G7 Daily Reports

G7 Daily Reports Stay ahead with the latest on Nigerian politics, trending stories, and daily happenings.

G7 Daily Reports: Your trusted source for timely updates and sharp insights..!

17/04/2026

Abu Aslam...

DA DUMI DUMI:BABBAR KOTU A KANO TAYI WATSI DA TUHUMAR CIN HANCI DA RASHAWA DA AKEYI YIWA TSOHON KWAMISHINA MURTALA GARO,...
14/04/2026

DA DUMI DUMI:

BABBAR KOTU A KANO TAYI WATSI DA TUHUMAR CIN HANCI DA RASHAWA DA AKEYI YIWA TSOHON KWAMISHINA MURTALA GARO, SAKAMAKON RASHIN BIN KA'IDAR BINCIKE YADDA YA KAMATA.

~SAHARA REPORTERS

DA DUMI DUMI: Kungiyar G7 Business Communty ta dakatar da duk wasu al'amura da s**a shafi Jam'iyyar APC mai mulki.Sanarw...
13/04/2026

DA DUMI DUMI:
Kungiyar G7 Business Communty ta dakatar da duk wasu al'amura da s**a shafi Jam'iyyar APC mai mulki.
Sanarwar ta fito daga bakin babban Daraktan kungiyar Hon. Ibrahim Khalil Ahmad (BABAHTEX), wanda ya bayyana hakan a wani faifan video daya saki a shafinsa na Fezbuk a safiyar yau litinin. Duk da bai bayyana cikakken dalilin faruwar hakan ba, ya bayyana cewa kowane lokaci zasu iya sanar da matsayarsu ta karshe akan wannan dambarwa. Saidai a binciken da G7 Daily Reports tayi mun samu bayani ta bakin daya daga cikin jagororin kungiyar cewa, matakin ya biyo bayan halin ko in kula da wofintarwa da kungiyar take fuskanta daga iyayenta, da masu ruwa tsaki na jam'iyyar APC.

DA DUMI DUMI:Gwamnan Kano Engr. Abba Kabir Yusuf yanzu haka yana ganawa da shugabannin kananan hukumomin jihar da mataim...
12/04/2026

DA DUMI DUMI:
Gwamnan Kano Engr. Abba Kabir Yusuf yanzu haka yana ganawa da shugabannin kananan hukumomin jihar da mataimakansu da sakatarorinsu da shugabannin majalisar kansiloli.

Hotuna daga: Salisu Yahaya Hotoro.

DA ƊUMI-ƊUMI:Bayan awanni kaɗan da sakin sa daga hannun DSS, mai magana da yawun Gwamnan Kano, Sanusi Bature, ya watsar ...
12/04/2026

DA ƊUMI-ƊUMI:

Bayan awanni kaɗan da sakin sa daga hannun DSS, mai magana da yawun Gwamnan Kano, Sanusi Bature, ya watsar da jar hularsa da aka saba ganin sa da ita, ya kuma saka sabuwar hular Omologo ta shugaba Asiwaju Bola Ahmad Tinubu.

Wannan mataki na zuwa ne bayan wata ƙara da ƴan Kwankwasiyya s**a shigar kan zargin cin zarafi da ɓatanci a shafukan sada zumunta.

Jam'iyyar ADC tana gudanar da taron fitarda sababbin shugabanninta a Kano.~G7 Daily Reports
12/04/2026

Jam'iyyar ADC tana gudanar da taron fitarda sababbin shugabanninta a Kano.

~G7 Daily Reports

Mutane 56 sun rasu yayin da jirgin yakin sojin Nijeriya ya saki bama-bamai bisa kuskure a BornoAƙalla mutane 56, galibin...
12/04/2026

Mutane 56 sun rasu yayin da jirgin yakin sojin Nijeriya ya saki bama-bamai bisa kuskure a Borno

Aƙalla mutane 56, galibinsu ’yan kasuwa, ake fargabar sun rasa rayukansu yayin da wasu 14 s**a jikkata sakamakon wani harin sama da aka kai a wata kasuwa ta mako-mako da ke kan iyakar jihohin Borno da Yobe.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa lamarin ya faru ne a kasuwar Jilli, wadda ke tsakanin ƙananan hukumomin Gubio a Jihar Borno da Geidam a Jihar Yobe, a ranar Asabar.

Rahotanni sun nuna cewa an kai harin ne a yayin wani samame na sojoji da ke farautar ’yan ta’addan Boko Haram. Sai dai an ce harin ya kauce daga inda aka nufa, ya afkawa jama’ar da ke gudanar da harkokinsu a kasuwar.

Kasuwar Jilli na jawo ’yan kasuwa da masu saye daga yankuna da dama, ciki har da Gubio, Chiweram da Benisheikh a Borno, da kuma Gurokayeya da Geidam a Yobe.

Wasu majiyoyi sun ce jirgin yaƙi da ya kai harin na bin diddigin wasu da ake zargi ’yan tada ƙayar baya ne da s**a je kasuwar domin karɓar haraji daga hannun ’yan kasuwa da kuma samun kayan abinci. Amma harin ya kasa cimma manufarsa.

Wani ganau ya bayyana cewa akalla gawarwaki 56 aka tabbatar, yayin da wasu mutum 14 ke karɓar magani a Asibitin Kwararru da ke Geidam a Jihar Yobe.

Har zuwa lokacin kammala wannan rahoto, rundunar sojin saman Nijeriya ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance dangane da lamarin ba.

AKALLA KASO 90 CIKIN DARI NA WADANDA S**A HALARCI TATTAUNAWA AKAN MAS'ALAR MATAIMAKIN GWAMNA SUN GOYI BAYAN GARO.Tsohon ...
12/04/2026

AKALLA KASO 90 CIKIN DARI NA WADANDA S**A HALARCI TATTAUNAWA AKAN MAS'ALAR MATAIMAKIN GWAMNA SUN GOYI BAYAN GARO.

Tsohon shugaban jam'iyyar APC na Nijeriya Abdullahi Umar Ganduje, da tsohon shugaban masu rinjaye a majalisar wakilai Alhassan Ado Doguwa, tare da wasu manyan 'yan siyasa sun goyi bayan Murtala Sule Garo ya zama mataimakin gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf.

Hakan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da Doguwa ya fitar a ranar Lahadi.

A cewar sa, an cimma matsayar ne bayan tattaunawa tsakanin jagorori da sauran masu ruwa da tsaki na jam'iyyar APC.

Ya kuma ce kaso 90 na wadanda s**a halarci zaman tattaunawar sun goyi bayan Murtala Sule Garo, yana mai kira ga gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya duba lamarin, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

11/04/2026

I got over 200 reactions on my posts last week! Thanks everyone for your support! 🎉

11/04/2026
11/09/2024

Address

Zoo Road
Kano

Telephone

+2347069380068

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when G7 Daily Reports posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to G7 Daily Reports:

Share