Chairman Zage-Zagi a Yau.

Chairman Zage-Zagi a Yau. Zazzau Media Writers Association Zamwa.

Zamu Kawo Karshen Cin Mutuncin Juna, a Kafofin Sadarwan Zamani(Social Media). Ga Al'ummar kasata.. Daga. Shafin Mallam Y...
28/06/2022

Zamu Kawo Karshen Cin Mutuncin Juna, a Kafofin Sadarwan Zamani(Social Media). Ga Al'ummar kasata..

Daga. Shafin Mallam Yusuf Yahaya Bamalli.

Siyasa Ra'ayi. Siyasa Mutuncinka. Siyasa, akidarka. Siyasa. Mafitanka ce. Siyasa addininka ne.

Amma cin mutunci, a siyasa jahilcine Cin mutunci a Siyasa rashin Ilimi ne, Dama ita Haka ake Gudanar da soyayya ga dan'siyasa. Ka fifita Mutuncinshi akan mutuncinka, Takan Siyasa, ka Kare martaban wani fiye da Martaban kanka Dana iyalinka, ko iyayeka. Wannan kuskure ne.

Siyasa ana yinta ne Domin Samar da yan'ci, tare da Samoma Al'umma saukin rayuwa, bakamar yadda ake gudanar mulkin Soja ba. Amma abin takaici, da ban tausayi, Al'ummarmu sun dauki Wannan Haka ta siyasa fagen cin mutunci, da zubarma da Juna mutunci, sabo da wani, ko banbancin Jam'iyya, ko manufa. Masu aukata Wannan aika-aika Musamman Matasanmu, kusani Kuna bata gobenku ne. Domin kaima Mahaifin wasu ne, Kuma kana da Iyaye, da Malamai da s**a karantar dakai Tarbiyya. Wani irin riba zaka samu akan abin Duniya, kana zubar da mutuncin gidanku, da mutuncinka Domin Kare Mutuncin wani.

Amma Kullun ana samun wasu Mutane marasa daraja da mutunci. Wanda Suke aibata fiyayyen halitta. Annabin muhammad (s.a.w) wani irin mataki ka dauka, Bayan shine akayi Duniya da abin dake ciki damu, Domin shi. ( S.a.w). Amma sabo da asaran lokaci. Kaje kana Bata ranka, Akan aikin wani. Wallahi tallahi. Muji tsoron Allah. A Kowani irin Lokaci, Kowani irin Hali. Bawa zai iya Amsa Kiran mahaliccinsa.

Kafar Sadarwa Zamani, ( social media) Kar ka dauketa hangar da Zara rabaka da mutuncika, da mutuncin iyayenka. Ayi siyasa na ilimi da wajewa. Kowa ya tsaya a Matsayinsa. Mu zauna lafiya da juna.

Allah ya zaunar da mu lafiya.

FROM ZAZZAU EMIRATE.Emir of Zazzau and Chairman Kaduna State Council of Traditional Rulers, His Highness Malam Ahmed Nuh...
28/06/2022

FROM ZAZZAU EMIRATE.

Emir of Zazzau and Chairman Kaduna State Council of Traditional Rulers, His Highness Malam Ahmed Nuhu Bamalli in Kaduna this afternoon attends the routine Meeting at Sir. Kashim Ibrahim Council Chamber, Kaduna Government House with all stakeholders in attendance.

Aliyu Kwarbai
Media and Publicity Office, Zazzau Emirate

DAGA MASARAUTAN ZAZZAU:-A safiyan yau Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a Fadansa ya aurar da uku daga ...
25/06/2022

DAGA MASARAUTAN ZAZZAU:-

A safiyan yau Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a Fadansa ya aurar da uku daga cikin 'Ya'yansa;

I. Malama Murjanatu Muhammadu Bukhari wanda aka aurar da ita ga Malam Musa H. Malami bayan da ya biya Naira Dubu Dari a matsayin Sadakinta sai,

Il. Malama Ninzihatu Sabo Mohammed Tukur wanda aka aurar da ita ga Malam Hussaini Yusuf wanda ya biya Naira Dubu Dari a matsayin Sadakinta sai kuma,

Ill. Malama Halimatu Ahmad Bamalli wanda aka aurar da ita ga Malam Dalhatu Ibrahim wanda shima ya biya Naira Dubu Dari a matsayin Sadakinta.

Na'ibin Zazzau Malam Kawu Abubakar Lamido ya jagoranci sauran Malamai wajen gabatar da addu'o'in neman albarkan Allah ga ma'auratan.

** Bayan Kamalla daurin aurarrakin da ya gudana a Fadan Zazzau a yau Ma'aikata daga Ma'aikatan Buga Muhimman Takardu da Kudade na Nijeriya wadanda s**a halarci daurin auren daya daga cikin abokin aikinsu Malam Hussaini Yusuf a Fadan na Zazzau s**a gabatar gaisuwan girmamawa ga Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a Fadansa.

*** Garkuwan Ayyukan Zazzau ya jagoranci Kurata 'Yan Asalin Masarautan Zazzau wadanda aka yaye a Makarantan Horar da Kurata na Zariya wajen gabatar da ziyarar girmamawa gami da godiya ga Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a Fadansa.

**** Da yammacin yau Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya hallarci bikin yayen Dalibai Saba'in da Biyar (75) wanda daga cikin su Dalibai Ashirin Da Biyar (25) s**a kasance sun Haddace Al'qurani a Makaranta tunawa da Atika Abdullahi wanda Marigayi Alhaji Usman Abdullahi Adada ya Hassasa a Anguwan Kaura cikin Birnin Zariya.

Aliyu Kwarbai.
Media & Publicity Zazzau Emirate.

DAGA MASARAUTAN ZAZZAU:-Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya bi sahun dubban Al'umman Muslimi wajen gab...
24/06/2022

DAGA MASARAUTAN ZAZZAU:-

Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya bi sahun dubban Al'umman Muslimi wajen gabatar da Sallan Jumma'a a Babban Masallacin Jumma'a wanda ke Kofan Fadan Zazzau.
Babban Limamin Kasar Zazzau Liman Dalhatu Kasim Imam shi ya jagoranci Sallan Mai Raka'a Biyu bayan gabatar da Hudduban Jumma'a.
Har ila yau, Mai Martaba Sarkin Zazzau ya karbi gaisuwan Jumma'a daga 'Yan Majalisan Masarautan Zazzau da Hakimai da Dagatai da Malamai da dimbin jama'a daga ciki da wajen Zariya.

Aliyu Kwarbai
Media & Publicity Zazzau Emirate.

SAURAN MAZAN JIYA.Farfesa Muhammad Shafi'u Abdullahi. Wakilin Makaranta Zazzau na Biyu. Shugaban Hukuman NBAIS, Bawan Al...
24/06/2022

SAURAN MAZAN JIYA.

Farfesa Muhammad Shafi'u Abdullahi. Wakilin Makaranta Zazzau na Biyu. Shugaban Hukuman NBAIS, Bawan Allah Mutumin kirki, Mai Son Cigaban Al'umma. Allah Ya Kara Lafiya Da Nisan Kwana Da Jikiri Mai Amfani.

DAGA MASARAUTAN ZAZZAU:-A safiyan yau mai rikon Darktan Koyar Da Ayyuka Na Kasa (NDE) na Jihar Kaduna Misis Victoria W. ...
23/06/2022

DAGA MASARAUTAN ZAZZAU:-

A safiyan yau mai rikon Darktan Koyar Da Ayyuka Na Kasa (NDE) na Jihar Kaduna Misis Victoria W. Dada a madadin Babban Darkatan Hukumar Na Kasa Malam Abubakar N. Dikko ta jagoranci Jami'e daga Hukumar wajen gabatar da ziyarar girmamawa ga Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a Fadansa.
Misis Dada ta gabatar da bayanai bisa kan ayyukan Hukumar ga Mai Martaba Sarkin Zazzau a lokacin gabatar da wannan ziyara.

** Malam Ibrahim Saleh Hassan Mai Bayar da Shawara ga Kungiyan Daidaita Zamantakewa Na Al'umma wanda take a Asokoro, Abuja ya jagoranci wakilai daga kungiyan wajen gabatar da ziyarar girmamawa ga Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a Fadansa.
Wakilan kungiyan sun gabatar da bayanai bisa kan ayyukan da suke gudanarwa ga Mai Martaba Sarkin Zazzau a lokacin gabatar da wannan ziyara.

*** Kantoman Gudanar da Mulkin Yankin Zariya Hajiya Balaraba Aliyu Inuwa ta jagoranci sauran Jami'e daga ofis dinta wajen gabatar da ziyarar aiki ga Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a Fadansa.
A lokacin gabatar da wannan ziyarar Hajiya Balaraba ta gabatar da bayanai bisa kan ayyukan da suke gudanarwa ga Mai Martaba Sarkin Zazzau da 'yan Majalisan Masarautan na Zazzau a lokacin wannan ziyara.

**** Malam Abdullahi Ibrahim Sakataren Daliban shekarar 2004 na fannin ISS/SOS a Kwallejin Horar da Malamai Na Gwamnatin Tarayya (FCE) dake Zariya ya jagoranci sauran membobin Ajin wajen gabatar da ziyarar girmamawa ga Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a Fadansa.
Malam Abdullahi ya gabatar da bayanai bisa kan ayyuka da makasudin taron da s**a gudanar na wannan shekara.

***** Malam Usman Ibrahim daga Makarantan Islamiyya da Sakandare na Tunawa da Bashir Babajo wanda ke Funtuwa a jihar Katsina ya jagoranci Malamai da Dalibai daga Makarantan wajen gabatar da ziyarar girmamawa gami da gani da ido ga Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a Fadansa.
Bisa umurnin Mai Martaba Sarkin Zazzau bayan mika godiyansa bisa wannan ziyara an zagaya da Daliban muhimman wuraren tarihi dake cikin Fadan Zazzau.

****** Shugaban Makarantan Awesons dake Zariya ya jagoranci Malamai da Daliban Makarantan wajen gabatar da ziyarar girmamawa gami da gani da ido ga Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a Fadansa.
Bayan kamalla wannan ziyara bisa umurnin Mai Martaba Sarkin Zazzau an zagaya da Daliban muhimman wuraren tarihi dake cikin Fadan Zazzau.

******* Shugabanin Kungiyar Koyar da Sana'a domin Dogaro da Kai a Arewa (SKILL-UP) sun gabatar da ziyarar girmamawa ga Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a Fadansa.
A lokacin wannan ziyara Malam Yusuf Jamoh ya gabatar da bayanai bisa kan ayyukan da kungiyar take gudanarwa ga Mai Martaba Sarkin Zazzau.

Aliyu Kwarbai.
Media & Publicity Office. Zazzau Emirate.

DAGA MASARAUTAN ZAZZAU:-A safiyan yau Alhaji Umar Sambo Shahada ya jagoranci wakilai daga al'umomin Maraban Jos da Birni...
22/06/2022

DAGA MASARAUTAN ZAZZAU:-

A safiyan yau Alhaji Umar Sambo Shahada ya jagoranci wakilai daga al'umomin Maraban Jos da Birnin Yero da Jama'are da Turunku da Anguwan Fulani Birnin Yero da Jama'are Fandeshun wajen tattaunawa da Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a Fadansa.

** Limamin Kona Malam Khalifa Ahmed Khalifa da Garkuwan Malaman Zazzau Alhaji Tukur Jabba wakilan Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli wajen bikin yayen Dalibai na;

(I) Makarantan Islamiyya na Anguwan Mai Fadama wanda ke Gwargwaje cikin Birnin Zariya hassawan Cibiyan Sheikh Abdulkadir Zariya da

(Il) Makarantan Attibyan wanda ke Anguwan Liman cikin birnin Zariya s**a gabatar da daliban da aka yaye ga Mai Martaba Sarkin Zazzau wanda ya sanya masu albarka.

*** Malam Umar Babuga Shugaban makarantan Matan Aure Na Hafsat Ibn Umar wanda ke Anguwan Iyan Juma cikin Birnin Zariya a madadin daliban makaranta ya jagoranci Malamai da Mahukuntan Makaranta wajen gabatar da godiyansu ga Mai Martaba Sarkin Zazzau bisa aika masu da wakilinsa Marafan Yamma Zazzau Alhaji Mustapha Ubaidullah a bikin yayen daliban da s**a gudanar a kwanakin baya.

Aliyu Kwarbai.
Media & Publicity Office. Zazzau Emirate.

GAYYATA! GAYYATA!! GAYYATA!!!. Aure Sunnar Annabi muyi koyi Ba Laifiba ne.. A Madadin Mahukunta Shafin Zage-Zagi A Yau.....
20/06/2022

GAYYATA! GAYYATA!! GAYYATA!!!.

Aure Sunnar Annabi muyi koyi Ba Laifiba ne..

A Madadin Mahukunta Shafin Zage-Zagi A Yau.. Suna Amfani da Wannan dama. Cikin Girmamawa da Biyayya. Suke Gayyatan yan'uwa da Abokan arziki. Zuwa Daurin Auren Daya daga Cikin Ma'aikatanta. ABUBAKAR SADIQ BELLO da Amaryarsa. SAFARA'U AHMAD I. BAGUDU.

Cikin Yardan Allah. Da Taimakonsa, Za'a Daura Auren ne Kamar Haka.

Ranan: Asabar 2/7/2022.
Lakoci: Karfe 11:00 na Rana.
Wurin: Daurin Auren. Gida Mai numba 4 Anguwar Katuka. Gidan Mai Girma Madauchin Zazzau.

Za'a Hadu a Gidan Marigayi Sarkin Zazzau Abubakar. Kwarbai Zaria City.

Allah yaba da ikon halarta. Amin.

Sanarwa daga.
Mahukunta Shafin Zage-Zagi A Yau.

DAGA MASARAUTAN ZAZZAU:-Da safiyan yau Litini Makaman Malaman Zazzau Alhaji Sani Yusuf Magaji ya jagoranci tawaga Jami'i...
20/06/2022

DAGA MASARAUTAN ZAZZAU:-

Da safiyan yau Litini Makaman Malaman Zazzau Alhaji Sani Yusuf Magaji ya jagoranci tawaga Jami'i daga Cibiyan Binciken Ma'adinai na Jami'ar Ahmadu Bello ta Zariya bisa karkashin Jagoranci Shugaban Cibiyan Farfesa S. A. Jonah wajen gabatar da ziyarar girmamawa ga Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a Fadansa.
Lokacin ziyarar Farfesa Jonah ya gabatar da bayanai bisa irin ci gaban da aka samu a wannan cibiya ga Mai Martaba Sarkin Zazzau a lokacin gabatar da wannan ziyara.

** Bajimin Kudun Zazzau Hakimin Gundumar Rigacikun Alhaji Abdurrashid Sani ya jagoranci Mahukuntan Kamfanin Sarrafa Tumatir (Tomato Jos) wanda aka kafa a Karamar Hukumar Igabi cikin 2017 Mai dauke da Ma'aikata 150 da Manoman Tumatir kusan 1000 wajen gabatar da ziyarar girmamawa ga Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a Fadansa.
Shugaban Masana'antan Missi Lee ta gabatar da bayanai bisa kan masana'antan ga Mai Martaba Sarkin Zazzau a lokacin gabatar da ziyaran wanda ya nuna farin cikin sa bisa samuwan Masana'antan gami da alkwarin bayar da gudunmuwar Masarautan Zazzau wajen ganin habbakan ta.

*** Alhaji Aminu Turaki Shugaban Kungiyan Tsoffin Dalibai na Kwalejin Koyon Kasuwanci da Aikin Akawu ta Zariya ya jagoranci jami'an kungiyan wajen gabatar da ziyarar girmamawa ga Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a Fadansa.
Alhaji Aminu ya gabatar da bayanai bisa kan kungiyan da kuma irin halin da Makarantan take ciki gami da godiya ga Mai Martaba Sarkin Zazzau da Majalisan sa bisa nada daya daga cikin 'Ya'yan kungiyan Alhaji Yusuf Abubakar Hayat a mukamin Magatakardan Masarautan Zazzau.
Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya nuna farin cikinsa bisa wannan ziyara tare da daukan alkwarin mika kukan shugabanin wannan kungiya bisa matsalolin dake addaban Kwalejin ga Hukumomin da s**a kamata.

**** Shuagabanin Kungiyar Musulumi Masu Yi Ma Kasa Hidima (NYSC MCAN) ta kasa reshen Jihar Kaduna bisa jagorancin Malam Ibrahim Suleiman Ibrahim sun gabatar da ziyarar girmamawa ga Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a Fadansa.
A lokacin wannan ziyarar membobin wannan kungiya sun sami tattaunawa da Mai Martaba Sarkin Zazzau kafin daga bisani ya bayar da umurnin zagaya wa dasu muhimman wuraren tarihi dake cikin Fadan Zazzau.

Aliyu Kwarbai
Media & Publicity Office Zazzau Emirate

DAGA MASARAUTAN ZAZZAU:-AN KARRAMA SARKIN ZAZZAUA safiyan yau Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli bisa ra...
18/06/2022

DAGA MASARAUTAN ZAZZAU:-

AN KARRAMA SARKIN ZAZZAU

A safiyan yau Mai Martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli bisa rakiyan 'Yan Majalisan Masarautan Zazzau da Hakimai da 'Yan Kasuwa da al'umman Anguwan Kwarbai gami da sauran masu ruwa da tsaki sun halarci kaddamar da ayyukan Gyara da Sabunta Makarantan Islamiyya na Anwaru Islam wanda Marigayi Magajin Garin Zazzau Alhaji Nuhu Bamalli ya Hassasa a Anguwan Kwarbai da kuma samar da Injunan Fitar da Kudi (ATM Gallery) a farfajiyan Fadan Zazzau wanda Bankin Fidelity ta samar bisa ayyukan kyautata ma al'umma da suke gudanarwa.
Kafin kaddamar da Makarantan wanda bikin ya sami halarcin Babban Darktan Shiyyan Arewa na Bankin Alhaji Hassan Imam sai da Mai Martaba Sarkin Zazzau ya kaddamar da 'yan kwamitin Amintattu na Makarantan.
Mai Martaba Sarkin Zazzau bayan kamalla kaddamar da aikin Makarantan ya koma fadansa a bisa kan Doki, inda ya kaddamar da Injunan Fitar da Kudi (ATM Gallery) da Bankin Fidelity ta samar a daura da kofan tunawa da Sarkin Zazzau Yamusa.

Aliyu Kwarbai.
Media & Publicity Office Zazzau Emirate.

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHIR RAJU'UN. Daga.Yusuf Yahaya Bamalli.Yanzu Muke Samun Labarin Rasuwan. Alhaji Muhammad Ladan K...
18/06/2022

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHIR RAJU'UN.

Daga.Yusuf Yahaya Bamalli.

Yanzu Muke Samun Labarin Rasuwan. Alhaji Muhammad Ladan Kafi. Wamban Bauchi. Za'ayi Jana'izarsa a Yau Asabar Da Misalin Karfe 9:00 Na Safe. A Kofar Fadar Mai Martaba Sarkin Bauchi.

Allah ya Gafarta Masa, Yasa Aljanna Makomansa, da Sauran Musulmi. Amin

Address

No. 15 Anguwan Katuka, Kwarbai Zaria City.
Kaduna

Telephone

+2348034610013

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Chairman Zage-Zagi a Yau. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Chairman Zage-Zagi a Yau.:

Share