV NEWS HAUSAGwamnatin Tarayya ta kaddamar da kwa...
14/07/2025

JAWABIN MINISTAN YADA LABARU GAME DA SHIRIN JANA'IZAR MARIGAYI BUHARI

DMCV NEWS HAUSA

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da kwamitin mutum 25 karkashin Sakataren Gwamnatin Tarayya Sanata Geoge Akume domin tabbatar da shirye shiryen Jana'izar wannan Dan kasa nagari.

Wasu daga cikin yan kwamitin sun hada daMinistocin Kudi, Tsare tsare, Tsaro, Yada Labaru, Ayyuka, Harkokin Cikin Gida da na Abuja da sauransu.

Shugaban kasa ya umurci kwamitin da ya gaggauta tafiya Jihar Katsina tare da zama a Daura har ranar Laraba da za ayi Addu'ar Uku.

A daidai lokacin da muke jimamin rashin wannan Dan kishin kasa, muna fata al'umma za su ci gaba da yi mashi Addu'ar fatan alkhairi.

Duba da cewa gobe Talata za ayi Jana'izar an dage taron Majalissar zartaswa na musamman da a da akai niyyar yi a goben zuwa ranar Juma'a. Yayinda shugaba Bola Tinubu ya umurci da a fara zaman Makoki na kasa na tsawon sati guda, inda tuni aka sassafto da tutoci Dan nuna girmamawa ga marigayi Buhari.

Kamar yadda aka ji Kuma tawaga ta musamman karkashin Jagorancin Mataimakin Shugaban kasa sun isa Birnin London dan tahow a da gawar marigayin, yayin da shi Kuma shugaban kasa da kansa zai tarbi gawar a birnin Katsina. An Kuma ayyana gobe Talata a matsayin ranar hutu a kasa.

Bayan isowar gawa, za ayi mashi Faretin Girmamawa da ban kwana kafin a.wuce Daura inda za ayi mashi Sallah da rufe shi a.Gidanshi.

Danjinkau

12/07/2025

GYARAN KUNDIN TSARIN MULKI: GWAMNATIN KATSINA TA TURA WAKILANTA
DMCV NEWS HAUSA

Gwamnan Jihar Katsina Mal.Dikko Umaru Radda ya amince da kafa wani babban kwamiti domin halartar taron Shiyya na yin dubi akan sake fasalin Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na shekarar 1999.

Taron da zai gudana a Kano, an gudanar da shi ne a Shiyyoyi 6 da ake da su fadin Kasar nan.

Majalissar Dattawan Najeriya ce ta shirya shi, kuma za'a yi taron na Shiyyar Arewa Maso Yamma a Jihar Kano karkashin Jagorancin Mataimakin Shugaban Majalissar Dattawa Sanata Barau Jibrin.

Gwamnan na Katsina Malama Dikko Radda ya kafa kwamiti ne mai dauke da mutane 20 da s**a hada da dattawa da kwararru a fannin shari'a da Malaman Manyan makarantu da Kungiyoyin al'umma da wakilan Gwamnati Dan wakiltar jihar ta Katsina.

Kwamitin wanda ke karkashin jagorancin Sanata Ibrahim Ida (Wazirin Katsina) ma da mambobin kamar haka:

Kwamishinan Shari'a da Kwamishinan Tsaro da Mai Ba Gwamna Shawara akan Kananan Hukumomi da Mai Ba Gwamna Shawara akan gyara aikin Gwamnati da wakilin Majalissar Dokoki ta Jihar Katsina da na Babbar Kotun Katsina.

Sauran sun hada da Mai Shairi'a Sadiq Abdullahi Mahuta(Galadiman Katsina) da Galadiman Daura da Farfesa Sadiq Radda da Farfesa Binta Dalhat Dan Ali da Dr.Abubakar Sadiq da Muhammad Lawal Aliyu mni da AD Umar da Suleiman Ibrahim Safana da dai sauran su.

Gwamna Radda ya bukaci Mambobin Kwamitin akan su yi aiki tukuru wurin sauke nauyinda aka dora masu ta hanyar gabatar da bukatun al'ummar Jihar Katsina a yayin zaman su.

Address

Kaduna

Telephone

+2348036411514

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DMCV News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share