14/01/2026
DA DUMI DUMI: Makusantan Sheikh Sani Khalifa Zaria Sun Maka Rundunar Sojin Najeriya A Kotu Kan Tsare Malamin Tsawon Wata Ɗaya Ba Tare Da Hukunci Ba
DAGA Shafin Tijjaniya Online
___________________________________________
Makusantan Sheikh Sani Khalifa Zaria sun ɗauki matakin shari’a ta hanyar maka Rundunar Sojin Najeriya a kotu, bisa zargin tsare malamin tsawon wata guda ba tare da gabatar da shi gaban kotu ko yanke masa hukunci ba.
Rahotannin da muka samu sun nuna cewa ‘yan uwa da magoya bayan malamin sun shigar da ƙarar ne domin neman adalci da kare haƙƙinsa na ɗan Adam, inda s**a bayyana cewa tsare Sheikh Sani Khalifa na tsawon wannan lokaci ya sabawa ka’idojin doka da kundin tsarin mulkin ƙasa.
Haka kuma, kwararrun lauyoyi masu rajin kare haƙƙin bil’adama sun haɗa kai domin jagorantar shari’ar, da nufin tabbatar da cewa an bi doka da oda, tare da kare mutuncin da martabar malamin.
Makusantan Sheikh ɗin sun jaddada cewa ba sa adawa da doka, amma suna buƙatar a bi dukkan hanyoyin shari’a bisa gaskiya da adalci, ba tare da zalunci, take haƙƙi ko bata suna ba.
A cewarsu, idan akwai laifi, to doka ta yi aikinta. Amma idan babu, wajibi ne a sako malamin tare da ba shi haƙƙinsa kamar yadda doka ta tanada.
Za mu ci gaba da bibiyar wannan lamari tare da kawo muku duk wani sabon bayani da zarar ya fito a hukumance.
Rahoton Rahma Abdulmajid