22/07/2025                                                                            
                                    
                                    
                                                                        
                                        JAGORAN NNPC YA GANA DA SHUGABA TINUBU
DMCV NEWS HAUSA
Rahotanni sun nu na cewa jagoran jam'iyyar NNPP Kuma tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya gana da Shugaba Bola Tinubu a ranar Litinin a fadar shugaban kasa.
Wannan ganawar da aka gudanar ta  sirri ta biyo bayan halartar Kwankwaso taron Nigeria Forest Economy Summit 2025 da aka gudanar a dakin taro na fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Wannan shi ne karo na biyu da aka samu yin ganawa tsakanin Kwankwaso da Tinubu a cikin sama da shekaru biyu da s**a gabata.
In za a iya tunawa a ranar 9 ga Yuni, 2023, kwana kadan bayan rantsar da Tinubu a matsayin shugaban ƙasa. Wannan ya sa Kwankwaso ya zama ɗan takarar shugaban ƙasa na farko da ya kai ziyara ga sabon shugaban ƙasar.
Bayan wancan ganawar, Kwankwaso ya shaida wa manema labarai cewa sun tattauna batutuwa masu nasaba da siyasa da mulki, kuma yana iya yin aiki tare da Shugaba Tinubu, duk da cewa bai fayyace yadda hakan zai kasance ba.
A yanzu dai wasu 'yan adawa sun hadu a jam’iyyar  African Democratic Congress (ADC) dan wani sabon haɗin gwiwa da nufin kalubalantar jam’iyyar mai mulki ta APC a zaɓen shekarar 2027.
Kwankwaso, wanda ya yi gwamna a Kano a sau biyu (1999–2003 da 2011–2015), ya kasance ministan tsaro a lokacin Shugaba Olusegun Obasanjo, kuma ya tsaya takarar shugaban ƙasa a 2023 a ƙarƙashin jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) inda ya zo na huɗu, amma ya samu nasara mai girma a Jihar Kano.
Jam’iyyarsa ta NNPP ta lashe kujerar gwamna da kuma mafi yawan kujerun majalisar dokokin jihar, abin da ke nuna har yanzu yana da karfi da tasiri a siyasar jihar da ma Arewa baki ɗaya.
Duk da cewa NNPP ba ta cikin jam’iyyun da s**a shiga cikin ADC-led coalition, wasu fitattun ‘yan adawa suna ci gaba da jawo Kwankwaso domin hada kai da sauran jam’iyyu kafin zaben shugaban kasa na 2027.
Wata majiya daga fadar shugaban kasa ta  bayyana cewa ba zai iya tabbatar da abin da s**a tattauna ba, saboda ganawar ta gudana ne a masaukin Shugaban Kasa,