02/08/2026
A YANZU DAI A JIHAR KATSINA BA DANTAKARA K**AR DIKKO _Wata Sabuwar Kungiya
DMCV News Hausa
An bayyana cewa a halin da ake ciki dai babu tsayayyen Dan takarar Gwamna a Jihar Katsina kamar Gwamna Malam Dikko Umar Radda.
Shugaban wata Sabuwar Kungiya ta siyasa a Karamar Hukumar Malumfashi Mai suna "Mafita Daya Ce Dikkon Dai" Aliyu S. Mohd shine ya Sanar da haka yayin da ziyarci sabon office din DMCV MEDIA a Malumfashi.
Aliyu Mohd ya ce tabbas akwai Yan takara uku aJam'iyyu uku da s**a hada da APC, ADC da PDP Amma Jamiyyyun biyu na ADC da PDP sun kasa warware rigingimun su na cikin gida.
Ya Kara da cewa a daidai lokacin da Jamiyyyar APC ta shirya dan fara campaign su sauran jam'iyyun sun kasa tabbatar da sahihanci mutum guda a matsayin Dan takara.
Shugaban Kungiyar ta MAFITA DAYA CE, DIKKON NE yace a lokacin da har yanzu wasu jagororin ADC s**a ki yadda su Mara ma Babban Kaita baya, Sai ga Shi a PDP ma ana maganar Bangaren Wike da naTanimu Turaki Kuma duk suna da Yan takara.
Ya shawarci al'ummar Malumfashi da ma jihar Katsina da su bude idonsu su baiwa Dikko dama ya idasa shekarun Shi 4 kamar yadda marigay Umaru Musa, Shema da Masari su ka yi.