Juma concept

Juma concept An bude shafin Juma concept ne ranar 20 ga watan mayu shakara ta 2025 domin ya'da shirye shiryen ta da harshen Hausa A Facebook , TikTok ,YouTube da Instagram.

Ministan Tsaro Ya Ajiye AikiMinistan tsaron Najeriya, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, ya ajiye aikinsa daga mukaminsa n...
01/12/2025

Ministan Tsaro Ya Ajiye Aiki

Ministan tsaron Najeriya, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, ya ajiye aikinsa daga mukaminsa nan take.

A wata wasiƙa da ta ɗauki ranar 1 ga Disamba, wadda ya aikawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Badaru ya bayyana cewa ya yi murabus ne saboda dalilan lafiya.

Shugaba Tinubu ya amince da murabus ɗin nasa, tare da gode masa bisa irin gudummawar da ya bayar wa ƙasa.

Ana sa ran Shugaba Tinubu zai sanar da majalisar dattawa sunan wanda zai maye gurbin Badaru a cikin wannan makon.

Badaru Abubakar, mai shekaru 63, ya taɓa kasancewa gwamnan jihar Jigawa har sau biyu daga 2015 zuwa 2023. An naɗa shi minista a ranar 21 ga Agusta, 2023, daga Shugaba Tinubu.

Murabus ɗinsa ya zo ne a daidai lokacin da Shugaba Tinubu ya bayyana dokar ta-baci kan harkokin tsaron ƙasa, inda ake jiran ƙarin bayani kan matakan da gwamnati za ta ɗauka.

Da Dumi-Dumi: An ji ƙarar harbe-harbe  a shelkwatar PDPA yanzu haka ana cikin ɗar-ɗar a shelkwatar jam’iyyar PDP da ke A...
18/11/2025

Da Dumi-Dumi: An ji ƙarar harbe-harbe a shelkwatar PDP

A yanzu haka ana cikin ɗar-ɗar a shelkwatar jam’iyyar PDP da ke Abuja kan yunkurin gudanar da taruka biyu daban-daban a lokaci guda.

Kwamitin Zartarwa na Kasa (NWC) da aka zaba a Ibadan, fadar jihar Oyo, da kuma bangaren da ministan Abuja, Nyesom Wike, ke goyon baya, duka sun tsara gudanar da taruka a yau.

Sakataren jam’iyya na kasa na bangaren Wike, Samuel Anyanwu, ya isa Wadata Plaza tare da wasu mambobin bangaren nasa.

Bayan dan lokaci, mambobin bangaren Taminu Turaki suma sun isa hedkwatar amma aka hana su shiga.

Sai dai gwamnonin jihohi biyu sun tilasta shiga, amma lokacin da sauran mambobin bangaren s**a yi kokarin shiga, jami’an tsaro s**a harba bindiga tare da sakin hayakin barkewa domin tarwatsa su.

lamarin ya haifar da rudani inda mutane s**a ruga neman tsira.

Yayin da yake jawabi ga 'yan jarida a ofishinsa kafin zuwan bangaren na biyu, Anyanwu ya ce karuwar tsaro al’ada ce domin hana tashin hankali da rikici.

YANZU-YANZU: Kakakin Majalisar Jihar Taraba Hadi Da Wasu Daga Cikin ’Yan Majalisar Jam'iyyar PDP Sun Sauya Sheƙa Zuwa AP...
18/11/2025

YANZU-YANZU: Kakakin Majalisar Jihar Taraba Hadi Da Wasu Daga Cikin ’Yan Majalisar Jam'iyyar PDP Sun Sauya Sheƙa Zuwa APC A Hukumance

Hoton Dakunan Kwana Na GGCSS Maga, Kebbi inda akai awon gaba da Dalibai 25, da Kuma hallaka Vice Principal
18/11/2025

Hoton Dakunan Kwana Na GGCSS Maga, Kebbi inda akai awon gaba da Dalibai 25, da Kuma hallaka Vice Principal

Jam'iyyar Haɗaka ADC Zata Kaddamar Da Sabuwar Hedikwatar Ofishin Jam'iyyar A Babban Birnin Tarayya Abuja Ayau Litinin
18/11/2025

Jam'iyyar Haɗaka ADC Zata Kaddamar Da Sabuwar Hedikwatar Ofishin Jam'iyyar A Babban Birnin Tarayya Abuja Ayau Litinin

YANZU-YANZU: Mun kammala dukkan wata shiri na daukan mataki kan Najeriya.Sa'o'i kadan bayan Trump ya yi barazanar daukar...
02/11/2025

YANZU-YANZU: Mun kammala dukkan wata shiri na daukan mataki kan Najeriya.

Sa'o'i kadan bayan Trump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya, sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth ya ce ma'aikatar tsaro ta Pentago ta shirya domin aiwatar da wannan umurni muddin Abuja ba ta dauki matakin kawo karshen kisan Kiristoci da masu tsattsauran ra'ayin Islama ke yi a kasar ba.

Natasha Ta Gayyaci Akpabio Zuwa Bikin Kaddamar da Ayyuka a KogiDangantaka tsakanin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan (PDP, ...
31/10/2025

Natasha Ta Gayyaci Akpabio Zuwa Bikin Kaddamar da Ayyuka a Kogi

Dangantaka tsakanin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan (PDP, Kogi ta Tsakiya) da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ta fara samun sauƙi bayan Akpoti-Uduaghan ta aika da gayyata ga Akpabio domin halartar bikin kaddamar da ayyuka a yankinta.

Gayyatar, wacce aka rubuta da hannunta, ta kuma haɗa da sauran sanatoci, kuma an karanta ta a zauren majalisar yayin zaman ranar Alhamis da Akpabio kansa ya karanta.

A cewar wasikar, bikin zai gudana ne a ranar Lahadi a Ihima, Jihar Kogi, domin bikin cika shekaru biyu da Akpoti-Uduaghan ta yi a majalisar dattawa.

“A yayin bikin cika shekaru biyu a matsayin Sanata mai wakiltar al’ummata, ina gayyatar sanatoci abokaina da su zo bikin kaddamar da ayyuka a Jihar Kogi,” in ji wasikar.

An bayyana Plot 101, Jimoh Akpoti Street, Ihima, Okene a matsayin wurin taro, inda aka ba da shawarar cewa sanatocin da ke tafiya ta jirgi su sauka a Obajana Airstrip kafin su ci gaba zuwa Ihima ta hanya.

Bayan karanta gayyatar, Akpabio ya taya ta murna a gaba da kowa da cewa:

“Ina taya ki murna a gaba.”

Wannan mataki na nuna sabon yanayi na sulhu bayan rikicin da ya barke a watan Fabrairu kan rabon kujeru a majalisar, wanda ya jawo dakatar da Sanata Akpoti-Uduaghan na tsawon watanni shida daga aiki a ranar 6 ga Maris.

Tun bayan dawowarta a ranar 24 ga Satumba, Sanatar ta fara sake shiga hulɗa da Akpabio a zauren majalisa, ciki har da bayar da gudunmawa a muhawara da dokoki. Amma wannan gayyatar ce ta fi nuna mataki kai tsaye na sulhu da shugabancin majalisar.

DA DUMI-DUMI: Rahotanni daga ƙasar Tanzania na nuna cewa dubban yan kasar sun k**a hanyar zuwa fadar gwamnatin kasar don...
31/10/2025

DA DUMI-DUMI: Rahotanni daga ƙasar Tanzania na nuna cewa dubban yan kasar sun k**a hanyar zuwa fadar gwamnatin kasar don ganawa ido da ido tsakanin su da shugaba Samia Saluhu inda zasu roƙe tayi murabus cikin lalama ko da tsiya.

HOTUNA: Yanda dandazon ɗaruruwan sojoji su ka yi wa Janar Christopher Musa rakiya yayin bankwana da barikin soja na Moga...
31/10/2025

HOTUNA: Yanda dandazon ɗaruruwan sojoji su ka yi wa Janar Christopher Musa rakiya yayin bankwana da barikin soja na Mogadishu Cantonment wanda ke unguwar Asokoro a Abuja bayan rantsar da sabon Babban Hafsan Hafsoshin tsaron Najeriya a jiya Alhamis.

Ziyarar tsoffin ‘yan wasan Barcelona shaida ce ta samuwar tsaro da zaman lafiya - Ministan Tsaron NijeriyaMinistan tsaro...
25/10/2025

Ziyarar tsoffin ‘yan wasan Barcelona shaida ce ta samuwar tsaro da zaman lafiya - Ministan Tsaron Nijeriya

Ministan tsaron Nijeriya, Dr. Bello Muhammad Matawalle, ya bayyana ziyarar tsoffin ‘yan wasan ƙungiyar kwallon kafa ta Barcelona zuwa Nijeriya a matsayin tabbacin dawowar zaman lafiya, tsaro da kwanciyar hankali a Nijeriya.

A wata sanarwa da mataimakinsa na musamman kan yaɗa labarai, Ahmad Dan-Wudil, ya fitar a Abuja ranar Juma’a, Matawalle ya ce ziyarar ta nuna yadda ƙasashen duniya ke sake samun kwarin gwiwa kan ƙoƙarin da gwamnatin Nijeriya ke yi wajen magance matsalar tsaro.

A cewar Matawalle, ziyarar tsoffin ‘yan wasan Barcelona zuwa Nijeriya hujja ce ta ci-gaban da ƙasarmu ta samu wajen farfaɗo da tsaro da zaman lafiya.

Hakazalika, ya ƙara da cewa wannan lamari ya nuna Nijeriya ta zama kasar da ke jan hankalin ƙasashen duniya sak**akon jajircewar jami’ai da hukumomin tsaron kasar.

Matawalle ya bayyana wasan sada zumunci da tsoffin ‘yan wasan Barcelona za su buga da tsoffin taurarin ‘yan wasan Afirka a ranar Asabar, 25 ga watan Oktoba 2025, a filin wasa na Moshood Abiola da ke Abuja, a matsayin nasara ga gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu wajen tabbatar da zaman lafiya da samuwar yanayi mai kyau domin gudanar da wasannin kasa da kasa.

Daga karshe, Matawalle ya kuma yi wa tawagar tsoffin ‘yan wasan maraba a madadin gwamnatin Nijeriya da ma ‘yan Nijeriya, da fatan natsuwa da nishadi a lokacin da za su shafe a Nijeriya.

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaban Jam'iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas Ya Tsere Don Gudun Karɓar Sammacin Kotu - Bar...
25/10/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaban Jam'iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas Ya Tsere Don Gudun Karɓar Sammacin Kotu - Barrister Badamasi Gandu

‎‎Babbar Kotu a jihar Kano ta aike wa da shugaban jam'iyyar APCn jihar Kano Prince Abdullahi Abbas da sammaci amma ya tsere ya ƙi karɓa, wannan mataki na kotun na zuwa ne bayan da wasu ƴan jam'iyyar APCn s**a kai ƙara gabanta bisa kora da shugaban jam'iyyar ya yi musu.

‎Barrister Badamasi Sulaiman Gandu ya bayyanawa manema labarai yadda al'amarin ya kasance inda ya ce Shugaban Jam'iyyar APC Abdullahi Abbas ya tsere Bayan da s**a kai masa sammacin kotu don jin ba'asin korar da ya yi wa wasu ƴan APCn jihar saboda suna faɗar gaskiya idan an yi rashin daidai a jam'iyyar tasu kasancewarsu ƴan ƙasa nagari.

‎Barrister Badamasi ya ƙara da cewa za su koma Kotu domin roƙon ta ba su dama su kafe sammacin a gaban ofishin jam'iyyar ta APC.

Me za ku ce?

Gwamnatin Kano ta janye dokar tsaftar muhalli ta watan Oktoba Ma'aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi ta jihar Kano ta sanar...
25/10/2025

Gwamnatin Kano ta janye dokar tsaftar muhalli ta watan Oktoba

Ma'aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi ta jihar Kano ta sanar da janye dokar tsaftar muhalli ta wata-wata, a wannan wata na Oktoba.

Daraktar Yaɗa Labarai ta ma'aikatar, Maryam Abdulkadir ta fitar da sanarwar a yammacin yau Juma'a.

Ya ce Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi Dakta Dahir M Hashim ne ya bada umarnin januewar saboda wasan kalankuwa da za a kaddamar a gobe Asabar.

A cewar sanarwar, Kwamishinan ya ce za a samu mahalrta bikin wasannin daga sassa daban-daban na ƙasa, inda ya ce ya k**ata a baiwa al'umma dama su yi zirga-zirga.

Address

Zoo Road Kano
Kano
8000

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Juma concept posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Juma concept:

Share

Category