AMANA PRESS

AMANA PRESS An samar da wannan kafar ce domin bayar da labarai kamar yadda suke ba tare da nuna wani bambanci ko son rai ba. Haka ma muna fassara wato Translation.

09/04/2026

Labaran AMANA PRESS, yau dai an yi waya tsananin Jami an Saudiyya da Iran

WATA KUNGIYA A GANJUWA TA KARRAMA SABON SAKATAREN TSARE-TSARE NA JAM'IYYAR APC JIHAR BAUCHI.Daga: Lawal Kafin Madaki.Wat...
08/04/2026

WATA KUNGIYA A GANJUWA TA KARRAMA SABON SAKATAREN TSARE-TSARE NA JAM'IYYAR APC JIHAR BAUCHI.

Daga: Lawal Kafin Madaki.

Wata kungiya mai zaman kanta a Jam'iyyar App Mai suna: Tsintsiya madaurinki Daya, reshen Gundumar Kafin Madaki, karamar hukumar Ganjuwa jihar Bauchi ta shirya Walima kare da karra wasu "ya"yan Jam'iyyar da s**a yi fice wurin hidimta wa al'ummarsu.
Kungiyar ta karrama mutane Hudu da s**a hada da: Shugaban Apc na jihar Bauchi, Hon. Muhammad Hassan Tilde, tare da sabon Sakataren Tsare-tsare na jiha Hon. Muhammad Bello Kari (Sallau B.Kafi) sai Dantakarar majalisar wakilai a Darazo/Ganjuwa, Hon. Bashir Ibrahim Bello tare da sugaban APC gundumar Kafin Madaki Hon. Hamza Bala Kafi.
Shugaban Kungiyar Hon. Safiyanu Abubakar Manja, ya bayyana ce wa sun shirya walima ne wa sabbin masu ruwa da tsaki (Exco) da aka zabo daga gundumar Kafin madaki, sannan sun yi amfani da wannan dama s**a karramar mutane Hudu da suke taka rawar gani a wannan mazaba tasu.

Hon. Nura Zungur (State Ex-officio) ne ya wakilci shugaban APC na jiha sakamakon rashin kasancewarsa a gari inda ya tafi wani aikin Jam'iyya.
Taron ya sami halartar "ya"yan Jam'iyyar tare da "yan'uwa da abokan arziki, inda aka gabatar da jawabai mabanbanta.

06/04/2026

Yadda Hon Isa Ashiru Kudsn ya Sami gaharumar tarba a mahaifarsa
Bello Kudan Gambo Jibrin Kudan Kemi Talks

RAHOTO: Zuwan Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna, Hon. Isa Ashiru Kudan Zuwa Jam’iyyar ADCDaga: Faruq Sani Kudan An gudanar da w...
05/04/2026

RAHOTO: Zuwan Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna, Hon. Isa Ashiru Kudan Zuwa Jam’iyyar ADC

Daga: Faruq Sani Kudan

An gudanar da wani gagarumin taro a yau inda tsohon ɗan takarar gwamna a Jihar Kaduna, Hon. Isa Ashiru Kudan, ya sanar da sauya sheƙa tare da shiga sabuwar jam’iyyar siyasa ta ADC (African Democratic Congress).

A cikin jawabin nasa, Hon. Isa Ashiru Kudan ya jaddada muhimmancin wayar da kan al’umma, inda ya ce lokaci ya yi da jama’a za su farka daga halin da suke ciki, su nemi mafita mai dorewa domin samun ingantacciyar shugabanci a zaɓe mai zuwa na shekarar 2027.

“Al’umma ya kamata su farka sosai, su duba halin da ake ciki, su kuma nemi mafita da za ta kai su ga makoma mai kyau,” in ji shi.

Ya kuma bayyana cewa akwai mutane da dama a Jihar Kaduna da s**a fara komawa jam’iyyar ADC, yana mai cewa wannan alama ce da ke nuna yadda jama’a ke neman sauyi a harkar siyasa.

Haka zalika, ya yi kira ga al’umma da kada su bari a rinjaye su da kuɗi yayin zaɓe. Ya ce:

“Idan s**a ba ku kuɗi, ku karɓa, amma ku tabbatar kun yi zaɓin da ya dace da zuciyarku a wajen kaɗa ƙuri’a a zaɓen 2027.” ku kada su su faɗi ƙasa warwars

Hon. Isa Ashiru Kudan ya ƙara da cewa jam’iyyar ADC na da burin kawo sauyi na gaskiya tare da samar da shugabanci nagari wanda zai inganta rayuwar al’umma baki ɗaya.

Rahotanni sun nuna cewa wannan sauya sheƙa na iya sauya yanayin siyasa a Jihar Kaduna, musamman ganin yadda magoya baya ke ci gaba da sauya akala zuwa sabuwar jam’iyyar.

02/04/2026

Wannan shi ne jerin sunayen da aka sallama da wadanda aka ba sabbin mukamai a NURTW Kaduna

30/03/2026

Idan baka mutu ba komai sai ka gani a wannan duniya .

12/03/2026

Yanzu shi ke nan babu 'yan adawa a Nijeriya?

11/03/2026

Abubuwan da ake buƙata aikatawa kwana goma na karshen Ramadan tare da Zainab Idris Bamalli (Kilishin Barden Malaman Zazzau)

09/03/2026

Kwalejin Tulip International Kaduna ta shirya wa 'Yan Jarida bukin shan ruwa

09/03/2026

Abin da ya kamata ku aikata a goman karshe na watan Ramadan

Address

Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AMANA PRESS posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AMANA PRESS:

Share