MC Arewa Sab multimedia

MC Arewa Sab multimedia Justice, Fairness and Equity in every report reaching out to you.

Ko makiyan Buhari sun san bai yi sata ba - AkpabioShugaban majalisar dattawa Sanata Godswill Akpabio, ya kwatanta mariga...
17/07/2025

Ko makiyan Buhari sun san bai yi sata ba - Akpabio

Shugaban majalisar dattawa Sanata Godswill Akpabio, ya kwatanta marigayi Muhammadu Buhari a matsayin shugaba na gari wanda ya mulki Najeriya ba tare da satar duƙiyar ƙasa ba.

Akpabio, ya bayyana hakan ne a lokacin taron majalisar zartaswa da aka gudanar a Abuja don yi wa Marigayi Buhari addu'o'i, ya ce masu s**arsa ma sun san cewa bai yi almubazzaranci da duƙiyar ƙasa ba lokacin da yake mulki.

Atiku bai kyauta ba da ya sauya sheƙa a lokacin makokin rasuwar Buhari - Festus Keyamo Ministan sufurin jiragen sama da ...
17/07/2025

Atiku bai kyauta ba da ya sauya sheƙa a lokacin makokin rasuwar Buhari - Festus Keyamo

Ministan sufurin jiragen sama da bunƙasa harkokin samaniya na Najeriya, Festus Keyamo ya soki tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, kan sauya sheƙa da ya yi daga jam'iyyar PDP a daidai lokacin da ake makokin rasuwar marigayi shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa Muhammadu Buhari.Sanarwar ya fito daga bakin shugaba Tinubu ne...
17/07/2025

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa Muhammadu Buhari.

Sanarwar ya fito daga bakin shugaba Tinubu ne lokacin taron majalisar zartaswa da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

"Kafin mu fara addu'o'i domin karrama Buhari, ina sanar da ku cewa mun sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa Muhammadu Buhari," in ji Tinubu.

17/07/2025

"Gaskiyar magana ba ni na haka kabarin Marigayi MUHAMMADU BUHARI ba"

Inji dattijon da akayi hira dashi a baya har yace shi ya haka.

Tawagar  Sheikh Bala Lau da Sheikh Yahaya Jingir sun halarci addu’ar Ukkun marigayi MUHAMMADU BUHARI yau a Daura
17/07/2025

Tawagar Sheikh Bala Lau da Sheikh Yahaya Jingir sun halarci addu’ar Ukkun marigayi MUHAMMADU BUHARI yau a Daura

Fitaccen ɗan siyasa kuma tsohon gogaggen ɗanjaridar nan na Najeriya, Dele Momodu ya bayyana ficewarsa daga jam'iyyar PDP...
17/07/2025

Fitaccen ɗan siyasa kuma tsohon gogaggen ɗanjaridar nan na Najeriya, Dele Momodu ya bayyana ficewarsa daga jam'iyyar PDP zuwa sabuwar haɗakar ADC ta yan hamayya.

A RA'AYIN KU;Wane ne zai maye gurbin Buhari a siyasar arewacin Najeriya?
17/07/2025

A RA'AYIN KU;
Wane ne zai maye gurbin Buhari a siyasar arewacin Najeriya?

WATA SABUWA; Buhari Yayi Min Wasiyyar Cewa ‘Don Allah In Kula Da Talakawan Najeriya’ – Peter Obi
16/07/2025

WATA SABUWA;
Buhari Yayi Min Wasiyyar Cewa ‘Don Allah In Kula Da Talakawan Najeriya’ – Peter Obi

16/07/2025

Yarinyar Marigayi MUHAMMADU BUHARI, ta baiyana sako da mahaifinta ya bata zuwa ga yan Najeriya a lokacin da yake kwance a Gadon Asibiti a London.
゚viralシfypシ゚

Rahotanni sun ce aƙalla mutum 27 ne ake zargin ƴanbindiga sun kashe a jihar Filato da ke tsakiyar Najeriya.An kuma jikka...
16/07/2025

Rahotanni sun ce aƙalla mutum 27 ne ake zargin ƴanbindiga sun kashe a jihar Filato da ke tsakiyar Najeriya.

An kuma jikkata wasu da dama.

Wannan hari na zuwa ne kimamin wata ɗaya da kai wani hari da ya hallaka kusan mutum 200 a wani ɓangare na jihar.

Mazauna jihar sun bayyana kaɗuwa da harin, wanda s**a ce ƴanbindigar da s**a kai shi sun je ne ɗauke da manyan bindigogi a safiyar Talata.

Maharan sun bi gida zuwa gida, inda s**a yi ta hallaka mutane da kuma cinna wa gidajensu wuta.

Wani jami'i a jihar ya shaida wa BBC cewa an ƙona wata jaririya mai kimamin wata uku tare da iyayenta.

Shi ma wani shugaban matasa ya bayyana cewa yawanci waɗanda lamarin ya rutsa da su, sun ƙone har ta kai ba a iya gane su.

Sun yi zargin cewa sojoji da ke kusa da wajen da aka kai harin sun ƙasa kai musu ɗauki yayin harin.

Ana sa ran gwamnan jihar ta Filato zai kai ziyara zuwa waɗannan al'ummomi da harin ya shafa - mai nisan kilomita 50 da Jos, babban birnin jihar.

Rahoton BBC

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya sanar da ficewa daga babbar jam'iyyar adawa ta PDP.
16/07/2025

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya sanar da ficewa daga babbar jam'iyyar adawa ta PDP.

A hasashen ku...
16/07/2025

A hasashen ku...

Address

Kaduna

Telephone

+2348056036969

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when MC Arewa Sab multimedia posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to MC Arewa Sab multimedia:

Share