Shurafa FORUM MEDIA Kaduna

Shurafa FORUM MEDIA Kaduna Ahlul Baiti Jirgin Tsira

04/02/2025

Sayyadi Hurera yahaya Gilima itama ta baiyana irin farin cikin da tayi na maludin kakan ninta ahlul baiti a.s kamar yadda zakuji

Wa'innan wakilan sheik mansur imam ne suma sun qayatar da gudun mawarsu ta begen Sayyida Fatima s.a
04/02/2025

Wa'innan wakilan sheik mansur imam ne suma sun qayatar da gudun mawarsu ta begen Sayyida Fatima s.a

04/02/2025
04/02/2025

Sidi mika'il shima yayi dan tsokaci dan gane da murnar maulud daya gudana kamar yadda zakuji

04/02/2025

Babbar baquwarmu daga bauci Sayyida Fatima itama ta baiyana mana irin farincikin ta na wannan babban taron maulidin sharifai daya gudana ranan lahadi 2/2/2025

Posto yayi magana ne akan hadin kai da zaman lafiya da kaunar juna yabada uzri anyimasa rasuwa yatafi,  muna miqa ta'azi...
04/02/2025

Posto yayi magana ne akan hadin kai da zaman lafiya da kaunar juna yabada uzri anyimasa rasuwa yatafi, muna miqa ta'aziyyarmu daukacin shurafa'u bakidaya Allah yajikan Wanda yarigamu gidan gaskiya.

An karrama wasu Sharifai da koren kyelle Allah ta'ala yakarawa iyalan gidan Annabi s.a.w.w martaba.
04/02/2025

An karrama wasu Sharifai da koren kyelle Allah ta'ala yakarawa iyalan gidan Annabi s.a.w.w martaba.

An karrama sarkin bakin sarkin sokoto, Sharif abulkadir,  Wanda ya sadaukar da dukiyar sa domin yiwa Annabi s a w w da i...
04/02/2025

An karrama sarkin bakin sarkin sokoto, Sharif abulkadir, Wanda ya sadaukar da dukiyar sa domin yiwa Annabi s a w w da iyalabsa a.s

03/02/2025

Yadda sharifai s**a baiyana farincikinsu kamar yadda sidi shamsu yake fada a hirar da akayi dashi

03/02/2025

An karrama Sharif Al Alawi, da koren kyelle kamar yadda kuke gani a cikin bidiyo

03/02/2025

Yadda sharifai s**a nuna farin cikinsu kamar yadda sidi abubakar Dan baiwa kaduna yafada

SHURAFA SUN SHIRYA GAGARUMIN MAULUDI A KADUNAA yau Lahadi, 03/08/1446, dandalin Shurafa na Harka Islamiyya karkashin Jag...
03/02/2025

SHURAFA SUN SHIRYA GAGARUMIN MAULUDI A KADUNA

A yau Lahadi, 03/08/1446, dandalin Shurafa na Harka Islamiyya karkashin Jagorancin Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) na na kasa su ka shirya gagarumin Mauludin Annabi Muhammad (S) da imam Ali (as) da sayyida fadima (s a), Mauludin ya gudana ne a 'Hall' na NUT, Magadishu da ke garin Kaduna.

Mauludin Wanda ya 'kayatar tare da faranta ran Masoya duka mahalarta taron, ya Sami bakuncin Manyan mutane da kuma malamai daban_daban, inda su ka baje kolin jawabai na falalar ahlul baiti a.s

Sayyid Badamasi Ya'akub, Dan uwa ga Jagoran Harka Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) shi ne ya fara gudanar da jawabi a wurin Taron, Shehin Malamin ya tabo bangarori da dama, Cikin jawabin ya tabo bangaren darajar Sayyada Zahra (Sa), ya yi bayani dangane da Bara'a da wilaya, Sannan Kuma ya ja hankalin Mahalarta Taron dangane da Kiran mutane zuwa ga son Ahlul Bait (As), Sannan ya hankaltar da 'yan uwa dangane da jarabawoyin da ke fuskantowa da duk Wanda yace zeso ahlul baiti

Daga bisani sharif sidi Al-Alawi Kano ya gabatar da nashi jawabin, Shima ya tabo janibobi da dama dangane da darajar Ahlul Bait (As), sannan se akaba Shaikh Abdul Hameed Bello Abun magana shima shehin ya gabatar da nashi jawabin, Inda ya fara da tunawa mutane dangane da wasiyyar da Manzon Allah (S) ya barwa Al'umma Kafin barinshi Duniya, wato Kur'ani da Ahlul Bait, ya yi bayani bangaren Bara'a da wilaya, sannan ya ja hankalin Mahalarta dangane da yada soyayyar Ahlul Bait Cikin Al'umma, ya yi magana dangane da sadaukarwa da Kuma hadin Kai.
Bayan kammala jawabin shehin malaminne akabawa Malam Yahya makaho inda yace shima ba a barshi a baya ba, ya zo wurin tare da bayar da gudummawarshi a wurin Taron, Inda ya rera wake ga Annabi Muhammad (S).

Sannan Fasto Yohanna Yd Buru ya yi Dan takaitaccen jawabi tare da sanyawa Taron albarka da fatan Allah ya maimaita mana na shekara Mai zuwa.

Bayan haka, Shareef Isa Ikon Allah, Wanda aka bashi jawabi Mai taken Dangantar Imam Ali (As) da Alkur'ani Mai girma'. , Malamin yayi takaitaccen bayani dangane da Imam Ali (As), Sannan ya sanarwa Mahalarta Taron mafarkin da yayi da Imam Ali (As) Kafin fitowarshi wurin Taron, bayan haka ya farantawa Mahalarta Taron da maganar tabbatar Addin Musulunci a wannan nahiya.

Bayan haka, Shareef Ahmad Rufa'i Shima ya yi jawabi, yayin da ya fara da maganar Manzon Allah (S) Wanda ya ke cewa "Ku ladabtar da 'Ya'yanku akan abubuwa guda uku, Son Annabinku, son Ahlul Bait da karatun Alkur'ani Mai girma"!. Ya ja hankalin Mahalarta sosai gaske dangane da riko da Ahlul Bait.

Malam Salisu Khalifa ya farantawa Mahalartan zukata da kasidu na yabon Ahlul Bait (As), bayan shi Yaran Sayyida Sun yi 'Display tare da wasu bakin da su ka gudanar da wakokin Sayyida (As)

Malama Jamila Auwal (Uwar gidan Malam Mukhtar Sahabi Kaduna) ta yi jawabi dangane da Sayyida Zahra (S A), Inda fado daraja na Wanda aka sawa sunan Sayyida Zahra tare da dabi'un da ya kamata ta lizimta domin kowa da Ita Sayyida Zahra (As).

Daga bisani Wakilin 'yan uwa na garin Kaduna, Malam Aliyu Umar Tirmizi ya Dora da nashi jawabin, Inda ya yi godiya ga Allah ta'ala dangane da kasancewarsu Masu Imani da Wilaya, Sannan ya ja hankalin 'yan uwa dangane da Sallah a Kan lokaci.

Daga karshe an yanka Alkaki tare sannan aka yi addu'a aka sallami kowa.

SHURAFA FORUM MEDIA KADUNA
2/2/2025
3/8/1445

Address

Kaduna
800283

Telephone

+2349033191609

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Shurafa FORUM MEDIA Kaduna posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Shurafa FORUM MEDIA Kaduna:

Share