Juma concept

Juma concept An bude shafin Juma concept ne ranar 20 ga watan mayu shakara ta 2025 domin ya'da shirye shiryen ta da harshen Hausa A Facebook , TikTok ,YouTube da Instagram.

YANZU-YANZU: Mun kammala dukkan wata shiri na daukan mataki kan Najeriya.Sa'o'i kadan bayan Trump ya yi barazanar daukar...
02/11/2025

YANZU-YANZU: Mun kammala dukkan wata shiri na daukan mataki kan Najeriya.

Sa'o'i kadan bayan Trump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya, sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth ya ce ma'aikatar tsaro ta Pentago ta shirya domin aiwatar da wannan umurni muddin Abuja ba ta dauki matakin kawo karshen kisan Kiristoci da masu tsattsauran ra'ayin Islama ke yi a kasar ba.

Natasha Ta Gayyaci Akpabio Zuwa Bikin Kaddamar da Ayyuka a KogiDangantaka tsakanin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan (PDP, ...
31/10/2025

Natasha Ta Gayyaci Akpabio Zuwa Bikin Kaddamar da Ayyuka a Kogi

Dangantaka tsakanin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan (PDP, Kogi ta Tsakiya) da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ta fara samun sauƙi bayan Akpoti-Uduaghan ta aika da gayyata ga Akpabio domin halartar bikin kaddamar da ayyuka a yankinta.

Gayyatar, wacce aka rubuta da hannunta, ta kuma haɗa da sauran sanatoci, kuma an karanta ta a zauren majalisar yayin zaman ranar Alhamis da Akpabio kansa ya karanta.

A cewar wasikar, bikin zai gudana ne a ranar Lahadi a Ihima, Jihar Kogi, domin bikin cika shekaru biyu da Akpoti-Uduaghan ta yi a majalisar dattawa.

“A yayin bikin cika shekaru biyu a matsayin Sanata mai wakiltar al’ummata, ina gayyatar sanatoci abokaina da su zo bikin kaddamar da ayyuka a Jihar Kogi,” in ji wasikar.

An bayyana Plot 101, Jimoh Akpoti Street, Ihima, Okene a matsayin wurin taro, inda aka ba da shawarar cewa sanatocin da ke tafiya ta jirgi su sauka a Obajana Airstrip kafin su ci gaba zuwa Ihima ta hanya.

Bayan karanta gayyatar, Akpabio ya taya ta murna a gaba da kowa da cewa:

“Ina taya ki murna a gaba.”

Wannan mataki na nuna sabon yanayi na sulhu bayan rikicin da ya barke a watan Fabrairu kan rabon kujeru a majalisar, wanda ya jawo dakatar da Sanata Akpoti-Uduaghan na tsawon watanni shida daga aiki a ranar 6 ga Maris.

Tun bayan dawowarta a ranar 24 ga Satumba, Sanatar ta fara sake shiga hulɗa da Akpabio a zauren majalisa, ciki har da bayar da gudunmawa a muhawara da dokoki. Amma wannan gayyatar ce ta fi nuna mataki kai tsaye na sulhu da shugabancin majalisar.

DA DUMI-DUMI: Rahotanni daga ƙasar Tanzania na nuna cewa dubban yan kasar sun k**a hanyar zuwa fadar gwamnatin kasar don...
31/10/2025

DA DUMI-DUMI: Rahotanni daga ƙasar Tanzania na nuna cewa dubban yan kasar sun k**a hanyar zuwa fadar gwamnatin kasar don ganawa ido da ido tsakanin su da shugaba Samia Saluhu inda zasu roƙe tayi murabus cikin lalama ko da tsiya.

HOTUNA: Yanda dandazon ɗaruruwan sojoji su ka yi wa Janar Christopher Musa rakiya yayin bankwana da barikin soja na Moga...
31/10/2025

HOTUNA: Yanda dandazon ɗaruruwan sojoji su ka yi wa Janar Christopher Musa rakiya yayin bankwana da barikin soja na Mogadishu Cantonment wanda ke unguwar Asokoro a Abuja bayan rantsar da sabon Babban Hafsan Hafsoshin tsaron Najeriya a jiya Alhamis.

Ziyarar tsoffin ‘yan wasan Barcelona shaida ce ta samuwar tsaro da zaman lafiya - Ministan Tsaron NijeriyaMinistan tsaro...
25/10/2025

Ziyarar tsoffin ‘yan wasan Barcelona shaida ce ta samuwar tsaro da zaman lafiya - Ministan Tsaron Nijeriya

Ministan tsaron Nijeriya, Dr. Bello Muhammad Matawalle, ya bayyana ziyarar tsoffin ‘yan wasan ƙungiyar kwallon kafa ta Barcelona zuwa Nijeriya a matsayin tabbacin dawowar zaman lafiya, tsaro da kwanciyar hankali a Nijeriya.

A wata sanarwa da mataimakinsa na musamman kan yaɗa labarai, Ahmad Dan-Wudil, ya fitar a Abuja ranar Juma’a, Matawalle ya ce ziyarar ta nuna yadda ƙasashen duniya ke sake samun kwarin gwiwa kan ƙoƙarin da gwamnatin Nijeriya ke yi wajen magance matsalar tsaro.

A cewar Matawalle, ziyarar tsoffin ‘yan wasan Barcelona zuwa Nijeriya hujja ce ta ci-gaban da ƙasarmu ta samu wajen farfaɗo da tsaro da zaman lafiya.

Hakazalika, ya ƙara da cewa wannan lamari ya nuna Nijeriya ta zama kasar da ke jan hankalin ƙasashen duniya sak**akon jajircewar jami’ai da hukumomin tsaron kasar.

Matawalle ya bayyana wasan sada zumunci da tsoffin ‘yan wasan Barcelona za su buga da tsoffin taurarin ‘yan wasan Afirka a ranar Asabar, 25 ga watan Oktoba 2025, a filin wasa na Moshood Abiola da ke Abuja, a matsayin nasara ga gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu wajen tabbatar da zaman lafiya da samuwar yanayi mai kyau domin gudanar da wasannin kasa da kasa.

Daga karshe, Matawalle ya kuma yi wa tawagar tsoffin ‘yan wasan maraba a madadin gwamnatin Nijeriya da ma ‘yan Nijeriya, da fatan natsuwa da nishadi a lokacin da za su shafe a Nijeriya.

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaban Jam'iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas Ya Tsere Don Gudun Karɓar Sammacin Kotu - Bar...
25/10/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaban Jam'iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas Ya Tsere Don Gudun Karɓar Sammacin Kotu - Barrister Badamasi Gandu

‎‎Babbar Kotu a jihar Kano ta aike wa da shugaban jam'iyyar APCn jihar Kano Prince Abdullahi Abbas da sammaci amma ya tsere ya ƙi karɓa, wannan mataki na kotun na zuwa ne bayan da wasu ƴan jam'iyyar APCn s**a kai ƙara gabanta bisa kora da shugaban jam'iyyar ya yi musu.

‎Barrister Badamasi Sulaiman Gandu ya bayyanawa manema labarai yadda al'amarin ya kasance inda ya ce Shugaban Jam'iyyar APC Abdullahi Abbas ya tsere Bayan da s**a kai masa sammacin kotu don jin ba'asin korar da ya yi wa wasu ƴan APCn jihar saboda suna faɗar gaskiya idan an yi rashin daidai a jam'iyyar tasu kasancewarsu ƴan ƙasa nagari.

‎Barrister Badamasi ya ƙara da cewa za su koma Kotu domin roƙon ta ba su dama su kafe sammacin a gaban ofishin jam'iyyar ta APC.

Me za ku ce?

Gwamnatin Kano ta janye dokar tsaftar muhalli ta watan Oktoba Ma'aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi ta jihar Kano ta sanar...
25/10/2025

Gwamnatin Kano ta janye dokar tsaftar muhalli ta watan Oktoba

Ma'aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi ta jihar Kano ta sanar da janye dokar tsaftar muhalli ta wata-wata, a wannan wata na Oktoba.

Daraktar Yaɗa Labarai ta ma'aikatar, Maryam Abdulkadir ta fitar da sanarwar a yammacin yau Juma'a.

Ya ce Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi Dakta Dahir M Hashim ne ya bada umarnin januewar saboda wasan kalankuwa da za a kaddamar a gobe Asabar.

A cewar sanarwar, Kwamishinan ya ce za a samu mahalrta bikin wasannin daga sassa daban-daban na ƙasa, inda ya ce ya k**ata a baiwa al'umma dama su yi zirga-zirga.

Majalisar Tarayya na nazarin ƙirƙirar sababbin jihohi 55 da ƙananan hukumomi 278Majalisar Tarayya ta fara tattaunawa kan...
24/10/2025

Majalisar Tarayya na nazarin ƙirƙirar sababbin jihohi 55 da ƙananan hukumomi 278

Majalisar Tarayya ta fara tattaunawa kan sabon kudiri na gyaran kundin tsarin mulki wanda zai iya kaiwa ga ƙirƙirar sababbin jihohi 55 da ƙananan hukumomi 278 a faɗin ƙasar.

Jaridar PUNCH ta rawaito cewa Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, wanda ke jagorantar kwamitin sake duba kundin tsarin mulki, ya bayyana haka a lokacin wani taron kwamitocin Majalisar Dattawa da ta Wakilai a Legas.

Barau ya ce majalisar ta shafe shekaru biyu tana gudanar da tattaunawa da al’umma da masu ruwa da tsaki, kuma yanzu an tattara kudiri 69, ciki har da buƙatun ƙirƙirar jihohi da ƙananan hukumomi da gyaran iyakoki.

Ya bayyana cewa burin su ne a mika farkon gyare-gyaren kundin tsarin mulki ga majalisun dokokin jihohi kafin ƙarshen shekara, tare da kira ga ‘yan majalisa da su yi aiki da kishin ƙasa da haɗin kai.

Wannan sabon yunkuri na zuwa ne bayan yunkuri da dama da s**a gaza a baya saboda rashin jituwa tsakanin jihohi da ra’ayoyi na siyasa, duk da cewa wasu gyare-gyare k**ar ’yancin kuɗi ga majalisun jihohi da bangaren shari’a sun samu nasara.

DA ƊUMI-ƊUMI: Tinubu Ya Sauke Janar Christopher Musa Daga Mukaminsa Na CDSShugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sauke Jan...
24/10/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Tinubu Ya Sauke Janar Christopher Musa Daga Mukaminsa Na CDS

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sauke Janar Christopher Gwabin Musa daga mukaminsa na Babban Hafsan Tsaron Najeriya (Chief of Defence Staff - CDS).

Rahotanni sun tabbatar da cewa Shugaban Ƙasar ya maye gurbinsa da Janar Olufemi Oluyede, wanda zai karɓi ragamar rundunar tsaro ta ƙasa nan take.

Jiga-jigan PDP a Arewa sun amince da Kabiru Turaki a matsayin ɗan takarar shugabancin jam’iyyar na ƙasa     Shugabanni d...
24/10/2025

Jiga-jigan PDP a Arewa sun amince da Kabiru Turaki a matsayin ɗan takarar shugabancin jam’iyyar na ƙasa

Shugabanni da jiga-jigan jam’iyyar PDP na yankin Arewa sun amince da Kabiru Turaki, tsohon ministan ayyuka na musamman da harkokin gwamnati a matsayin ɗan takarar shugabancin jam’iyyar a matakin ƙasa.

Jiga-jigan PDP na Arewa sun amince da Turaki ne a wani taro da s**a gudanar a daren Laraba a birnin Abuja.

Cikin manyan shugabannin PDP na Arewa da s**a halarci taron akwai Bala Mohammed, gwamnan Bauchi; Caleb Mutfwang na Plateau; Ahmadu Fintiri na Adamawa; Dauda Lawal na Zamfara; da kuma Umar Damagum, shugaban rikon kwarya na jam’iyyar PDP. ゚viralシviralシfypシ゚viralシalシ

DA DUMI DUMIN TA Ana babban cin hanci da rashawa a hukumar Hajji Ina Goyonn bayan binciken EFCC -Sheikh Bn UthamanSakata...
24/10/2025

DA DUMI DUMIN TA

Ana babban cin hanci da rashawa a hukumar Hajji Ina Goyonn bayan binciken EFCC -Sheikh Bn Uthaman

Sakataren Kwamitin National Hajj Commission of Nigeria (NAHCON) ya tabbatar da babban cin hanci a harkokin Hajji, ya goyi bayan binciken Economic and Financial Crimes Commission (EFCC)

Daya daga kwamishinonin hukumar NAHCON, Sheikh Muhammad Bin‑Uthman, wanda ke wakiltar yankin-shiyar Arewacin Yamma, ya bayyana cewa akwai babban mataki na cin hanci da rashawa cikin gudanar da ayyukan Hajji a Najeriya.

Ya ce: duk da cewa dokar NAHCON (NAHCON Establishment Act, 2006) ta nuna cewa ya k**ata kwamishinoni su shiga muhimman al’amura na hukumar, amma a aikace hakan ba kullum ake yi ba.

Sheikh Bin-Uthman ya bada misali ga aikin Hajjin shekarar 2025, inda gwamnati ta ba da tallafin naira biliyan 90 ga fursunoni masu zuwa Hajji, amma kwamishinoni ba su san yadda aka kashe kudin ba.

Ya kara da cewa: an bai wa wata kamfani daga Saudiyya kwangila ba tare da sanin kwamishinoni guda shida ba, har ma daraktan aikin gudanarwa na NAHCON bai san da ita ba kuma ya nuna damuwa.

Sheikh Bin-Uthman ya bayyana wuraren da cin hanci da rashawa s**a fi yawa: kwangiloli na masauki, ciyarwa, sufuri da dai sauransu.

A yayin da yake goyon bayan binciken da EFCC ke yi, ya ce: “Wannan bincike zai bai wa kowa dama ya kare kansa. Idan wanda ake bincike yana da dalili na gaskiya, to babu dalili ya damu.”

Ya ƙara da cewa kasancewarsa a matsayin kwamishina ba ya ba shi dama ko masaniyar duk harkokin hukumar k**ar yadda aka k**ata ba ma’aikatan gudanarwa ba su kawo rahoto ko tuntuba gare su ba. ゚viralシviralシfypシ゚viralシalシ

Ya bayyana cewa ya taɓa tattaunawa da shugaban NAHCON, Prof. Salih Umar Faruk (wanda aka ambata da “Pakistan” a cikin labarin) game da wasu abubuwa, amma ya ce ba zai bayyana cikakken abin da tattaunawar ta ƙunsa ba saboda kiyaye mutunci.

Wata wasiƙa da aka fitar daga ajiyar sirrin Email na Hillary Clinton, tsohuwar sakatariyar Amurka, ta bayyana cewa tsoho...
24/10/2025

Wata wasiƙa da aka fitar daga ajiyar sirrin Email na Hillary Clinton, tsohuwar sakatariyar Amurka, ta bayyana cewa tsohon shugaban Libiya Muammar Gaddafi yana da fiye da ton 143 na zinari da azurfa, da nufin ƙirƙiryar sabon kuɗin Afrika mai suna Golden Dinar.

Wasiƙar da abokiyar amintarta Sidney Blumenthal ta aika, ta nuna cewa bayanan leƙen asirin Faransa sun ga wannan shiri a matsayin barazana ga kuɗin CFA franc da tasirin Faransa a Afrika. An ce Shugaba Nicolas Sarkozy ne ya jagoranci harin kan Libiya domin kare muradun Faransa, samun mai, da hana Gaddafi ciyar da burinsa na haɗa kan Afrika gaba ɗaya.

Abin lura, babu wani ambaton dalilan jinƙai da NATO ke amfani da su, abin da ya tayar da tambaya kan ainihin manufar yaƙin.

Shin kuna ganin an hallaka Gaddafi ne domin kare sha’anin Yammacin Duniya, ba domin dimokuraɗiyya ba k**ar yadda aka ce?

📷Mu'ammar Gaddafi/Credit [Getty Images]

Address

Zoo Road Kano
Kano
8000

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Juma concept posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Juma concept:

Share

Category