Hasken Zamani 24

Hasken Zamani 24 DOMIN SAMUN LABARU DA DUMI DUMINSU KASANCE DA SHAFIN GASKIYA NEWS 24.

Allah Ya yi wa Samira Isah Modibbo rasuwa a yau, kuma za a gudanar da jana’izarta da ƙarfe 9 na safe a gidansu da ke bay...
06/08/2026

Allah Ya yi wa Samira Isah Modibbo rasuwa a yau, kuma za a gudanar da jana’izarta da ƙarfe 9 na safe a gidansu da ke bayan Government Secondary School, Makarfi Road, lamba 16 Kangiwa Road, layin Asibitin MSK, Rigasa, Kaduna

Samira Isah Modibbo ta kasance ƙwararriyar mai harkar fasaha da kasuwanci, ƙwararriyar ayyukan ci gaba da kuma jagorar al’umma, wadda ta samu horo a fanni da dama

Ta shafe sama da shekaru da dama tana aiki a fannonin jin ƙai da ƙungiyoyin sa-kai, inda ta ba da gudunmawa wajen ƙarfafa mata, ilimi da fasaha a Najeriya.

A tsawon shekarun da ta yi tana gudanar da ayyukanta, Samira ta jagoranci tare da tallafa wa ƙungiyoyi da dama wajen aiwatar da ayyukan da s**a taimaka wajen sauye-sauyen manufofi, tare da ilmantarwa da ƙarfafa mata, ƙananan yara mata da yaran da ba sa zuwa makaranta sama da dubu 27.

Allah Ya jiƙanta da rahama, Ya gafarta mata, Ya kuma bai wa iyalanta da ‘yan uwanta haƙurin jure wannan babban rashi. Amin.

NEMAN TAIMAKO FISABILILLAH Kungiyar Khairul Ummah Humanitarian foundation tana Rokon Al'umma Da Su Taimaka Wajen ceto ra...
06/08/2026

NEMAN TAIMAKO FISABILILLAH

Kungiyar Khairul Ummah Humanitarian foundation tana Rokon Al'umma Da Su Taimaka Wajen ceto rayuwar Zainab Sunusi Dake Karamar Hukumar funtua Jihar katsina Wacce za'ayi ma dashen kashi akan kudi Naira Miliyan Biyar.

Kungiyar ta roki al'ummar Annabi Muhammadu (s.a.w) da su Bada Taimakon su gwargwadon Karfin su. Domin Ceto wannan marainiyar sabo da Allah.

Ga Account na kungiyar khairul Ummah kamar haka 👇👇👇👇

FIDELITY BANK
A/c56017606-95
Khairul Ummah Humanitarian Foundation

Domin Karin Bayani a tuntubi 08037624598

Allah ya Bada Ikon taimakawa Ameeen.

YAKIN DA YA SA AKA ƊAGA SHI DAGA MAJOR ZUWA LIEUTENANT COLONEL A CIKIN FILIN DAGA! A lokacin da Boko Haram s**a mamaye G...
06/08/2026

YAKIN DA YA SA AKA ƊAGA SHI DAGA MAJOR ZUWA LIEUTENANT COLONEL A CIKIN FILIN DAGA!

A lokacin da Boko Haram s**a mamaye Gamboru-Ngala, mutane da dama sun yi zaton garin ba zai sake komawa hannun Najeriya ba.

Sai wani matashin kwamanda ya ce:

"Ko mu kwato garin, ko mu mutu a ƙoƙarin yin hakan."

Wannan kwamandan shi ne Lt. Col. Muhammad Abu Ali.

Shi ne ya jagoranci 272 Task Force Battalion a sahun gaba wajen kai farmakin da ya karya ƙarfin Boko Haram a Gamboru-Ngala. Ba ya ɓoye a baya yana bada umarni; yana tare da dakarunsa a gaban yaƙi, yana ƙarfafa musu gwiwa har aka sake daga tutar Najeriya a garin.

Jarumtakar da ya nuna ta girgiza rundunar soji.

bayan samun wannan babbar nasara, Babban Hafsan Sojin Ƙasa na lokacin, Lt. Gen. Tukur Yusuf Buratai, ya kai ziyara Gamboru-Ngala da tsakar dare domin taya dakarun murna da kuma yaba musu. A can ne ya sanar da ƙarin girman Muhammad Abu Ali daga Major zuwa Lieutenant Colonel, tare da ba shi lambar yabo ta musamman saboda jarumtakar da ya nuna a fagen daga.

Wannan ba karin girma ne na ofis ba...

Karin girma ne da aka samu da jini, da gumi, da sadaukar da kai a filin yaƙi.

Sai dai a ranar 4 ga Nuwamba, 2016, Muhammad Abu Ali ya sake shiga gaba wajen fafatawa da Boko Haram a Mallam Fatori, inda ya rasu yana yaƙi tare da dakarunsa.

Wasu jarumai suna rayuwa ne domin ƙasa... wasu kuma suna mutuwa domin al'umma ta rayu.

Allah Ya jiƙan Lt. Col. Muhammad Abu Ali. Za a ci gaba da tuna jarumtarsa har abada.

Shin kuna kallon shirin kasango kuwa?
05/08/2026

Shin kuna kallon shirin kasango kuwa?

Fadi kalma Daya akan wannan Bawan Allah.
01/08/2026

Fadi kalma Daya akan wannan Bawan Allah.

Gwamnatin Nigeria ta lalata haramtattun makamai masu dinbin yawa da Niyyar Kawo karshen matsalar tsaro a Kasar.
01/08/2026

Gwamnatin Nigeria ta lalata haramtattun makamai masu dinbin yawa da Niyyar Kawo karshen matsalar tsaro a Kasar.

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Muhammadu Sanusi II ya cika shekaru 65 a duniya.Shin wanne Fata zakuyi mashi?
31/07/2026

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Muhammadu Sanusi II ya cika shekaru 65 a duniya.

Shin wanne Fata zakuyi mashi?

Jana'izar Sardaunan Sokoto Alhaji Abubakar Alhaji tsohon Ministan Kuɗi a Lokacin Gwamnatin Soji ta Janar Ibrahim Badamas...
30/07/2026

Jana'izar Sardaunan Sokoto Alhaji Abubakar Alhaji tsohon Ministan Kuɗi a Lokacin Gwamnatin Soji ta Janar Ibrahim Badamasi Babangida, kuma Tsohon Jekadan Najeriya a Birtaniya

Alhaji Abubakar Alhaji ya rasu yana da shekaru 88 a Duniya. An yi masa Jana'iza a Masallacin Sarkin Musulmi Muhammad Bello Dake Kan Wuri Sokoto.

Hoto daga Shafin Sultanent Council na Fesbuk

Malam Rabi'u Mai Ɗan Kai Ya Rasu A Jihar KanoZai yi wuya wanda yake cikin ƙwaryar Kano da wasu sassa na gefenta a ce bai...
30/07/2026

Malam Rabi'u Mai Ɗan Kai Ya Rasu A Jihar Kano

Zai yi wuya wanda yake cikin ƙwaryar Kano da wasu sassa na gefenta a ce bai san shi ba, saidai ƴan bana-bakwai.

_*Sulemana Abdul Samed,* wanda aka fi sani da *Awuche* kuma aka san shi a matsayin mutumin da ya fi kowa tsawo a *Ghana,...
30/07/2026

_*Sulemana Abdul Samed,* wanda aka fi sani da *Awuche* kuma aka san shi a matsayin mutumin da ya fi kowa tsawo a *Ghana,* ya rasu yana da shekaru *33* a duniya._

_*Awuche* ya shafe tsawon lokaci yana fama da matsalolin lafiya da ke da nasaba da yanayin girman jiki *(gigantism)*._

_Ƴan makonni kafin hakan, ɗan kasuwa *Ibrahim Mahama* ya yi alƙawarin ɗaukar nauyin dukkan kuɗaɗen maganinsa bayan an yi kira da a taimaka masa._

Address

Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hasken Zamani 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hasken Zamani 24:

Shortcuts

Share

Category