Freedom TV Hausa

Freedom TV Hausa An bude shafin FREEDOM TV HAUSA Facebook ne ranar 5 ga watan December 2018 don wallafa labarai da bidiyo a harshen Hausa.

Godiya ta tabbata ga Allah Madaukakin saki

Kamfanin sadarwa na 9 Mobile ya canza suna zuwa T2. Yanzu masu amfani da 9 Mobile za su ga ya canza zuwa T2.A baya, kamf...
09/08/2025

Kamfanin sadarwa na 9 Mobile ya canza suna zuwa T2. Yanzu masu amfani da 9 Mobile za su ga ya canza zuwa T2.

A baya, kamfanin yana amsa sunan Etisalat, daga shekara 2008 zuwa 2017. Daga baya ya koma 9mobile bayan janye hannun jarin 'yan kasuwa UAE. A yanzu kuma, ya sauya daga 9Mobile zuwa T2.

Gwamnan Kano ya nemi duk Kwamishinan da ya san ba zai iya ba,  ya ajiye aikinsa.
06/08/2025

Gwamnan Kano ya nemi duk Kwamishinan da ya san ba zai iya ba, ya ajiye aikinsa.

Idan kuna bukatar tallace - tallace za ku iya tuntubar mu ta wannan lambar kai tsaye kira ko WhatsApp. 08163617923 Ko 08...
03/08/2025

Idan kuna bukatar tallace - tallace za ku iya tuntubar mu ta wannan lambar kai tsaye kira ko WhatsApp.
08163617923 Ko 08141662524
Zamu tallata muku hajojin ku akan Farashi mai Rahusa
Freedom TV Hausa .

22/12/2024

Kuyi muna tagging din duk wani Malamin addini da kuma mutane masu daraja da kuka sani.

Let's f0ll0w them now👇👇

Ƙasar Iran me kimanin mutum Miliyan 90 suna maraba da zuwan jagoran Harkar Musulunci a Najeriya Maulana Shaikh Ibraheem ...
11/10/2023

Ƙasar Iran me kimanin mutum Miliyan 90 suna maraba da zuwan jagoran Harkar Musulunci a Najeriya Maulana Shaikh Ibraheem Zakzaky.

Labarin zuwan Shaikh Zakzaky ƙasar Iran shi ne labari mafi yaɗuwa a dukkan kafofin sadarwa na ƙasar Iran tsawon kwana 3 a jere.

Dubban ɗalibai Iranawa da ƴan ƙasashen waje, musamman Najeriya masu karatu a ƙasar s**ayi cikar gaske a filin jirgin sama na Imam Khumaini da safiyar Laraba, dake Tehran domin su tari Jagora Shaikh Zakzaky.
Kasuwanni dayawa sun rufe, ofisoshi dayawa sun tafi hutu kowa ya fita domintarbar Jagoran Harkar Musulunci Shaikh Ibraheem Zakzaky.

Ɗalibai sun bar makarantu domin ganin babban bako Shaikh Zakzaky, wakilan Gwamanti da manyan malamai su ne a gaba wajan tarban Shaikh Zakzaky.

Wata ƴar Jarida me suna Zainba Reza, ta tabbatar min da cewa, wannan shi ne cika mafi girma a tarihi tun bayan sake fasalin filin jirgin da sake buɗe shi a ranar 8/May/2004 .

Maraba da sauka Jagora.
—Bilya Dass

Isowar Shiekh Ibrahim Zakzaky (H)Tuni dai Filin Sauka da Tashin jiragen Sama na Imam Khumaini dake birnin Tehran Jamhuri...
11/10/2023

Isowar Shiekh Ibrahim Zakzaky (H)

Tuni dai Filin Sauka da Tashin jiragen Sama na Imam Khumaini dake birnin Tehran Jamhuriyar Musulunci ta Iran ya cika maƙil da almajirai da Masoya Sheikh Zakzaky a daidai lokacin da ake dakon saukar sa a wannan birni..

Tun shekaran Jiya dai ƴan Gwagwarmaya dake Iran suke ta yaɗa sanarwar gagarumar tarbar da s**a shiryawa shehin malamin dake hanya zuwa ƙasar don zuwa asibiti neman Magani tare da iyalin Sa.

Ana saran jirgin zai sauka karfe 10:21 na wannan safiya agogon Iran karfe 7:51 agogon Nigeria.

Allah ya sakko dasu lafiya

ImamHasArrived
ShugabaYaIso
#امامآمد
Saifullahi Ɗandume

Al'ummar wasu garuruwa dake karamar hukumar Binji a jihar Sokoto s**a fara barin garuruwansu zuwa gudun Hijira saboda ma...
06/10/2023

Al'ummar wasu garuruwa dake karamar hukumar Binji a jihar Sokoto s**a fara barin garuruwansu zuwa gudun Hijira saboda matsalar tsaro. Kamar yadda Mubashir Suleiman mazaunin garin ya bayyana

Suna gudun hijira ne a sakomakon matsalar Rashin Tsoro da ke cigaba da Addabar Yankunan na Asarar Rayuka da sace-sacen mutane, a kullu yaumin.

Yadda Al-ummar Arewacin Nigeria ke cigaba da kaura daga Yankunan su Sakomakon matsalar Rashin Tsoro da ke cigaba da Adda...
06/10/2023

Yadda Al-ummar Arewacin Nigeria ke cigaba da kaura daga Yankunan su Sakomakon matsalar Rashin Tsoro da ke cigaba da Addabar Yankunan na Asarar Rayuka da sace-sacen mutane, a kullu yaumin.

Shin kuna ganin Haryanzu akwai sauran mafita a wurin wadannan miyagun Azzaluman yan siyasar nan kuwa..??

06/10/2023

Wani mahalifi ya daddatsa dan cikinsa a Jihar Akwa Ibom, bayan ya zarge shi da hakar masa rogo a gona ba tare da izini ba jaridar Aminiya na ruwaito. Ana zargin mutumin mai suna cif Akpan Aniekan da daddatsa dan nasa mai suna Boniface Innocent Uko mai shekara 26 mazaunin kauyen Ebe Ikpe a Karamar

Naira Tiriliyan Daya (1,000,000,000,000.00), Sune Kuɗin Da Wani Babban Sojan Nijeriya Ya Sace. Ta Yaya Za Mu Samu Tsaro?...
05/10/2023

Naira Tiriliyan Daya (1,000,000,000,000.00), Sune Kuɗin Da Wani Babban Sojan Nijeriya Ya Sace. Ta Yaya Za Mu Samu Tsaro?

Cewar Barr. Abba Hikima

Fitaccen Mawaƙi Naziru Sarkin Waƙa ya ce kar wanda ya sake kiransa da sunan ya ɗaga kwali, ya yin gangamin neman ƴanci.Y...
04/10/2023

Fitaccen Mawaƙi Naziru Sarkin Waƙa ya ce kar wanda ya sake kiransa da sunan ya ɗaga kwali, ya yin gangamin neman ƴanci.

Ya ƙara da cewa “amma idan fita ce, kowa ya yi sallama da iyalansa a fita kar a dawo sai da ƴanci, a dawo da rai da ƴanci, ko a dawo ba rai da ƴanci, wannan duk muna maraba da shi, amma bana maraba da inyi rubutu in nuna ko in ɗaga kwali, ban kuma ce waɗanda s**a yi basu san me suke ba. Inji Sarkin Waƙa

Wani matashi kenan a Nijeriya daya faɗo daga saman mota inda ya turje fuska tare da jin wasu raunuka ana tsaka da nuna f...
01/10/2023

Wani matashi kenan a Nijeriya daya faɗo daga saman mota inda ya turje fuska tare da jin wasu raunuka ana tsaka da nuna farin ciki da tunawa da zagayowar samuwar 'yancin kai.

Address

Kaduna

Telephone

+2348163617923

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Freedom TV Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Freedom TV Hausa:

Share