AMANA PRESS

AMANA PRESS An samar da wannan kafar ce domin bayar da labarai kamar yadda suke ba tare da nuna wani bambanci ko son rai ba. Haka ma muna fassara wato Translation.
(2)

BOOT PARTY, TA TSAIDA COMRADE SUNUSI INUWA ZAGI A MATSAYIN DAN TAKARAN GWAMNAN JIHAR BAUCHI.A wani zaman daidaito da "ya...
01/06/2026

BOOT PARTY, TA TSAIDA COMRADE SUNUSI INUWA ZAGI A MATSAYIN DAN TAKARAN GWAMNAN JIHAR BAUCHI.

A wani zaman daidaito da "ya"yan Jam'iyyar Boot mai alaman Takalma s**a gudanar a ranar juma'a 29/5/2026, sun tsaida comrade Sunusi Inuwa Zagi domin yi masu takarar gwamnan jihar Bauchi a zaben 2027.
Sun gabatar da daidaiton ne bisa amincewar wakilai da s**a halarci zaman, kuma nan take s**a aminta da tsayawar matashin.
Da yake jawabi jim kadan bayan kaddamar da shi, matashin ya sha alwashin inganta shugabanci na gari, tare da muhimmanta matasa, kuma yasha alwashi matukar ya kai ga nasara zai maida mafi karancin albashin Ma'aikatan jihar Bauchi #100,000.
Jam'iyyar Boot Jam'iyya don inganta gobe.

Tsohon Dan Majalisar  Tarayya Mai Wakiltar Dawakin Kudu Da Warawa Mustapha Bala Dawaki Ya Canza Sheka Daga Jam'iyyar APC...
30/05/2026

Tsohon Dan Majalisar Tarayya Mai Wakiltar Dawakin Kudu Da Warawa Mustapha Bala Dawaki Ya Canza Sheka Daga Jam'iyyar APC Zuwa NDC

Yayin da babban zaben kasa na shekarar 2027 ke kara kusantowa, shugaban ma'aikata na helkwatar jam'iyyar APC ta kasa (Chief of Staff), kuma tsohon dan Majalisar Tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Dawakin kudu da Warawa a jihar Kano, kuma dan takarar komawa majalisar a kakar zabe ta 2027, Alhaji Mustapha Bala Dawaki ya canza sheka daga jam'iyyar APC zuwa jam'iyyar NDC ta su Injiniya Dakta Rabi'u Musa Kwankwaso.

Canjin shekar ta sa ya biyo bayan zargin rashin adalci da shi da magoya bayansa ke yi, dangane kwarfiya da aka yi musu yayin zaman sulhu da jam'iyyar ta yi na fidda 'yan takarkarun majalisun jiha dana tarayya karkashin jagorancin Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf.

Hakan nan zaben fidda gwani na wanda zai tsayawa jam'iyyar takarar dan majalisar tarayyar na kato bayan kato da aka gabatar a kafatanin mazabun kananan hukumomin Dawakin kudu da Warawa, bayan rashin samun daidaito tsakanin 'yan takarkarun, wanda aka baiwa dan majalisar jiha mai ci a yanzu, Alhaji Shu'aibu Rabi'u Nagoggo Gano nasara ya bar baya da kura, inda magoya bayan Mustapha Bala Dawaki su kai zargin an tafka magudi yayin tattara kuru'un da aka kada a zaben.

Tuni dai dimbin magoya bayan tsohon dan majalisar tarayyar ke bayyana ficewarsu daga tsohuwar jam'iyyar ta sa ta APC a fili, ta hanyar aikawa da sakonni a shafukan sada zumunta na zamani, da kuma nuna sabon katin shaidarsu na shiga jam'iyyar NDC da s**a mallaka.

Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Magani Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin LafiyaGwamnatin Jihar Zamfara ta bay...
21/05/2026

Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Magani Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya

Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana cewa, ta gudanar da aikin kula da marasa lafiya 6,842 ta hanyar babban shirin tallafin lafiya kyauta da aka tanada domin yi wa al’umma tiyata da sauran kulawar lafiya ba tare da biyan kuɗi ba.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an ce an fara aiwatar da shirin tun daga watan Agustan shekarar 2023 a manyan cibiyoyin lafiya da s**a haɗa da Asibitin Ƙwararru na Yariman Bakura, Babban Asibitin Gusau, Cibiyar Kula da Ido ta Gusau da kuma Asibitin Farida.

Sanarwar ta ce, kashi na 015, 016 da 017 na shirin tallafin lafiyar an gudanar da su daga ranar Juma’a 1 ga watan Mayu zuwa Lahadi 17 ga watan Mayun 2026.

A cewar gwamnatin jihar, shirin ya haɗa da yi wa marasa lafiya tiyatar ciwon ido na yanar ido, wato cataract, cututtukan kumburin mara irin su hernia da hydrocele, gyaran matsalar yoyon fitsari ga mata (VVF), tare da wayar da kan jama’a kan muhimmancin kula da lafiya.

Sanarwar ta ƙara da cewa, shirin na daga cikin manufofin Gwamna Dauda Lawal na magance manyan matsalolin lafiya da ake fama da su domin inganta rayuwa da walwalar al’ummar jihar Zamfara.

“Shirin Tallafin Lafiya na Musamman da aka gyara yana ba da damar samun kulawar lafiya kyauta ga masu fama da cututtukan da s**a haɗa da cataract, hernia, hydrocele da kuma gyaran matsalar yoyon fitsari ga mata,” in ji sanarwar.

Gwamnatin ta kuma bayyana cewa baya ga bayar da magani, ana amfani da shirin wajen ilmantar da jama’a kan muhimmancin kula da lafiya da tsaftar rayuwa.

An bayyana cewa an gudanar da ayyukan jinyar ta hanyar amfani da tsarin tantance marasa lafiya ta fasahar sadarwa domin kai kulawar ƙwararru zuwa yankunan karkara da ƙananan birane a ƙananan hukumomi 14 na jihar.

Sanarwar ta ce, kashi 17 da aka gudanar zuwa yanzu sun haɗa da tiyata 5,282 da kuma jinyar wasu marasa lafiya 1,200, inda aka kula da masu cututtukan kumburi da masu fama da cataract, mata masu matsalar VVF da sauran nau’o’in tiyata na musamman da na gama gari.

Gwamnatin jihar ta jaddada aniyarta ta ci gaba da gudanar da irin wannan tallafin lafiya musamman domin taimaka wa marasa ƙarfi da masu buƙata a faɗin jihar.

20/05/2026

Ga gaskiya abin da ya faru a Fagge ta Jihar Kano

SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR FAGGE HON SALISU USUMAN MASU, KENAN YAYIN GUDANAR DA TABBATAR DA ZABEN FIDDA GWANI NA DAN MAJALISAR JAHA HON TUKUR MUHAMMAD.

17/05/2026

Za mu tabbatar da Shugaban Kasa Tinibu da Gwamna Namadi sun maimaita - Injiniya Ahmad Zakari OON Santurakin Kazaure Dan Takarar Majalisar Tarayya Kazaure, Roni da 'Yan Kwashi a Jihar Jigawa.

11/05/2026

Yadda muka kafa kasuwar Dakatsalle da ke karamar hukumar Bebeji Jihar Kano inji Shugaban Kasuwar ALH. UMAR ABDULLAHI LAW AND LAW.

Abba Kabir Yusuf

09/05/2026

Shugaban Kasuwar Gafan a Ƙaramar Hukumar Garun Malam ya Kai karar Shugaban Ƙaramar Hukumar wajen Gwamna Abba Kabir Yusuf saboda yunkurin rufe musu kasuwar da suke kula da iyalansu

Rahama Sadau press

TARON APC A ZAMFARA: Gwamna Lawal Ya Tabbatar Da Cewa Ƙarfin Gwamnati Na Rataye Ne Da Kyawawan Tsare-tsaren Jam’iyyaGwam...
07/05/2026

TARON APC A ZAMFARA: Gwamna Lawal Ya Tabbatar Da Cewa Ƙarfin Gwamnati Na Rataye Ne Da Kyawawan Tsare-tsaren Jam’iyya

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jaddada cewa nasara da ɗorewar kowace gwamnati na da alaƙa kai tsaye da ƙarfinta a fagen siyasa, musamman yadda jam’iyyarta ke da tsari mai ƙarfi da haɗin kai.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin da ya halarci taron zaɓen shugabannin jam’iyyar APC na Jihar Zamfara, wanda aka gudanar a filin baje kolin kasuwanci da ke Gusau.

A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, wakilai 745 daga ƙananan hukumomi 14 da kuma mazabu 147 na jihar ne s**a zaɓi sabbin shugabannin jam’iyyar APC ta jihar ta hanyar amincewa da juna ba tare da gardama ba.

Sanarwar ta ƙara da cewa, Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, Hadiza Sabuwa Balarabe, wadda ta jagoranci kwamitin gudanar da zaɓen, ita ce ta tabbatar da sakamakon tare da halartar rantsar da sabbin shugabannin jam’iyyar.

A jawabin da ya gabatar, Gwamna Lawal ya bayyana taron a matsayin lokaci mai muhimmanci kuma mai ma’ana ga ci gaban jam’iyyar, yana mai cewa hakan wata dama ce ta ƙarfafa tsarin jam’iyya da inganta dimokuraɗiyya a cikinta.

Ya ce, “Wannan tsari da ya kai ga zaɓe, tabbatarwa da kuma rantsar da sabbin shugabanni, wani muhimmin mataki ne da ke ƙara tabbatar da gaskiya, adalci da sahihancin jam’iyyarmu a matakin jiha da ƙasa.”

Gwamnan ya kuma gode wa shugabannin jam’iyyar a matakin ƙasa bisa jagoranci da goyon bayan da suke bayarwa wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya a cikin APC, tare da yabawa kwamitin zaɓen bisa ƙwarewa da gaskiyar da s**a nuna wajen gudanar da aikin.

Ya ƙara da cewa, taron ya kasance wata hanya ce ta sabunta alƙawarin jam’iyyar na haɗin kai, ladabi, haɗa kowa da kowa da kuma yi wa jama’a hidima, yana mai jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da aiwatar da tsare-tsare da s**a shafi tsaro, noma, ilimi, lafiya, gine-gine da bunƙasar tattalin arziki domin tabbatar da ci gaba mai ɗorewa a Zamfara.

“Mun san cewa ƙarfan gwamnati yana fitowa ne daga ƙarfan ginshiƙin siyasa. Jam’iyya mai haɗin kai da tsari mai kyau ita ce ke samar da ingantaccen shugabanci da ci gaba. Wannan taro na da matuƙar muhimmanci wajen daidaita tsarin jam’iyya da manufofin gwamnati,” inji shi.

A nasa jawabin karɓar muƙami, sabon Shugaban APC na Jihar Zamfara, Honorabul Kabiru Moyi B/Magaji, ya yi alƙawarin inganta dimokuraɗiyya a cikin jam’iyyar tare da ƙarfafa haɗin kai a tsakanin mambobinta.

Address

Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AMANA PRESS posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AMANA PRESS:

Share