Freedom Radio Kaduna

Freedom Radio Kaduna Freedom Radio 92.9 Kaduna mun himmatu wajen isar da sahihan labarai, shirye-shiryen nishaɗi, faɗakarwa, ilimantarwa, tare da bayyana ra'ayin al'umma.
(3)

Muryar Jama'a! guda cikin jerin gidajen Rediyo na Freedom Radio Group, Freedom Radio Nigeria

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya, NDLEA, ta gargadi iyaye da su ƙara sanya ido kan kayan zaƙi da...
09/08/2026

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya, NDLEA, ta gargadi iyaye da su ƙara sanya ido kan kayan zaƙi da ’ya’yansu ke yawan ci, musamman biskit da alewa mai laushi.

Daraktan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a na hukumar, Femi Babafemi, ya ce samamen da NDLEA ta gudanar a baya-bayan nan ya bankaɗo ƙoƙarin masu safarar miyagun ƙwayoyi na ɓoye haramtattun abubuwa cikin wasu kayan abinci na yau da kullum.

Babafemi ya shawarci iyaye da su yi taka-tsantsan idan s**a lura ’ya’yansu ko matasa na yawan neman wasu nau’o’in biskit ko alewa, saboda wasu daga cikin kayayyakin na iya ƙunsar abubuwan da ba a zato.

Gargadin na zuwa ne bayan NDLEA ta ƙwace wasu kwantena biyu masu tsawon ƙafa 40 a Legas, inda aka gano kayayyaki masu ɗauke da tabar wiwi da aka ɓoye cikin kayayyakin da ake shigo da su ƙasar.

Daga cikin kayayyakin da aka gano akwai motocin da aka yi amfani da su, janareto, batura da yadudduka, baya ga dubban fakitin alewa mai laushi da aka haɗa da tabar wiwi da kuma wasu nau’o’in biskit masu ɗauke da ita.

Hukumar ta ce wannan sabon salon ɓoye miyagun ƙwayoyi na buƙatar ƙarin taka-tsantsan daga iyaye da sauran masu kula da yara domin kare matasa daga haɗarin amfani da haramtattun ƙwayoyi.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya shawarci ma’aurata 1,500 da s**a amfana da shirin auren gata na jihar da su tab...
09/08/2026

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya shawarci ma’aurata 1,500 da s**a amfana da shirin auren gata na jihar da su tabbatar da zaman lafiya a gidajensu ta hanyar haƙuri da fahimtar juna.

Gwamnan ya yi wannan kira ne yayin da yake jawabi ga ma’auratan, inda ya tunatar da su cewa aure ibada ne, don haka ya kamata su gudanar da rayuwar aurensu bisa koyarwar Alƙur’ani da Sunnar Annabi Muhammad (SAW).

Ya kuma bukaci ma’auratan da su yi adalci, mutunta juna da kuma ƙoƙarin warware matsalolin gidajensu cikin fahimta da haƙuri.

Abba Kabir Yusuf ya ce ya kamata ma’auratan su yi amfani da shawarwari da ilimin da s**a samu yayin zaman horaswa da ba su kafin aure domin gina gidaje masu ɗorewa da cike da fahimtar juna.

Gwamnan ya kuma yi addu’ar Allah Ya sanya albarka a aurensu, Ya ba su ’ya’ya nagari waɗanda za su amfani iyalansu, al’umma da bil’adama baki ɗaya.

Iran ta ce tattaunawar da take yi da Oman kan yadda za a gudanar da zirga-zirgar jiragen ruwa a Mashigar Hormuz na samun...
09/08/2026

Iran ta ce tattaunawar da take yi da Oman kan yadda za a gudanar da zirga-zirgar jiragen ruwa a Mashigar Hormuz na samun ci gaba.

Sai dai wani babban jami’in tsaro a Tehran, Mohammad Bagher Zolghadr, ya bayyana cewa Iran ba za ta amince da sake buɗe mashigar ba matuƙar Amurka ba ta amince da wasu sharudda guda shida da ƙasar ta gindaya ba.

Daga cikin buƙatun Iran akwai sassauta takunkuman tattalin arzikin da aka kakaba mata, biyan diyya kan asarar da aka samu sakamakon yaƙin, da kuma kawo ƙarshen toshe tashoshin jiragen ruwan Iran da Amurka ke yi.

Wasu bayanai daga wani jami’in tsaron Iran na nuna cewa sake buɗe Mashigar Hormuz na da alaƙa kai tsaye da cimma waɗannan buƙatu da Iran ta gabatar.

Tun da farko, Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araqchi, ya bayyana cewa Iran da Oman sun yi kusa sosai da cimma yarjejeniya kan wata sabuwar hanyar gudanar da zirga-zirgar jiragen ruwa ta Mashigar Hormuz.

A wani ci gaban kuma, Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ta zargi Iran da kai harin makami mai linzami kan ɗaya daga cikin jiragen ruwanta na dakon mai.

07/08/2026

“Hon. Sulaiman Ibrahim Kotu bai taba zama Shugaban Jam’iyyar ADC na Kaduna ta Kudu ba, bare ma yayi ikirarin cewa wai ya ajiye kuma ya fita” ~ Hon. Ibrahim Ahmad (Shugaban Matasan Jam’iyyar ADC na Kaduna).

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta gurfanar da wani tsohon jami’inta, Nwaogu Ihechimere Ezeakolam, a gaban Babbar Kotu...
07/08/2026

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta gurfanar da wani tsohon jami’inta, Nwaogu Ihechimere Ezeakolam, a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, bisa zargin kasancewa mamba a ƙungiyar IPOB da gwamnati ta haramta.

An gurfanar da Ezeakolam ne a ranar Alhamis a gaban Mai Shari’a Mohammed Garba Umar, inda gwamnatin tarayya ta gabatar da tuhume-tuhume guda huɗu a kansa.

DSS na zargin tsohon jami’in da bai wa IPOB goyon baya da kayan aiki, da kuma shiga ƙungiyar duk da sanin cewa an haramta ta.

Hukumar ta kuma zarge shi da wallafa saƙonni a shafukan sada zumunta domin ƙarfafa jama’a su mara wa ƙungiyar baya, tana mai cewa hakan ya saɓa wa tanade-tanaden dokar yaƙi da ta’addanci ta shekarar 2022.

Sai dai Ezeakolam ya musanta dukkan tuhume-tuhumen da aka karanta masa a gaban kotu.

Mai shari’ar ya ɗage shari’ar zuwa ranar 29 ga Oktoba domin fara sauraron ƙarar, tare da bayar da umarnin ci gaba da tsare tsohon jami’in a gidan gyaran hali na Kuje har sai an yanke hukunci kan buƙatar belinsa.

Gwamnatin Najeriya ta ayyana IPOB a matsayin ƙungiyar ta’addanci tare da haramta ayyukanta a shekarar 2017.

Rahotannin daga kafafen yaɗa labaran Isra’ila sun ce hukumar leƙen asirin ƙasar, Mossad, ta sallami manyan jami’ai biyu ...
07/08/2026

Rahotannin daga kafafen yaɗa labaran Isra’ila sun ce hukumar leƙen asirin ƙasar, Mossad, ta sallami manyan jami’ai biyu da ake zargi da tsara wani shirin kifar da gwamnatin Iran wanda bai yi nasara ba.

Tashar Channel 12 ta Isra’ila ta ruwaito cewa shugaban Mossad, Roman Goffman, ne ya ɗauki matakin sallamar jami’an biyu.

Rahoton ya ce ɗaya daga cikin jami’an ya jagoranci sashen tattara bayanan sirri na Mossad tun watan Disamban 2015, yayin da ɗayan kuma ke jagorantar sashen da ke kula da harkokin Iran. Sai dai ba a bayyana sunayensu ba.

An ce jami’an biyu sun tsara wani shirin ɓoye da nufin kifar da gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, ta hanyar amfani da ƙungiyoyin Kurdawa da kuma ƙarfafa zanga-zangar gama-gari a ƙasar.

Rahotannin sun ƙara da cewa Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya gabatar da shirin ga Shugaban Amurka, Donald Trump, a wani yunƙuri na shawo kansa ya amince da kai hari kan Iran a watan Maris.

A lokacin da aka tsara shirin, David Barnea ne ke jagorantar Mossad, kafin daga bisani Roman Goffman ya maye gurbinsa a watan Yunin wannan shekara.

Saudiya, Turkiyya da Pakistan sun rattaba hannu kan wata sabuwar yarjejeniyar tsaro da nufin ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da...
07/08/2026

Saudiya, Turkiyya da Pakistan sun rattaba hannu kan wata sabuwar yarjejeniyar tsaro da nufin ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da taimakon juna tsakanin ƙasashen uku.

An sanya hannu kan yarjejeniyar ne a birnin Makka, a wani taro da ya samu halartar Yarima mai jiran gado na Saudiya, Mohammed bin Salman, Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, da Firaministan Pakistan, Shehbaz Sharif.

Ƙarƙashin yarjejeniyar, duk wani hari da aka kai wa ɗaya daga cikin ƙasashen uku za a ɗauke shi a matsayin hari da aka kai wa sauran ƙasashen.

Yarjejeniyar ta zo ne a lokacin da ake ci gaba da samun rikici tsakanin Amurka da Iran, wanda ya shafi tsaron yankin Tekun Fasha tare da haifar da matsaloli ga zirga-zirgar jiragen ruwa a Mashigar Hormuz da kuma Tekun Maliya.

Ana kallon sabon tsarin haɗin gwiwar a matsayin wani mataki na ƙara haɗin kan ƙasashen uku wajen tunkarar ƙalubalen tsaro da ke fuskantar yankin.

Hukumar Raya Kasuwanni ta Jahar Kaduna wato Kaduna Markets Development tareda hadin Guiwar Hukumar da ke Bayar da Izinin...
06/08/2026

Hukumar Raya Kasuwanni ta Jahar Kaduna wato Kaduna Markets Development tareda hadin Guiwar Hukumar da ke Bayar da Izinin mallakar filaye ta Jahar Kaduna (KADGIS) sun gudanar da taro domin fara bayar da takardun mallakar shaguna a Jahar Kaduna wato C o O don kawo karshen rigingimun da ake samu akan mallakar shaguna a fadin Jahar Kaduna.

Tunda farko, Shugaban Hukumar KADGIS Dr. Bashir Garba Ibrahim, ya bayyana wannan tsari na samarwa da masu shaguna takardar mallaka amatsayin abinda zai kawo cigaba wanda yace babu wata Jaha a fadin Kasar nan da aka taba irin wannan tsari sai jihar Kaduna, inda yace wannan abin ayabawa Gwamnan Jihar Kaduna ne Sanata Malam Uba Sani.

📷Abdulmajid Kura

Mahukuntan Kuwait sun soke lasisin makarantar ƴan Iran guda ɗaya tilo da ke ƙasar, tare da bayar da umarnin rufe ta baya...
06/08/2026

Mahukuntan Kuwait sun soke lasisin makarantar ƴan Iran guda ɗaya tilo da ke ƙasar, tare da bayar da umarnin rufe ta bayan rikicin da ya biyo bayan hare-haren Iran a yankin Gabas ta Tsakiya.

Wata majiya daga Ma’aikatar Ilimi ta Kuwait ta tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa an bayar da umarnin rufe makarantar, sai dai ba a bayyana takamaiman dalilin da ya sa aka ɗauki matakin ba.

Kuwait na daga cikin ƙasashen yankin Tekun Fasha da Iran ta kai wa hare-hare a lokacin rikicin, lamarin da aka danganta da kasancewar sojojin Amurka a ƙasar.

Wata takardar Ma’aikatar Ilimi da AFP ta gani ta bayyana cewa ministan ilimi ya yanke shawarar soke lasisin makarantar mai zaman kanta ta Iran tare da rufe ta.

Bisa umarnin, makarantar ba za ta karɓi sababbin ɗalibai a shekarar karatu mai zuwa ba, yayin da aka buƙaci iyaye su mayar da ƴaƴansu zuwa wasu makarantu.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta EFCC da ta gaggauta komawa kotu domin ...
06/08/2026

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta EFCC da ta gaggauta komawa kotu domin neman soke umarnin da ya ba ta damar rufe asusun gwamnatin Jahar Osun.

Tinubu ya bayyana cewa matakin ya ba shi mamaki, musamman saboda lokacin da aka ɗauke shi, jahar na dab da gudanar da zaɓen gwamna.

Shugaban ya ce bai kamata a ɗauki wani mataki da zai sa a zargi hukumomin gwamnatin tarayya da yin katsalandan a zaɓen Osun ba.

Ya jaddada cewa tun bayan hawansa mulki, ya guji tsoma baki cikin ayyukan EFCC da sauran hukumomin bincike domin su gudanar da aikinsu cikin 'yanci.

Sai dai Tinubu ya ce duk da cewa bai samu cikakken bayani kan dalilin rufe asusun ba, ya umarci EFCC da ta nemi soke umarnin kotun tare da dakatar da duk wani mataki da ta ɗauka kan gwamnatin Osun.

EFCC ta samu umarnin kotu na rufe asusun gwamnatin Osun ne a ranar 5 ga Agustan 2026, yayin da hukumar ba ta fitar da ƙarin bayani kan matakin ba har zuwa lokacin wallafa rahoton.

Address

5 Yakubu Gowon Way
Kaduna
800266

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Freedom Radio Kaduna posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Freedom Radio Kaduna:

Shortcuts

Share