DMCV News Hausa

DMCV News Hausa Sss

04/05/2025
MANAJAN KASUWANCI TA KAMFANIN NNPCL MARYAM IDRIS BAGIWA KATSINA.ALLAH YA TAYA RIKO
04/05/2025

MANAJAN KASUWANCI TA KAMFANIN NNPCL MARYAM IDRIS BAGIWA KATSINA.

ALLAH YA TAYA RIKO

KO AKPABIO HALARTACCEN SANATA NE?DMCV DAILY NEWSA dai dai lokacin da Kotu Ta Yanke Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Tsawon S...
01/05/2025

KO AKPABIO HALARTACCEN SANATA NE?

DMCV DAILY NEWS

A dai dai lokacin da Kotu Ta Yanke Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Tsawon Shekaru Uku Ga Baturen Zaben Da Ya Yi Magudi Har Ta Kai Ga Akpabio Ya Zama Sanata, to ko mu Iya cewa shugaban majalisar Dattawan Halartacce ne?

Meye Ra'ayinku?

30/04/2025

KATSINAWA MU FITO MU TARBI SHUGABAN KASA _ Gwamnati

DMCV NEWS
Gwamnatin Jihar Katsina Ta Buƙaci Al'umma Su Fito Yi Ma Shugaba Tinubu Kyakkyawar Tarba Idan Ya Zo Jihar Ranar Juma'a

Gwamnatin Jihar Katsina ta yi kira ga al'ummar jihar da su fito kwansu da kwarkwatansu domin yi wa Mai Girma Shugaban Ƙasa, Asiwaju Bola Ahmad Tinubu, kyakkyawar tarba a ziyarar aiki da zai kai jihar a ranar Juma'a, 2 ga Mayu, 2025.

Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar, Dr. Bala Salisu Zango, ya bayyana wannan kira ne a wani taron manema labarai da aka gudanar a gidan gwamnatin jihar a ranar Laraba. Ya bayyana cewa ziyarar Shugaban Ƙasa ta kwanaki biyu za ta ba al'ummar jihar damar nuna godiya ga gwamnatin tarayya bisa irin tallafin da take ba wa jihar.

Dr. Zango ya bayyana cewa Shugaban Ƙasa zai ƙaddamar da wasu muhimman ayyukan ci gaba da gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dikko Umar Radda ta aiwatar a cikin shekaru biyu da ta yi tana mulki. Waɗannan ayyuka sun haɗa da babbar hanyar da ta ratsa wajen kauce wa cunkoso (Bypass), wadda ta tashi daga hanyar Dutsin-ma ta haɗe da hanyar Kano, ta zagaya ta ratsa hanyar Daura ta haɗe da hanyar zuwa 'Yandaki da ke kan hanyar zuwa Kaita.

Haka kuma, Shugaban Ƙasa zai ƙaddamar da cibiyar haɗa kayan aikin gona ta zamani (Agric Mechanization Centre), wadda za ta horar da matasan jihar kan yadda ake haɗa kayan aikin gona na zamani.

Kwamishinan ya jaddada cewa waɗannan ayyuka za su inganta rayuwar al'ummar jihar Katsina ta hanyoyi daban-daban, kamar inganta harkokin kasuwanci, samar da ayyukan yi, da kuma haɓaka noma. Ya kuma bayyana cewa ziyarar za ta ba gwamnatin jihar damar tattaunawa da Shugaban Ƙasa kan batutuwan da s**a shafi ci gaban jihar, musamman batun tsaro.

Dr. Zango ya yi kira ga al'ummar jihar da su fito da yawa domin nuna ƙauna da goyon baya ga Shugaban Ƙasa, tare da nuna irin farin cikin da suke da shi na ziyarar da zai kawo jihar.

HAIHUWA MAI DADI:ALLAH YA YI ALBARKAWannan ita ce Dr. Sayyada Madinatu Sheikh Dahiru Usman Bauchi Sirikar Maulana Sheikh...
30/04/2025

HAIHUWA MAI DADI:
ALLAH YA YI ALBARKA

Wannan ita ce Dr. Sayyada Madinatu Sheikh Dahiru Usman Bauchi Sirikar Maulana Sheikh Shareef Ibrahim Saleh Alhusaini Ce Kuma Ɗiya Ga Maulana Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Sayyada Madinatu Itace Mace Ta Farko Da Take Ɗauke Da PHD A Fannin Ilimin Fiqhu A Arewacin Nijeriya Tayi Karatunta A Babban Jami'an Musulunci Na Kasar Morroco kuma Mahaddaciyan Al Qur'ani Ce Ta Kware A Kowane Fanni Na Ilimin Addini.

Ko wane Fata za ku yi mata?

Allah Ya ƙara Mata Lafiya...

Maganar Auren Mawaki Rara da Abokiyar aikinshi Aisha Humaira na ta kara tabbata, ko wane Fata da Addu'a za ku yi masu?
25/04/2025

Maganar Auren Mawaki Rara da Abokiyar aikinshi Aisha Humaira na ta kara tabbata, ko wane Fata da Addu'a za ku yi masu?

SHUGABAN BANKIN RAYA AFIRKA ADB YA KARA GODIYA Shugaban Bankin Bunƙasa Kasashen Afrika, Mista Akinwumi Adeshina Ya Yaba ...
18/04/2025

SHUGABAN BANKIN RAYA AFIRKA ADB YA KARA GODIYA

Shugaban Bankin Bunƙasa Kasashen Afrika, Mista Akinwumi Adeshina Ya Yaba ma Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Domin Bayyana Jin Dadinsa, Bisa Ga Goyan Bayan Da Ya Nuna Masa A Lokacin Da Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan Ya Ba Da Sunan Sa, Kan Matsayin Shugaban Bankin, A Lokacin Da Ya Ziyarce Shi A Gidansa Dake Kaduna Kwanan Baya

Address

Kaduna

Telephone

+2348036411514

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DMCV News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share