Shurafa FORUM MEDIA Kaduna

Shurafa FORUM MEDIA Kaduna Ahlul Baiti Jirgin Tsira

MAUKIB SHURAFA'U ALI MUHAMMAD S.A.W.W Wanda yahada da sharifai daban daban na fadin kaduna agun taron maulidin fiyayyan ...
08/09/2025

MAUKIB SHURAFA'U ALI MUHAMMAD S.A.W.W

Wanda yahada da sharifai daban daban na fadin kaduna agun taron maulidin fiyayyan halitta Muhammad s.a.w.w

Wanda akasabayi duk shekara,12 ga Rabiyul awwal, ranar asabar 6/9/2025



6/September 2025

JAGORA (H) YA GANA DA 'YAN UWA A MUNASABAR ASHURADaga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) Jagora ya gana da ba'adin 'yan...
06/07/2025

JAGORA (H) YA GANA DA 'YAN UWA A MUNASABAR ASHURA

Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

Jagora ya gana da ba'adin 'yan uwa a yau Asabar 9 ga Almuharram 1447 a gidansa da ke Abuja, a munasabar juyayin Shahadar Abi Abdullahil Husain (AS).

A yayin jawabinsa, Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya bayyana Ashura a matsayin alama da ta fita daban, inda yace, babu yini kamar ranar Ashura, domin yini ne da ya alamta dukkannin zalunci. “Duk irin wani zalunci da za ka siffata ya auku a doron duniya to Ashura ya alamta shi. Don haka Ashura darasi ne babban gaske, shi yasa raya shi raya addini ne.”

Yace, Imam Husaini (AS) ya fito ne da nufin kawo gyara a al'ummar kakansa (S), da yin umurni da kyakkyawa da hana munkari. “Wannan sai ya ƙare a bayar da kansa (a yanka) a Karbala. To wannan abinda ya fito dominsa, wanda shi ne ya karata da yin Shahada, shi ne muke rayawa. An ce masa ko dai ya mika wuya ne a fasa wannan, ko kuma (ya miƙa) kansa, sai ya ba da kansa. Don haka muke cewa, shi Imam Husaini (AS) ya yi 'thaura', wato ya yi juyin-juya-hali, ya sauya tunanin mutane, ya nuna musu cewa, ba a karɓan zalunci, ba a yarda da zalunci, ba a bin azzalumai.”

Jagora ya bayyana nasara a matsayin tsayawa ƙyam a tafarkin Allah ko da za a Shahadantar da mutum kamar yadda Imam Husaini (AS) ya yi. “A wasikar Imam Husaini (AS) ga yan uwansa, ya ce musu, wanda ya biyo ni zai yi Shahada, kuma wanda ya zauna ba zai yi nasara ba. To ku fada mini, mece ce nasara? Shahada.”

Yace, “Da ace Imam Husaini ya miƙa wuya ne, sai ya zauna lafiya ya yi wa'azi, ka ga kenan da yanzu ya zama Sunnah, in ka tashi kace ya kamata a kawo sauyi, sai a ce ka kai Imam Husaini ne, da ya ga abinda ya gani ai miƙa wuya ya yi, saboda haka don me kai ma ba za ka miƙa wuya ba? Da sai miƙa wuya ga azzalumai ya zama shi ne addini.

Jagora ya bayyana cewa, har yanzu mutum na da damar kasancewa tare da Imam Husaini (AS) kuma ya samu rabo irin na wanda s**a kasance tare da shi. “Duk wanda kuka gan shi yanzu yana mara ma azzalumai baya, in a wancan lokacin yake, wa zai mara ma? Azzalumai. Wanda ka ga ya dake akan sai dai ko a kashe shi, amma ba zai bar tafarkin Allah ba, to irin shi ne zai bi Imam Husaini da ace ya zo a lokacinsa."

Yace, inda za ka tambayi Namarud wa kake so ka ka`she? Zai ce Ibraheem (AS). Firauna kuma wa yake so ya ka`she? Musa (AS). Lokacin Manzon Rahma (S) su Abujahal, Walid Bin Mugira, Abu Sufyan bin Harb duk wa suke son su ka`she? Annabi (S). A lokacin Mu'awiyya Dan Abisufyan, lokacin Ali (AS) na raye, inda za ka tambaye shi wa yake so ya ka`she? Zai ce Amirulmuminin (AS). To Yazidu kuma wa yake so ya ka`she? Imam Husaini (AS). To yanzu fa, Trump da Netanya`hu wa suke so su ka`she? Sayyid Khamenie. Don haka yace: “Ka ga kowane Fir'auna da Musansa. Ya kamata ka san wane ne Fir'aunan wannan zamanin, wane ne kuma Musa a wannan zamanin. In ka san wannan za ka gane wane ne Yazidun zamaninka, wane ne Husainin zamaninka... Saboda idan kana tare da Yazidun yau, ba abinda zai raba ka da Yazidun zamanin jiya in da a zamanin ka zo.”

A karshe, Jagora (H) ya yi kira da mu ɗauki darasin da Ashura ke koyar da mu na sadaukarwa da tsayawa ƙyam ba tare da wasu dabaru ba. “Mutum ya tsaya ƙyam tsakani da Allah, ƙyam-ƙyam-ƙyam saboda Allah, ko me zai faru ya faru. Sadaukarwa saboda Allah, saboda Allah, saboda Allah. Mu ɗauka ma kawukanmu wani alƙawari guda; mu ɗauka ma Imam Husaini (AS) alkawarin cewa abin nan da ya fito dominsa, za mu cigaba daga inda ya tsaya har ya zuwa bayyanar wanda da bayyanarsa ne za a samu mafita insha Allah, Allah Ya gaggauta bayyanarsa.”








09/Al-Muharram/1447
05/July/2025

06/07/2025
Muna taya ɗaukacin al'ummar Musulmi murnar shiga sabuwar shekarar Hijjah ta 1447. Muna roƙon Allah Ta'ala Ya sadar da mu...
27/06/2025

Muna taya ɗaukacin al'ummar Musulmi murnar shiga sabuwar shekarar Hijjah ta 1447. Muna roƙon Allah Ta'ala Ya sadar da mu da alheran da ke cikin wannan shekara; Ya kuma kiyaye mu daga sharrukan da ke cikinta.

Allah Ta'ala Ya maimaita mana; Ya nuna mana na shekaru masu zuwa cikin ƙoshin lafiya da yalwar arziki.






01/Al-Muharram/1447
27/06/2025

SANARWA! SHEKARAR 1446 TA KAMMALA بسم الله الرحمن الرحيماللهم صل على محمد وال محمد وعجل فرجهم. Ana sanar da ƴan'uwa cewa...
26/06/2025

SANARWA!

SHEKARAR 1446 TA KAMMALA

بسم الله الرحمن الرحيم

اللهم صل على محمد وال محمد وعجل فرجهم.

Ana sanar da ƴan'uwa cewa yau Alhamis 29 ga Zhul Hijjah shekarar 1446 ta kawo ƙarshe don ta cika kwana 355 daidai. Don haka gobe Juma'a za ta zama 1 ga watan Al-Muharram 1447.

Kada a manta da ayyukan ƙarshen shekera a yau da kuma ayyukan sabuwar shekara gobe. Akwai salloli da addu'o'i ma'thurai na waɗannan ranakun. A duba cikin مفاتيح الجنان da sauran littafan addu'o'i.

Kamar yadda aka saba za a shiga zaman jajen tunawa da shahadar Abi Abdillah (AS) daga gobe ke nan, in sha Allah.

السلام على الحسين المظلوم الشهيد 🙏






29/ZulHijja/1446
26/06/2025

04/02/2025

Sayyadi Hurera yahaya Gilima itama ta baiyana irin farin cikin da tayi na maludin kakan ninta ahlul baiti a.s kamar yadda zakuji

Wa'innan wakilan sheik mansur imam ne suma sun qayatar da gudun mawarsu ta begen Sayyida Fatima s.a
04/02/2025

Wa'innan wakilan sheik mansur imam ne suma sun qayatar da gudun mawarsu ta begen Sayyida Fatima s.a

04/02/2025

Sidi mika'il shima yayi dan tsokaci dan gane da murnar maulud daya gudana kamar yadda zakuji

04/02/2025

Babbar baquwarmu daga bauci Sayyida Fatima itama ta baiyana mana irin farincikin ta na wannan babban taron maulidin sharifai daya gudana ranan lahadi 2/2/2025

Posto yayi magana ne akan hadin kai da zaman lafiya da kaunar juna yabada uzri anyimasa rasuwa yatafi,  muna miqa ta'azi...
04/02/2025

Posto yayi magana ne akan hadin kai da zaman lafiya da kaunar juna yabada uzri anyimasa rasuwa yatafi, muna miqa ta'aziyyarmu daukacin shurafa'u bakidaya Allah yajikan Wanda yarigamu gidan gaskiya.

An karrama wasu Sharifai da koren kyelle Allah ta'ala yakarawa iyalan gidan Annabi s.a.w.w martaba.
04/02/2025

An karrama wasu Sharifai da koren kyelle Allah ta'ala yakarawa iyalan gidan Annabi s.a.w.w martaba.

Address

Kaduna
800283

Telephone

+2349033191609

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Shurafa FORUM MEDIA Kaduna posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Shurafa FORUM MEDIA Kaduna:

Share