Freedom Radio Kaduna

Freedom Radio Kaduna Freedom Radio 92.9 Kaduna mun himmatu wajen isar da sahihan labarai, shirye-shiryen nishaɗi, faɗakarwa, ilimantarwa, tare da bayyana ra'ayin al'umma.

Muryar Jama'a! guda cikin jerin gidajen Rediyo na Freedom Radio Group, Freedom Radio Nigeria

06/06/2026

Yadda 'yan kasuwar bushashshen kifi dake yankin Mile 12 a Jihar Legas s**a wayi gari gwamnatin Jihar ta rushe musu wuraren sana'ar su da shagunan su.

Mubarak Abdullahi Muhammad, wanda dan asalin jihar Kebbi ne, na daya daga cikin wadanda abin ya shafa, ga kuma yadda tattaunawar mu dashi ta kasance.

Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Bauchi ta tabbatar da mutuwar mutane bakwai sakamakon wani sabon rikici da ya ɓarke tsakani...
05/06/2026

Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Bauchi ta tabbatar da mutuwar mutane bakwai sakamakon wani sabon rikici da ya ɓarke tsakanin manoma da makiyaya a karamar hukumar Darazo ta jihar.

Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Ƙasa (NHIA) reshen jihar Kaduna ta gudanar da taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki ...
04/06/2026

Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Ƙasa (NHIA) reshen jihar Kaduna ta gudanar da taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki na ɓangaren kamfanoni masu zaman kansu da taron ya gudana a Yau a Kaduna.

Shugaban ofishin Hukumar reshen jihar Kaduna, Aliyu Dodo Lawal, ya bayyana cewa yawan halartar taron na nuna muhimmancin wayar da kai da hukumar ke yi kan shirye-shiryen inshorar lafiya.

Ya ce dokar NHIA ta 2022 ta mayar da inshorar lafiya dole ga hukumomin gwamnati da ma kamfanoni masu zaman kansu.

Ya ce ana buƙatar ma’aikatu da hukumomin gwamnati (MDAs) su yi rijistar ma’aikata, sannan kamfanonin da ke neman kwangila dole su gabatar da sahihin takardar inshorar lafiya ta NHIA.

Ya ƙara da cewa za a ƙaddamar da tsarin yanar gizo wato dijital domin tabbatar da sahihancin takardu cikin sauƙi da kuma gaskiya da adalci.

Shugaban Hukumar na shiyyar Arewa maso Yamma, Ibrahim Gwamba, ya ce shirin na da nufin tabbatar da inshorar lafiya ga kowa a Najeriya.

Ya ce kusan kashi 97 cikin 100 na ma’aikatan gwamnatin tarayya sun shiga tsarin, tare da jaddada ƙudirin gwamnati na tabbatar da cikakken bin doka.

An gabatar da kasidu biyu a wajen taron kan fa’idojin inshorar lafiya da hanyoyin ƙara yawan masu shiga tsarin.

Mahalarta taron sun kuma bayar da shawarwari, inda aka bayyana cewa lafiya haƙƙi ne ba gata ba.

Wannan shiri na daga cikin ƙoƙarin NHIA na faɗaɗa samun ingantaccen kiwon lafiya mai sauki ga ‘yan Najeriya.

The National Health Insurance Authority (NHIA) Kaduna State Office has organized a stakeholders’ engagement meeting for ...
04/06/2026

The National Health Insurance Authority (NHIA) Kaduna State Office has organized a stakeholders’ engagement meeting for the organized private sector at the Kaduna ICT Hub, Kanta Road, Kaduna today.

The State Coordinator, Aliyu Dodo Lawal, said the large turnout shows the agency’s commitment to sensitizing stakeholders on health insurance programmes.

He explained that the NHIA Act 2022 makes health insurance mandatory for public and private institutions.
He noted that Ministries, Departments and Agencies (MDAs) are required to enroll staff, while companies involved in public procurement must present valid NHIA Health Insurance Certificates.

He added that a digital platform will soon be introduced to verify certificates and improve transparency.
The Zonal Director, North-West, Ibrahim Gwamba, said the scheme is aimed at achieving universal health coverage in Nigeria.

He added that about 97% of federal workers are already enrolled, and emphasized government commitment to full compliance of the policy.

Two papers were presented on the benefits of health insurance and strategies for increasing enrollment. Participants also contributed suggestions, while stakeholders described healthcare as a right, not a privilege.

The engagement is part of NHIA’s efforts to expand access to affordable and quality healthcare.

Majalisar Wakilan Amurka ta amince da wani ƙuduri da ke neman Shugaba Donald Trump ya janye sojojin Amurka daga yaƙin da...
04/06/2026

Majalisar Wakilan Amurka ta amince da wani ƙuduri da ke neman Shugaba Donald Trump ya janye sojojin Amurka daga yaƙin da ake yi da Iran, ko kuma ya nemi sahalewar Majalisar Dokoki kafin ci gaba da duk wani matakin soja.

A ƙuri'ar da aka kaɗa, wasu ƴan majalisa huɗu daga jam'iyyar Republican sun haɗa kai da ƴan jam'iyyar Democrat wajen mara wa ƙudurin baya, lamarin da ya nuna ƙarin rashin jituwa a cikin jam'iyyar shugaban ƙasar kan manufofinsa game da Iran.

Yanzu dai ana sa ran ƙudurin zai wuce zuwa Majalisar Dattawa domin ci gaba da nazari.

Sai dai masu sharhi na ganin ƙudurin na fuskantar ƙalubale, kasancewar shugaban ƙasa na da ikon yin amfani da kujerar na-ƙi (veto) domin hana aiwatar da duk wani mataki da yake ganin zai tauye ikonsa.

Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da ake ƙara samun muryoyin adawa da yadda Trump ke tafiyar da rikicin Iran, ciki har da daga wasu mambobin jam'iyyarsa ta Republican.

04/06/2026

AN TASHI LAFIYA 04/06/2026.
Tare da: Samira Saad Zakirai.

03/06/2026

Tsarabar Sallah | Freedom Radio Kaduna .

Ina ‘Yan Kaduna Ta Tsakiya…Ku Zo Mu Tattauna👇
03/06/2026

Ina ‘Yan Kaduna Ta Tsakiya…Ku Zo Mu Tattauna👇

03/06/2026

Rundunar 'Yan Sandan Najeriya reshen jihar Yobe sun gano wani wurin kera makamai a Potiskum.

Address

5 Yakubu Gowon Way
Kaduna
800266

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Freedom Radio Kaduna posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Freedom Radio Kaduna:

Share