Dimokuradiyya

Dimokuradiyya Dimokuradiyya Adon Kasa. Youtube Channel: Dimokuradiyya TV An kafa Jaridar Dimokuraɗiyya ne Domin Tabbatar Da Mulkin da Jama'a s**a zaɓa da kansu Dan su Amfana.
(11)

Jarida ce da a ka kafa domin samar da labarai da dumi-dumin su, dambarwar siyasa, binkicen kwakwaf, da Nishadi, domin tabbatar da mulkin da jama'a s**a zaba don su amfana.

02/06/2026

ZAUREN DIMOKURADIYYA: Zailani da Uba Sani Kowa Na Buƙatar Kowa, Don Haƙa Muna Nemawa Zailani Afuwa Daga Mai Girma Gwamnan Kaduna.

02/06/2026

Labarun duniya daga nan Dimokuraɗiyya

02/06/2026

Gwamna Uba Sani Ya Yi Addu’ar Allah Ya Tona Asirin Masu Haddasa Matsalar Tsaro

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya yi addu’ar Allah Ya tona asirin duk masu haddasa matsalar tsaro, ko da kuwa suna cikin gwamnati ne.

Ya bayyana hakan ne yayin da ya kai ziyara tantunan alhazan Jihar Kaduna a Mina, inda ya ce: “Allah Ya tona asirinsu, Ya yi maganinsu, idan kuma masu shiriya ne, Allah Ya shirye su.”

Tinubu Ya Yaba wa MOFI Kan Samar da Lamunin Gidaje na Naira Biliyan 128 ga Iyalai 1,859Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu,...
02/06/2026

Tinubu Ya Yaba wa MOFI Kan Samar da Lamunin Gidaje na Naira Biliyan 128 ga Iyalai 1,859

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yabawa Hukumar Kula da Kadarorin Gwamnatin Tarayya ta Najeriya (MOFI) bisa nasarar samar da lamunin gidaje na Naira biliyan 128 ga iyalai 1,859 a faɗin ƙasar.

Tinubu ya ce wannan nasara ta nuna cewa manufofin gwamnati na iya taimakawa wajen faɗaɗa mallakar gidaje ga ’yan Najeriya, musamman ta hanyar samar da lamuni mai sauƙin biya.

Ya ƙara da cewa shirin ya nuna yadda gyare-gyaren tattalin arziki da saka hannun jari a fannin gidaje za su iya inganta rayuwar al’umma tare da rage matsalar ƙarancin gidaje a ƙasar.

Buratai: Hukumomin Tsaro Za Su Iya Gano Maboyar Ƴan Bindiga Idan S**a Nemi HakaTsohon Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Najeri...
02/06/2026

Buratai: Hukumomin Tsaro Za Su Iya Gano Maboyar Ƴan Bindiga Idan S**a Nemi Haka

Tsohon Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Najeriya kuma tsohon Jakadan Najeriya a Jamhuriyar Benin, Tukur Buratai, ya bayyana cewa hukumomin tsaron ƙasar na da fasahar da za su iya gano tare da bibiyar ƴan bindiga da masu garkuwa da mutane da ke aikata laifuka a sassa daban-daban na ƙasar nan.

Buratai ya ce jami’an tsaro na da ƙwarewa da kayan aikin zamani da za su iya gano inda masu laifin suke, yana mai jaddada cewa idan aka yi amfani da waɗannan dabaru yadda ya kamata, za a samu nasara wajen daƙile ayyukan ta’addanci da garkuwa da mutane.

Ya kuma yi kira da a ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro domin magance matsalolin tsaro da ke addabar wasu yankunan Najeriya.

Wike: Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja Batu ne na Tsaron Ƙasa, Ina Tafiya a HankaliMinistan Babban Birnin Tarayya Abuja...
02/06/2026

Wike: Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja Batu ne na Tsaron Ƙasa, Ina Tafiya a Hankali

Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya bayyana cewa yawan shanun da ke yawo a titunan Abuja batu ne da ya shafi tsaron ƙasa, yana mai cewa yana tafiyar da lamarin cikin taka-tsantsan domin kauce wa rikice-rikice.

Wike ya ce ba daidai ba ne a ci gaba da ganin dabbobi suna yawo a cikin babban birnin ƙasar, yana mai jaddada cewa manufar gwamnati ita ce inganta kiwon zamani ta hanyar kiwo a wurare na musamman (ranching).

Ya kuma amince da cewa har yanzu ana ganin shanu a wasu titunan Abuja, lamarin da ya ce gwamnati na ci gaba da ƙoƙarin magancewa.

Ministan ya ƙara da cewa gwamnatin babban birnin tarayya na buƙatar goyon bayan jama'a da kafafen yaɗa labarai wajen wayar da kan al'umma domin kare martaba da kyawun Abuja.

02/06/2026

'Tinubu Jan Wuya ne a Murde Zabe': Babachir Lawal na Ganin APC za Ta Zarce

Ƴan Majalisar Wakilai 13 Sun Sauya Jam’iyya, Chinda Ya Yi Murabus Daga Matsayin Jagoran Marasa RinjiAkalla ƴan majalisar...
02/06/2026

Ƴan Majalisar Wakilai 13 Sun Sauya Jam’iyya, Chinda Ya Yi Murabus Daga Matsayin Jagoran Marasa Rinji

Akalla ƴan majalisar wakilai 13 ne s**a sanar da sauya jam’iyyarsu a zaman Majalisar Wakilai, lamarin da ya kara sauya fasalin siyasar majalisar gabanin zaben 2027.

Daga cikin masu sauya sheka akwai wasu da s**a fice daga APC zuwa PDP, wasu kuma daga PDP zuwa APM da sauran jam’iyyu.

A wani ci gaba mai alaka da hakan, tsohon Jagoran Marasa Rinji a Majalisar Wakilai, Kingsley Chinda, ya ajiye mukaminsa bayan sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.

Matakin ya kawo karshen takaddamar da ta dade tana tattare da ci gaba da zamansa a matsayin jagoran ‘yan adawa bayan rahotannin sauya jam’iyyarsa.

Sauya shekar ta baya-bayan nan na nuna yadda ake ci gaba da samun sauye-sauyen siyasa a Majalisar Tarayya yayin da shirye-shiryen zaben 2027 ke kara daukar zafi.

Gwamnatin Tarayya Ta Soke Hutun Ritaya Na Watanni Uku Ga Ma’aikataGwamnatin Tarayya ta umarci ma’aikatu, hukumomi da cib...
02/06/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Soke Hutun Ritaya Na Watanni Uku Ga Ma’aikata

Gwamnatin Tarayya ta umarci ma’aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnati da su daina tura ma’aikata hutun ritaya na wajibi na watanni uku kafin su bar aiki.

Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya, Didi Walson-Jack, ta bayyana cewa dokokin aikin gwamnati ba su tanadi irin wannan hutu ba, sai dai sun wajabta sanarwar watanni uku kafin ritaya da halartar taron shiryawa ritaya.

Saboda haka, ma’aikata za su ci gaba da aiki har zuwa ranar ritayarsu a hukumance.

02/06/2026

PDP Ta Motsa a Kano, Ta Ɗauki Matsaya game da Takarar Jonathan a 2027

Address

No: 21 4Th Avenue Sa'adu Zungur Street Gwarimpa FCT, Abuja
Kaduna
800273

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dimokuradiyya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Dimokuradiyya:

Share

Category