01/06/2026
AN YI KIRA GA MATASA
DMCV News Hausa
An yi Kira ga yan siyasar Jihar Katsina musamman Matasa na jihar da ma Kasa baki daya da su koyi yin Siyasa Mai tsabta ba siyasar kiyayya da gaba ba.
Malam Nasir Abdullahi, Sakataran Jami:ar WIGWE UNIVERSITY dake garin Port Harcourt, ya yi kiran a zantawar Shi da Babban Editan DMCV News Hausa.
Malam Nasir Na Allah Ya kuma ƙarfafi matasa da su fito su shiga harkar siyasa da jajircewa, saboda yanzu “lokacin matasa” ne – Youths O’clock.
Matashin kuma Dan Gwagarmaya ya ƙara da cewa mutane su riƙe katin zabensu yadda ya kamata, domin lokaci ya yi da za a “warke zaren da aka ɗaure” a zaben 2027.
Ya Kara da cewa Matasa su daina bari ana amfani da su wajen Bangar Siyasa inda daga Karshe ake barin su da danasani wani lokacin ma hada raunuka koma asarar rayukansu.
Ya Kuma yi Kira ga shugabanin al'umma da su taimaka wajen Kara fadakar da Al'ummar, yana mai cewa nauyi ne da Allah SWT ya dora masu.