Dimokuradiyya

Dimokuradiyya Dimokuradiyya Adon Kasa. Youtube Channel: Dimokuradiyya TV An kafa Jaridar Dimokuraɗiyya ne Domin Tabbatar Da Mulkin da Jama'a s**a zaɓa da kansu Dan su Amfana.
(4)

Jarida ce da a ka kafa domin samar da labarai da dumi-dumin su, dambarwar siyasa, binkicen kwakwaf, da Nishadi, domin tabbatar da mulkin da jama'a s**a zaba don su amfana.

Ƙasar Saudiyya ta haramta ƙara kuɗaɗen haya har na tsawon shekaru BiyarYarima mai jiran gado na Masarautar Saudiyya, Muh...
26/09/2025

Ƙasar Saudiyya ta haramta ƙara kuɗaɗen haya har na tsawon shekaru Biyar

Yarima mai jiran gado na Masarautar Saudiyya, Muhammad bn Salman ne ya bayar da umarnin dakatar da ƙarin kuɗin haya na tsawon shekaru 5 a birnin Riyadh da ke ƙasar.

Wannan doka wadda za ta fara aiki daga ranar 25 ga Satumbar 2025, za ta shafi gidajen zama da kuma wurare sana’a da dai sauransu.

Dokar ta ce ko kaɗan masu gidajen ba za su iya ƙara kuɗin haya ba har zuwa tsawon shekarun nan biyar cur da a ka ambata.

Har wa yau, kowane mai haya zai ci gaba da biyan kuɗin da yake biya kai tsaye ba tare da ƙari ba tsawon shekarun kuma mai gida ba shi da ikon karɓe gidansa daga hannun ɗan haya a tsakanin shekarun sai dai idan ta k**a mai gidan ne zai koma gidansa da zama ko kuma ɗan haya ya fita a karan kansa ko kuma idan gidan ne ya samu wata matsala ta daban.

26/09/2025

Gwamnatin jihar Bauchi ta kori wasu manyan ma'aikatan Bogi Biyu a jihar

Ga rahoton Salma Musa

Barr Bukarti ya mai da martani kanƙi amincewa da jam'iyyar matasa da hukumar zaɓe ta ƙasa taƙi amincewa da itaDalili ɗay...
26/09/2025

Barr Bukarti ya mai da martani kanƙi amincewa da jam'iyyar matasa da hukumar zaɓe ta ƙasa taƙi amincewa da ita

Dalili ɗaya tak da INEC ta bayar na watsi da nemanmu na rajistar Access Party shine wai cewa "alamar AP ta yi k**a da ta DLP". Don Allah ku duba ku gani. Ta yaya waɗanda alamomi biyu su ka k**a?

Abinda doka ta hana shine alamun jam'iyyu biyu su zama iri ɗaya ko kuma su yi k**a sosai ta yadda za su rikitar da mai zaɓe. Dan Allah ta yaya waɗannan alamomi biyu za su rikitar wani mai hankali?

Mu a gani mu INEC ta na neman yi mana rashin adalci ne kawai saboda suna tsoronmu. Ƴansiyasa suna ganin wannan tafiya za ta zama musu babbar barazana a 2027. Wannan alamar nasara ce in shaa Allah.

Mun rubuta wa INEC martani cewa su buɗe tattaunawa da mu cikin kwanaki bakwai domin mu warware wannan matsala. Idan ba su yi haka ba, za mu shigar da ƙara, mu nemi cewa kotu ta tilastawa INEC ta yi mana rejista.

Hukumar zaɓen Najeriya ta yi watsi da buƙatar su Bulama Bukarti ta yi wa Tafiyar Matasa rajista a matsayin jam‘iyyar siy...
26/09/2025

Hukumar zaɓen Najeriya ta yi watsi da buƙatar su Bulama Bukarti ta yi wa Tafiyar Matasa rajista a matsayin jam‘iyyar siyasa da sunan Access Party

Ku biyo mu zamu kawo muku cikkaken bayani.

Sojoji sun k**a masu ba da labari ga 'yan ta'adda har su 26Cikakken rahoto na nan tafe
25/09/2025

Sojoji sun k**a masu ba da labari ga 'yan ta'adda har su 26

Cikakken rahoto na nan tafe

INA GIZO KE SAƘAR? Jagoran ƴan adawa a siyasar Najeriya, Atiku Abubakar ya nuna damuwar sa yana mai cewa a kullum sai an...
25/09/2025

INA GIZO KE SAƘAR? Jagoran ƴan adawa a siyasar Najeriya, Atiku Abubakar ya nuna damuwar sa yana mai cewa a kullum sai an rasa rai a kasar nan saboda sakacin da gwamnati ke yi a ɓangaren tsaro, a lokaci guda kuma gwamnatin Tinubu na nuna farin cikin cikar burinta na tara kudaden shiga a asusunta, Inji shi.

25/09/2025

Labarun duniya a taƙaice

25/09/2025

FAƊI MU JI; Kalli Wannan Bidiyon in ke ce zaki yadda a yi Miki kishiyar nan kuwa?

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un.Cikin tsananin jimami da Alhini muna sanar da rasuwar mahaifiyar Malam Ibraheem Musa...
25/09/2025

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un.

Cikin tsananin jimami da Alhini muna sanar da rasuwar mahaifiyar Malam Ibraheem Musa babban sakataren yada labarai na Gwamnatin Jihar Kaduna.

An shirya yi mata Sallar Janaza k**ar yadda addinin Musulunci ya tanadar yau Alhamis da misalin karfe 1:30 na rana a yau a Unguwan Shanu Kaduna (Layin ‘Yan Taba).

Muna rokon Ubangiji Allah ya gafarta mata kurakuranta, ya saka mata da Aljannah.

Cibiyar masu karatun Alƙur’ani ta ƙasa ta nesanta kanta daga nadin da aka ce an yi wa tsohon gwamnan Kano, Dr. Abdullahi...
25/09/2025

Cibiyar masu karatun Alƙur’ani ta ƙasa ta nesanta kanta daga nadin da aka ce an yi wa tsohon gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, a matsayin Khadimul Qur’an.

Shugaban cibiyar, Goni Sunusi Abubakar, ya bayyana cewa babu hannusu a naɗin, inda wata ƙungiya ta bogi ta yi amfani da takardar cibiyar don yin nadin.

Cibiyar ta ja kunnen jama’a da malamai su yi watsi da ikirarin, tare da jaddada cewa jagoranci sahihi na cibiyar yana hannun Goni Sunusi Abubakar da amintattun shugabanni na ƙasa.

25/09/2025

BIDIYO: Najeriya ta sake neman kujerar dindindin na kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya, ta kuma soki kalaman diflomasiyya game da rikice-rikicen Gabas ta Tsakiya - tare da dagewa kan samar da kasashe biyu don warware yakin Isra'ila da Falasdinu

Hotunan gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf yayin da ya sake sahale fitar da naira biliyan biyar don biyan haƙƙoƙ...
24/09/2025

Hotunan gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf yayin da ya sake sahale fitar da naira biliyan biyar don biyan haƙƙoƙin ma'aikata

Address

No. 218 Mogadishu Layout Kaduna City Center Ahmadu Bello Way Kaduna.
Kaduna
800273

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dimokuradiyya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Dimokuradiyya:

Share

Category