DMCV News Hausa

DMCV News Hausa Sss

AN YI KIRA GA MATASADMCV News HausaAn yi ‎Kira ga yan siyasar Jihar Katsina musamman Matasa na jihar da ma Kasa baki day...
01/06/2026

AN YI KIRA GA MATASA

DMCV News Hausa

An yi ‎Kira ga yan siyasar Jihar Katsina musamman Matasa na jihar da ma Kasa baki daya da su koyi yin Siyasa Mai tsabta ba siyasar kiyayya da gaba ba.

Malam Nasir Abdullahi, Sakataran Jami:ar WIGWE UNIVERSITY dake garin Port Harcourt, ya yi kiran a zantawar Shi da Babban Editan DMCV News Hausa.

Malam Nasir Na Allah ‎Ya kuma ƙarfafi matasa da su fito su shiga harkar siyasa da jajircewa, saboda yanzu “lokacin matasa” ne – Youths O’clock.

‎Matashin kuma Dan Gwagarmaya ya ƙara da cewa mutane su riƙe katin zabensu yadda ya kamata, domin lokaci ya yi da za a “warke zaren da aka ɗaure” a zaben 2027.

Ya Kara da cewa Matasa su daina bari ana amfani da su wajen Bangar Siyasa inda daga Karshe ake barin su da danasani wani lokacin ma hada raunuka koma asarar rayukansu.

Ya Kuma yi Kira ga shugabanin al'umma da su taimaka wajen Kara fadakar da Al'ummar, yana mai cewa nauyi ne da Allah SWT ya dora masu.

ANA ZARGIN WASU MAGIDANTA DA MUSAYAR MATAN AUREN SUDMCV News HausaWasu rahotanni sun bayyana cewa jami’an tsaro sun cafk...
13/05/2026

ANA ZARGIN WASU MAGIDANTA DA MUSAYAR MATAN AUREN SU

DMCV News Hausa

Wasu rahotanni sun bayyana cewa jami’an tsaro sun cafke wasu maza bakwai a Jihar Bauchi bisa zargin gudanar da wani abu mai tayar da hankali, inda ake zargin suna musayar matansu a tsakaninsu domin aikata lalata.

Bincike ya nuna cewa mutanen sun yi ikirarin cewa sun fara aikata hakan ne bayan wani daga cikinsu ya ce ya samu umarni daga wani “Annabi” a mafarki. Lamarin ya jawo cece-kuce da tofin Allah tsine daga al’umma, inda mutane da dama s**a bayyana takaicinsu tare da kira ga hukumomi su zurfafa bincike kan abin da ya faru.

Wasu malamai sun yi gargadin cewa bai kamata mutane su rika bin duk wani mafarki ko ikirari ba tare da tabbatarwa da koyarwar addini ba, domin hakan kan iya jefa mutum cikin babban kuskure da barna ga al’umma.

Ko me za ku ce Kanannan Al'amari?

SHUGABANNIN ADC BANGAREN USMAN WAMBA SUN KARBI RANTSUWAR K**A AIKIDMCV News HausaAn Rantsar da Sabbin Shugabannin Jam'iy...
13/05/2026

SHUGABANNIN ADC BANGAREN USMAN WAMBA SUN KARBI RANTSUWAR K**A AIKI

DMCV News Hausa

An Rantsar da Sabbin Shugabannin Jam'iyyar ADC na Jihar Katsina

Tsohon shugaban Jamiyyyar Alhaji Musa Usman Wamba ne ya sake zama shugaban jam’iyyar ADC karo na biyu.

An gudanar da bikin rantsuwar a harabar hedkwatar jam'iyyar da ke Katsina, tare da sauran sabbin shugabannin jam’iyyar.

Taron da aka gudanar ranar Talata 12 ga watan Mayu shekarar 2026, ya samu halartar mambobi da magoya bayan jam’iyyar daga sassa daban-daban na jihar. Inda s**a shaida rantsuwar.

Sabbin shugabannin da aka rantsar za su jagoranci harkokin jam’iyyar a matakin jiha tare da ɗora jam’iyyar a kan turbar ƙarfafa siyasa, haɗin kai da kuma shirye-shiryen tunkarar zaɓuɓɓuka masu zuwa.

Sabon shugaban Jamiyyyar Alhaji Musa Usman Wamba ya bayyana godiyarsa ga shugabanni da mambobin jam’iyyar bisa ci gaba da nuna masa goyon baya da amincewa da jagorancinsa karo na biyu.

Ya ce wannan damar da aka sake ba shi za ta ƙara masa ƙwarin guiwa wajen yi wa jam’iyyar aiki da gaskiya da riƙon amana.

Wamba ya kuma yi kira ga dukkan shugabanni da mambobin ADC a faɗin jihar Katsina da su haɗa kai domin ganin jam’iyyar ta samu ci gaba da kuma ƙara samun karɓuwa a tsakanin al’umma.

Ya jaddada cewa sabuwar shugabancin za ta mayar da hankali wajen bunƙasa jam’iyyar daga matakin ƙasa zuwa mazaɓu, tare da bai wa Matasa da Mata damar taka muhimmiyar rawa a harkokin siyasa.

Tsohon sakataren Jamiyyyar Junaidu lawal da wasu daga cikin mahalarta taron sun bayyana farin cikinsu da yadda aka gudanar da tsarin cikin lumana da haɗin kai, suna masu bayyana fatan cewa sabon shugabancin zai kawo cigaba da sabon salo na tafiyar da jam’iyyar a jihar Katsina.

Sai dai DMCV ta yi ƙoƙarin jin dayan bangaren na Jamiyyyar ta ADC Wanda basu halarci taron ba inda s**a ce mu basu lokaci za su tuntubemu.

Jamiyyyar da ake gani ta taso da Farin jini na fama da rigingimun cikin gida da ke neman su rage mata farin jinin nata.

Malumfashi

SHIMA MALAM BAWA NA BUKATAR TAIMAKON KUDMCV News HausaSUBHANALLAH.Malam Bawa Umar Ubangiji Allah Yabaka Lafiya Yasa Zakk...
09/05/2026

SHIMA MALAM BAWA NA BUKATAR TAIMAKON KU

DMCV News Hausa

SUBHANALLAH.

Malam Bawa Umar Ubangiji Allah Yabaka Lafiya Yasa Zakkar Jikice Malam Yana Buqatar Addu'a Taku Malam Yana Kwance Sosai Baida Lafiya Sakamakon Tsananin Rashin Lafiya Dake Damunsa Tsawon Lakoci .

Duk Wanda Yasan Malam Ya Sanshi Da Kokarin Hidimar Addini Da Kuma Kokarin Ganin Mutane Sun Samu Ilimi Ingan tacce , Malam Yanada Himma Da Kuma Kokarin Ganin Ya Hada Kan Al'umma Su Zama Tsuntisya Madaurinki Daya

Sakamakon Irin Kokarin Malam Ya sanyani Yin Wannan Rubutu Ba Wani Ya sanyani ba Al'umma Muna Buqatar Ku Taimaka Ma Malam Da Addu'a Kan Larurar Dake Damunsa Sannan Kutaimaka Masa Da Duk Abinda Ya Samu Domin Malam Baida Halin Yima Kanshi Magani Dan Yanzu .

Al'umma Ina Kara Neman Taimakon Ku Kan Rashin Lafiya Ta Malam Duk Wanda Yataimaki Wani Allah Zai Taimakeshi Albarkar Annabi Muhammad S A W Ataimaki Malam

domin Qarin Bayani A tuntubeni ta Wannan Numbers tawa.

08144112364
08162330606

Allah Yabada Ikon Taimakawa Amman Tabbas Malam Yana Jin Jiki Wanda Jiya A Masallachi An Dan Nema Masa Taimako Dan Allah Al'umma mutaimaki Malam

Malam Allah Yabaka Lafiya Yasa Zakkar Jikice Tareda Sauran Marasa Lafiya Gida Da Asibiti Amin ya Allah
U. Nabula

BAYIN ALLAH A TAIMAKADMCV News Hausaslm akwai wata mata baiwar  mai suna salamatu Hayin majema, malumfashi  da take ciki...
09/05/2026

BAYIN ALLAH A TAIMAKA

DMCV News Hausa

slm akwai wata mata baiwar mai suna salamatu Hayin majema, malumfashi da take cikin wani mawuyacin Hali na kuncin rayuwa, yanzu haka yayan ta ukku ba su da lfy, gidan su ba abinci , ba bu kudin magani, shi kan shi gidan da suke zaune Yana bukatar gyara, Dan Allah Wanda ke da halin taimakon ta ya taimaka Dan a fitar da iyalan wannan mata daga cikin halin da suke ciki. 08088531028,

Malumfashi live post

BAYAN TA JAGORANCI GANGAMIN DAGA DAN-KAMFAI: GWAMNATI TA BAIWA TEEMA MUKAMIDMCV News HausaShugaban karamar hukumar Nassa...
30/04/2026

BAYAN TA JAGORANCI GANGAMIN DAGA DAN-KAMFAI: GWAMNATI TA BAIWA TEEMA MUKAMI

DMCV News Hausa

Shugaban karamar hukumar Nassarawa ya baiwa Fatima Naseer Teemahcool mukamin jami'a mai kula da harkokin mata a karamar hukumar.

Wannan na zuwa ne bayan Teemahcool ta jagoranci wani gangamin daga Dan-kamfai a Jihar Kano

Ko dama hakan na nufin mukami ko wani sani take nema?

GWAMNA RADDA YA JINJINA MA ENGR. MUNTARI SAGIRDMCV News HausaGwamna Radda Ya Ƙaddamar da Muhimman Ayyukan Raya Ƙasa Wand...
21/04/2026

GWAMNA RADDA YA JINJINA MA ENGR. MUNTARI SAGIR

DMCV News Hausa

Gwamna Radda Ya Ƙaddamar da Muhimman Ayyukan Raya Ƙasa Wanda Injiniya Muntari Sagir Ya Samar A Malumfashi

A ranar Litinin 20 ga watan Afrilu 2026, Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda, ya ƙaddamar da jerin muhimman ayyukan raya ƙasa da Injiniya Muntari Sagir ya samar a garin Malumfashi, a wani mataki na inganta walwala da jin daɗin al’umma.

Ayyukan da aka ƙaddamar sun haɗa da gina ɗakin tiyata tare da samar da kayan aiki na zamani a ƙaramar asibitin garin, domin ƙara inganta harkokin lafiya. Haka kuma an samar da tsanyar ruwa tare da zagaye maƙabarta, wanda zai taimaka wajen tsafta da kare muhalli.

Bugu da ƙari, an gina masallacin salloli biyar na rana domin sauƙaƙa ibada ga al’umma, tare da samar da mota ga makarantar ‘yan mata domin tallafa wa harkokin ilimi.

A fannin horar da ma’aikatan lafiya, an gina dakunan karatu a makarantar koyon aikin ungozoma (midwifery) ta garin, yayin da kuma aka gina ƙaramar asibiti mai ɗauke da gadaje 10 a garin Danjanku domin ƙara kusantar da ayyukan lafiya ga jama’a.

Da yake gudanar da jawabi dangane da ayyukan, Gwamna Radda ya jinjinawa Injiniya Muntari Sagir bisa wannan kokari da yayi a fannoni da dama domin inganta rayuwar al'umma, ya kuma bayyana samun irin shi a cikin al'umma abun alfahari ne domin yana taimakawa kwarai da gaske yana kuma rage ma gwamnati wata ɗawainiyar sabo da abun da ya kamata ace gwamnatin nayi ne.

Shima a nashi Jawabin Galadiman Katsina Hakimin Malumfashi Maisharia Sadiq Abdullahi Mahuta Murabus yace ayyukan wannan bawan Allah ba ga Ilimi da lafiya Kadai ya tsaya ba, har da Masarautar Katsina inda ya bada gudummuwa wajen Gina fadar Galadanchi a garin Malumfashi.

Jama'a da dama sun yi jawabi da yaba ma Muntari Sagir kan wannan kokari na Shi. Kuma taron ya samu halarcin jami'an Gwamnati da sauransu.

DMCV Media na godiya ga D G Media, Sakataren yada Labarun Gwamna Ibrahim Kaola da ma M S Ingawa S.A Media.
Malumfashi

KARAMAR HUKUMAR MALUMFASHI TA GYARA WASU MOTOCIDMCV News HausaKaramar Hukumar Malumfashi a Jihar Katsina ta gyara wasu m...
18/04/2026

KARAMAR HUKUMAR MALUMFASHI TA GYARA WASU MOTOCI

DMCV News Hausa

Karamar Hukumar Malumfashi a Jihar Katsina ta gyara wasu motocin bas na ɗalibai guda biyu da motar kashe gobara duba da irin aikin su ga Al'umma.

Motocin bas ɗin da aka samar tun a shekarar 2007 a lokacin Shugaban Karamar Hukumar Hon. Abdulaziz Lawal Danyari, domin taimakawa wajen jigilar ɗalibai mata daga yankuna masu nisa, yanzu an gyara su ƙarƙashin jagorancin Shugaban Karamar Hukuma na yanzu, Hon. Mukhtar Abdullahi (M.A City), domin ƙara ƙarfafa ilimin ‘ya’ya mata.

kamar yadda Kansilan dake kula da Ilimi da jin dadin Al'umma (ESD), Nura Bala ya sanar, ya ce wannan na daga cikin kokarin shugaban karamar Hukumar na kyautata ma AL'UMMAR Shi.

Nura Bala Kuma yayi fatan za a ci gaba da ba Hon. Muntari City goyon bayan da ya kamata dan ci gaba da Yi ma al'umnar Karamar Hukumar Malumfashi Hidinar
Danjinkau

GWAMNATIN LAGOS TA SAYO SABBIN JIRAGEN KASA 45DMCV News HausaGwamna Babajide Sanwo Olu  ya jagoranci bikin karɓar sabbin...
17/04/2026

GWAMNATIN LAGOS TA SAYO SABBIN JIRAGEN KASA 45

DMCV News Hausa

Gwamna Babajide Sanwo Olu ya jagoranci bikin karɓar sabbin jiragen guda 24 daga wakilan kamfanin da s**a ƙera shi.

Jiragen da aka kera a kasar China za su rika zirga zirga ne a cikin garin Lagos dan saukaka cinkoson ababen hawa.

irin wannan kokari a ke so a GA gwamnatocin Arewa su ma sun Fara.

Ko Kuna ganin hakan na yiwuwa a Arewan?

09/04/2026

Address

Kaduna

Telephone

+2348036411514

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DMCV News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share