07/04/2026
Fassarar Deewanin 'Maulanah Sheikhul Islam, Alhaji Ibrahim Nyass Alkaulakhy Attijjany RTA' Zuwa Harshen Hausa
Bissmillahir Rahmaneer Raheem - Wa Sallallahu Alan Nabiyil Kareem
- Harful Aleep:
Darasi Na Biyu (002)
٨- فَـنَشْأَتُهُ كَنْزِيَّةُ الْـحَقِّ وَحْــدَهُ
لِـذَاكَ أَتَانَـا قَــاسِمًا وَمُقَــسَّمَا
8- Sa'annan Faruwar Sa SAW ita ce taskar Gaskiya shi kaɗai
Saboda Haka ne ma Yazo Mana Shine mai Rabo, kuma Shine Mai Raba Dukkan Rabon Duniya da Lahira.
٩- فَـآيُ جَمِيـعِ الرُّسْلِ آيُ مُحَمَّدٍ
فَمِنْـهُ إِلَيْـهِ كُـلَّ شَـأْنٍ مُعَمَّمَــا
9- Sa'annan Ayoyin Dukkan Manzannin Allah (Mu'ujizoji), Ayoyin Annabi Muhammad SAW ne (Mu'ujizojin Sa ne)
Kuma Dukkan Lamura daga Gare Shi Suke Wanzuwa Izuwa Gare Shi Baki ɗaya, SAW.
٠١- مَوَاهِبُ رَبِّ الْعَرْشِ طَهَ مُحَمَّدٌ
وَرَحْمَتُهُ هُوَ الرَّحِـيمُ فَـأَكْرِمَـــا
10- Kyaututtukan Ubangijin Al'arshi, Shine Ɗaha Annabi Muhammadu SAW
Kuma shine Rahamar Sa, Shine Mai Yawan Jinƙai, Dan Haka Ka Kai Matuqa Cikin Girmama Shi SAW.
١١- بَشِيرٌ نَذِيرٌ مُقْسِطٌ وَهْوَ قَاسِـــمٌ
جَوَادٌ كَرِيمٌ بَاسِطُ الْكَفِّ مُنْعِمَــا
11- Manzon Allah SAW mai Bushara ne, Mai Gargaɗi, Mai Kaiwa Matuqa Wajen Adalci, Kuma Shine Mai Raba Dukkan Alkhairan Ubangiji
Mai Yawan Kyauta ne, Mai Girman Karamci, mai shinfiɗa tafin Baiwa ne ga Dukkan Halitta, Mai Ni'imtarwa ne SAW.
١٢- مُقَفًّى أَمِينٌ وَهْـوَ فِي الرُّسْـلِ مُجْتَبًى
حَبِــيـبُ إِلَــــهِ الْعَـرْشِ بَــدْءاً وَمَخْتَمَا
12- Cikamakin Annabawa ne Shi SAW, Amintaccen Ubangiji Kuma Amintaccen Bayin Sa, Kuma Shi Zaɓaɓɓe ne a Cikin Dukkan Manzanni Baki Daya,
Masoyin Ubangijin Al'arshi tun daga Farko Har Zuwa Karshe SAW
١٣- وَأَبْيَضُ يُسْتَسْقَى الْغَمَامُ بِوَجْهِــــهِ
بِهِ نَارَ لَيْلُ الْجَهْلِ إِذْ كَـانَ مُــظْـلِمَــا
13- Kuma Shi (Annabi SAW) Mai Farin Fuska ne Wanda Ake Neman Shayar da Ruwan Sama (A Wajen Allah) da Albarkar Fuskar sa SAW,
Da Shi ne Aka Haska Daren Jahilci a Lokacin da yake Cikin tsananin Duhu (ta Hanyar Bayyanar Hasken Muslumci)
١٤- قُلُوبَ جَمِيـعِ الْخَلْقِ أَحْيَا بِنُورِهِ
وَأَلْسُـنَهُمْ أَحْـيَا فَــزَكَّـى وَعَلَّمَـــا
14- Zukatan Dukkan Halitta an Rayata ne Da Hasken Sa (Saboda Hasken Sa Ya Darsu a Ciki) SAW
Kuma ya raya Halsunansu, ya tsarkake su, kuma ya koyar da su Ilimai, SAW.
Mu Hadu a Darasi na Uku (3)
Allah qara mana Soyayyar Manzon Allah SAW da Iyalan Gidan Sa Da Dukkan Sahabban sa, Ameen 🤲