Naijalite Hausa

Naijalite Hausa Naijalite Hausa, Jarida Ce Na Jihar Neja An kafata Ne Domin Kawu Labarai, Na Cikin Jihar Neja Dama Sauran Jahohi Nijeriya Harma Duniya Baki Daya

DA DUMI-DUMI: Ministan Tsaron Ghana Dr. Edward Omane Boamah da Ministan Muhalli, Ibrahim Murtala Muhammed sun rasa rayuk...
06/08/2025

DA DUMI-DUMI: Ministan Tsaron Ghana Dr. Edward Omane Boamah da Ministan Muhalli, Ibrahim Murtala Muhammed sun rasa rayukansu a wani hatsarin jirgin sama mai saukar ungulu na sojojin Ghana a kan hanyarsa ta zuwa Obuasi.

Rahoton na cewa helikwaftan ƙirar Z-9 na kan hanyar zuwa Obuasi ne da safiyar wannan yini na Laraba ɗauke da fasinjoji biyar da matuƙan jirgin uku, inda kwatsam sai aka daina ji daga matuƙa jirgin.

Wurin da haɗarin ya faɗo ba cikin yankin Ashanti ne na ƙasar, kuma akwai fargabar dukkan waɗanda ke cikin helikwaftan sun ƙone ƙurmus.

MATSAYAR NEJA KAN ƳAN TA'ADDA:Ba za mu yi wata sulhu da 'yan bindiga ba. Sulhu ɗinmu zai kasance ne kawai tsakanin manom...
06/08/2025

MATSAYAR NEJA KAN ƳAN TA'ADDA:

Ba za mu yi wata sulhu da 'yan bindiga ba. Sulhu ɗinmu zai kasance ne kawai tsakanin manoma da makiyaya. Idan wata jiha k**ar Kaduna ta yanke shawarar yin sulhu da 'yan bindiga, to su gina katanga tsakaninsu da jiharmu ta Neja. Idan waɗancan 'yan bindigar s**a ketara zuwa Neja su sace shanunmu, za mu bi su har Kaduna, mu karɓo dabbobinmu da karfi da iko. Inji— Gwamna Umar Bago

Allah ya sa a raƙe su bilhaƙƙi

Comrade-Zakari Y Adamu Kontagora

YANZU-YANZU: Jami'an tsaron ƙasar mu Najeriya, sunyi nasarar cafke wani matashi mai kaima 'yan boko haram manfetur aciki...
06/08/2025

YANZU-YANZU: Jami'an tsaron ƙasar mu Najeriya, sunyi nasarar cafke wani matashi mai kaima 'yan boko haram manfetur acikin kwalbar lamun kwalba, mai suna Amadu Muhammad Dogo" acikin Maiduguri-Gamboru-Ngala dake jahar Borno a arewa maso gabashin Najeriya.

Kuyi sharing! wannan rubutu domin duniya susan halinn da Arewacin Najeriya take ciki.!

Daga Suleiman Omar Farouk

YAN BINDIGA SUN SACE MUTUM 20 A WANI SABON HARI DA S**A KAI A ZAMFARADaga: Abdulmajid Idris Gunna A kalla mata da ‘yan m...
05/08/2025

YAN BINDIGA SUN SACE MUTUM 20 A WANI SABON HARI DA S**A KAI A ZAMFARA
Daga: Abdulmajid Idris Gunna

A kalla mata da ‘yan mata 20 ne ‘yan bindiga s**a sace a garin Moriki da ke karamar hukumar Zurmi a jihar Zamfara, yayin da suke neman itace a wajen gari a ranar Asabar.

Wani mazaunin yankin, Sufyanu Moriki, ya tabbatar da faruwar lamarin ga gidan talabijin na Channels, yana mai cewa har yanzu masu garkuwar ba su nemi kudin fansa ba.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara Yazid Abubakar ya ce hukumar su ba ta samu bayani kan lamarin ba tukuna.

Rahotanni sun bayyana cewa hadin gwiwar ‘yan ta’adda da mayaka ma su da’awar jihadi na kungiyar Lakurawa a yankin na kara dagula lamarin tsaro a Arewacin Najeriya.

An tsinci gawarwakin mutane uku sun mutu sak**akon ƙishirwa a kusa da rijiyar Achigour, kan hanyar Agadez–Dirkou. Daya d...
05/08/2025

An tsinci gawarwakin mutane uku sun mutu sak**akon ƙishirwa a kusa da rijiyar Achigour, kan hanyar Agadez–Dirkou. Daya daga cikinsu dan Nijar ne, yana dauke da kati. Sauran biyun ba su da takardu.
Ana rokon jama'a su yada saƙon don iyalansu su gane su.

05/08/2025

An tsinci gawarwakin mutane uku sun mutu sak**akon ƙishirwa a kusa da rijiyar Achigour, kan hanyar Agadez–Dirkou. Daya daga cikinsu dan Nijar ne, yana dauke da kati. Sauran biyun ba su da takardu.
Ana rokon jama'a su yada saƙon don iyalansu su gane su.

Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammad Sanusi II, PhD, CON, ya kai ziyara Gidan Marigayi Tsohon Shugaban Ƙasa, Janar ...
05/08/2025

Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammad Sanusi II, PhD, CON, ya kai ziyara Gidan Marigayi Tsohon Shugaban Ƙasa, Janar Muhammadu Buhari, dake Kaduna, domin yi wa iyalansa ta’aziyya.

Talata, 5 ga Agusta, 2025.

YANZU-YANZU: Bello Turji ya ƙuduri niyyar ajiye mak**ai kuma ya saki mutane 32 - Asadus-Sunnah Kasurgumin jagoran ƴan ta...
05/08/2025

YANZU-YANZU: Bello Turji ya ƙuduri niyyar ajiye mak**ai kuma ya saki mutane 32 - Asadus-Sunnah

Kasurgumin jagoran ƴan ta’adda a jihar Zamfara, Bello Turji, ya saki mutane 32 da ya yi garkuwa da su tare da amincewa da ya dena kaiwa manoma hari, bayan ganawa da malaman addinin Musulunci a dajin Fakai, karamar hukumar Shinkafi.

Jaridar Premium Times ta rawaito cewa Malamin addini Musulunci, Musa Yusuf, wanda ya fi shahara da Asadus-Sunnah ne ya bayyana hakan a wani taron addini a Kaduna, inda ya ce al’ummar Shinkafi ne s**a bukaci a shiga tsakani domin su samu damar komawa gonakinsu.

A cewar Yusuf, ganawar ta gudana sau uku a watan Yuli, kuma Turji da wasu fitattun mayaka k**ar Dan Bakkolo, Black, Kanawa da Malam Ila sun amince da yarjejeniyar zaman lafiya, ciki har da ajiye mak**ai da barin manoma su koma gonaki ba tare da fargaba ba.

Yusuf ya ce wadanda aka sako sun hada da mata da yara, kuma sun shafe kusan watanni hudu a hannun Turji.

Wasu daga cikinsu sun haifi yara a daji, yayin da daya daga cikinsu ta kamu da cizon maciji.

Ya ce tun bayan yarjejeniyar, zaman lafiya ya fara dawowa a yankin Shinkafi, inda manoma ke ci gaba da aikin gona cikin kwanciyar hankali.

Malamin ya gargadi wasu malamai da ke s**ar Turji a kafafen sada zumunta da su daina, yana mai cewa hakan na iya tayar da zaune tsaye.

Ya yabawa Shugaba Bola Tinubu, Nuhu Ribadu, Gwamna Dauda Lawal da Sanata Shehu Buba saboda goyon bayan hanyar zaman lafiya wajen magance matsalar tsaro a Zamfara.

MÙĢÙN ÑÙFI: Ya Boye Buhunan Masara Sama Da Dubu Uku Saboda Idan Farashin Ta Ya Haura Ya Fitar Ya Siyar, Sai Ga Shi Masar...
05/08/2025

MÙĢÙN ÑÙFI: Ya Boye Buhunan Masara Sama Da Dubu Uku Saboda Idan Farashin Ta Ya Haura Ya Fitar Ya Siyar, Sai Ga Shi Masarar Ta Rubè, Kamar Yadda Jaridar Rariya Ta Ruwaito.

Me za ku ce?

Abdulmajid Idris Gunna

04/08/2025

SHAFIN NAIJALITE HAUSA
ZATA DAUKI SABBIN
WAKILAI REPORTERS
MATA DA ZAMA MUTUM
HUDU

04/08/2025

Wannan shine Bidiyon matar da jami'an tsaron C-Watch na Malumfashi s**a k**a jiya tana ɗauke da kwalkwaron magazin ɗin Bindiga uku tare da kayan sojoji da jaket da wasu ababe.

Matashiya 'Yar Asalin Jihar Yobe, Nafisa Abdullahi Ta Lashe Gasar Turanci Ta Duniya Da Aka Gudanar A Birnin LandanNafisa...
04/08/2025

Matashiya 'Yar Asalin Jihar Yobe, Nafisa Abdullahi Ta Lashe Gasar Turanci Ta Duniya Da Aka Gudanar A Birnin Landan

Nafisa Abdullah Aminu, yarinya ‘yar shekaru 17 daga jihar Yobe, ta samu babban nasara a gasar ƙasa da ƙasa ta harshen Turanci da aka gudanar a London, Birtaniya, ƙarƙashin TeenEagle Global Finals 2025.

Nafisa, wadda ke karatu a Nigerian Tulip International College (NTIC), Yobe, ta fice daga cikin fiye da ɗalibai 20,000 daga ƙasashe 69 – ciki har da waɗanda harshen Turanci ke matsayin na uwa-uba a wurinsu.

Wannan gagarumar nasara da ta samu ana kallonta a matsayin abin alfahari ga Najeriya da nahiyar Afrika gaba ɗaya, duba da asalin jihar da ta fito wadda ke fama da ƙalubale a harkar ilimi da tsaro.

A sak**akon haka, hukumomi da malamai a jihar Yobe sun nuna farin ciki da wannan nasara, suna fatan za ta zama abin ƙarfafa guiwa ga sauran matasa domin yin fice ta hanyar ilimi da ƙoƙari.

Wane fata zaku yi mata?

Address

Yakila Hanyan Zuwa Tegina Kusa Da Masallacin Juma'a Cikin Garin Yakila Gunna
Kagara

Telephone

+2348084664424

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Naijalite Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Naijalite Hausa:

Share