SARAUNIYA NEWS

SARAUNIYA NEWS SARAUNIYA NEWS Sahihiyar Jarida Ce Da Take Kawo Ingantattun Labarai, Siyasa, Rahotanni, Wasanni, Nis

21/11/2025

Tura Ta Kai Bango

19/11/2025

Fusatattun Matasa Sun Jefi Ayarin Motocin Gwamnan Neja.

BIDIYO: Sahara Reporters

WANDA AKE ZARGI DA KITSA MUNANAN HARE-HAREN JIHAR KANOKotu a Abuja ta daure Hussaini Ismail wanda ake yi wa inkiya da Ma...
19/11/2025

WANDA AKE ZARGI DA KITSA MUNANAN HARE-HAREN JIHAR KANO

Kotu a Abuja ta daure Hussaini Ismail wanda ake yi wa inkiya da Mai Tangaran tsawon shekaru 20 sak**akon samun sa da laifin kai munanan hare-hare a jihar Kano cikin shekarar 2012.

A cewar yan sandan farin kaya (SSS) sun gabatar da shaidar cewa, Mai Tangaran shine ya jagoranci kaddamar da hare-haren da kungiyar ISWAP ta kai sassan jihar Kano.

Harin da ya hada da Hedikwatar yansanda ta Bompai, sansanin yansandan kwantair da tarzoma ta jihar Kano, ofishin yansanda na Farm Centre,, ofishin yansanda na Unguwa Uku da sauran wurare.

HOTUNA: Yadda shugaban ƙaramar hukumar Roni a jihar Jigawa ya tallafa wa al'ummarsa da baron sayar da ruwa domin dogaro ...
01/11/2025

HOTUNA: Yadda shugaban ƙaramar hukumar Roni a jihar Jigawa ya tallafa wa al'ummarsa da baron sayar da ruwa domin dogaro da kai.

Magidanci Ya Sheke Matarsa A Jihar Kano Saboda Ta Ki Yi Masa Kuli-Kuli Daga Yasir Kallah Wata Babbar Kotun jihar Kano da...
31/10/2025

Magidanci Ya Sheke Matarsa A Jihar Kano Saboda Ta Ki Yi Masa Kuli-Kuli

Daga Yasir Kallah

Wata Babbar Kotun jihar Kano da ke zamanta a titin Miller Road ta bayar da umarnin tsare wani mutum mai suna Idris Kurma a gidan kaso sak**akon zargin sa da ake da laifin kashe matarsa mai suna A'isha Idris bayan ta ƙi niƙa gyaɗa domin ta yi masa ƙuli-ƙuli k**ar yadda ya umarce ta.

Alƙalin kotun, Justice Musa Ɗahiru ne ya bayar da umarnin bayan gurfanar da wanda ake zargin a gabansa da laifin kisan kai, wanda ya saɓa wa sashi na 221 a kundin dokar penal code.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru a ƙauyen Goda na ƙaramar hukumar Shanonon jihar Kano.

A yayin zaman kotun, lauyan masu gabatar da ƙara, Barrister Lamiɗo Abba Soron Ɗinki ya karanta wa wanda ake zargin abin da ake tuhumar sa, inda kuma ya musanta aikatawa. Hakan ne ya sa Soron Ɗinki ya nemi a ɗage zaman kotun domin masu gabatar da ƙarar su kawo shaidunsu.

Mai shari'ar ya amince da roƙon inda ya ɗage zaman kotun zuwa ranar 12 ga watan Disamba, 2025, domin ci gaba da sauraren ƙarar.

Da Ɗumi-Ɗumi: Shugaba Tinubu Ya Canja Manyan Hafsoshin Sojin Nijeriya Daga Yasir Kallah Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sau...
24/10/2025

Da Ɗumi-Ɗumi: Shugaba Tinubu Ya Canja Manyan Hafsoshin Sojin Nijeriya

Daga Yasir Kallah

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sauya manyan hafsoshin sojin Nijeriya domin ƙarfafa tsaron ƙasa, k**ar yadda Sunday Dare, Mai Bai Wa Shugan Ƙasa Shawara na Musamman a kan yaɗa labarai, ya sanar a yau Juma'a.

Shugaban Kasar ya zaɓi Janar Olufemi Oluyede ya maye gurbin Janar Christopher Musa a matsayin Babban Hafsan Hafsoshin ƙasar. Sabon Babban Hafsan Sojin Ƙasa shi ne Manjo Janar W. Shaaibu. Air Vice Marshall S.K Aneke shi ne ya zamo Sabon Babban Hafsan Sojin Sama, yayin da Rear Admiral I. Abbas ya zamo Sabon Babban Hafsan Sojin Ruwa. Shi kuma Manjo Janar E.A.P Undiendeye zai ci gaba da riƙe muƙaminsa na Shugaban Hukumar Leƙen Asiri na Tsaro.

YANZU-YANZU: Ƴan Sanda Sun K**a Sowore A Kotu Daga Yasir Kallah Rundunar ƴan sandan Nijeriya ta k**a mai rajin kare haƙƙ...
23/10/2025

YANZU-YANZU: Ƴan Sanda Sun K**a Sowore A Kotu

Daga Yasir Kallah

Rundunar ƴan sandan Nijeriya ta k**a mai rajin kare haƙƙin ɗan'adam, kuma tsohon ɗan takarar kujerar shugaban ƙasar Nijeriya, Omoyele Sowore, a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja.

Sowore, wanda ya jagoranci zanga-zangar neman sakin jagoran haramtacciyar ƙungiyar fafutukar kafa ƙasar Biafra ta IPOB, Nnamdi Kanu, a ranar Litinin a Abuja ya tsare daga wajen zanga-zangar a lokacin da ƴan sanda s**a damƙe wasu daga cikin mabiyansa.

Kafin a fara zanga-zangar, rundunar ƴan sanda ta yi gargaɗi ga masu shirya zanga-zangar da su guji zuwa kusa da wasu wurare masu muhimmanci a Birnin Tarayyar amma Sawore ya yi kunnen uwar shegu, inda ya ce yana da ƴancin yin zanga-zangar.

A yau ne Soworen ya halarci zaman kotun da ke gudana a game da batun Kanu a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja.

"A yau, na haɗu da Kanu Agaji, babban lauyan Kanu Nnamdi, a Babbar Kotun Tarayya, kuma ya faɗa min cewa tawagarsa za ta janye daga ƙarar, inda za ta bar Nnamdi Kanu ya ci gaba da shari'arsa ba tare da wakili ba. Ya yi matuƙar tabbatar da cewa gabaki ɗaya siyasa ce," Soworen ya wallafa kafin a k**a shi.

A lokacin da yake ƙoƙarin fita daga kotun ne tawagar ƴan sanda ta tsayar da shi tare da umartar sa da ya bi su zuwa ofishinsu.

Bayan sun ɗan yi musayar yawu ne Soworen ya amince ya bi su.

Da yake magana game da kamun, ɗaya daga cikin makusantan Soworen ya shaida wa Daily Trust cewa tun da farko Kwamishinan Ƴan Sanda na Birnin Tarayyar ya tura wa Soworen saƙon gayyata kuma dama zai amsa gayyatar.

Auren Mai Wushirya: Babu Kotun Da Ke Da Ikon Yi Wa Mutum Auren Dole – NBA  Daga Yasir Kallah Ƙungiyar Lauyoyin Nijeriya ...
22/10/2025

Auren Mai Wushirya: Babu Kotun Da Ke Da Ikon Yi Wa Mutum Auren Dole – NBA

Daga Yasir Kallah

Ƙungiyar Lauyoyin Nijeriya (NBA) ta soki umarnin da wata kotun majistare a jihar Kano ta bayar na tursasa aurar da wasu ƴan TikTok guda biyu, Idris Mai Wushirya da Basira Ƴar Guda, sak**akon zargin su da ake musu na aikata laifin wallafa wasu bidiyoyi na rashin ɗa'a.

Umarnin, wanda Mai Shari'a Halima Wali ta bayar a ranar Litinin, ya zo bayan yaɗuwar wasu bidiyoyi a shafukan sada zumunta da ke nuna matasan guda biyu suna nuna soyayyarsu ga juna, wanda kuma Hukumar Tace Fina-Finai da Ɗab'i ta Kano ta same su da aikata rashin ɗa'a da yaɗa alfasha.

Kotun ta umarci Hukumar Hisba ta jihar Kano da ta sa ido a kan shirin auren, inda ta yi gargaɗin cewa idan aka gaza shirya auren a cikin lokacin da ta gindaya to hakan zai zamo raini ga kotun.

Da yake yin martani a game da batun, shugaban ƙungiyar lauyoyin, Afam Osigwe, ya bayyana hukuncin kotun a matsayin asalin rashin fahimtar ikon shari'a a ƙarƙashin Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya da kuma take haƙƙoƙin mutane.

Ya bayyana cewa babu wata kotu da ke da ikon tursasa mutum ya auri wani, inda ya ƙara da faɗin cewa wannan umarnin kotun ba shi da tushe a cikin tsarin dokokin Nijeriya.

Osigwe ya yi kira da a yi gaggawar sake nazarin dokar, sannan ya shawarci hukumomin shari'ar da su ɗauki matakan da s**a dace wajen guje wa sake aikata ire-iren hukuncin da ya saɓa wa kundin tsarin mulki a gaba.

A Karo Na Farko Sauro Ya Ɓulla A Ƙasar Iceland Daga Yasir Kallah A karo na farko an gano halittar sauro a ƙasar Iceland ...
21/10/2025

A Karo Na Farko Sauro Ya Ɓulla A Ƙasar Iceland

Daga Yasir Kallah

A karo na farko an gano halittar sauro a ƙasar Iceland wadda ta kasance ɗaya daga cikin ƙasashen duniya mara sa sauro, k**ar yadda wani mai bincike ya faɗa wa AFP a ranar Litinin.

An ga wasu jinsunan sauro da ake kira Culiseta Annulata guda uku, mata biyu da namiji ɗaya a nisan kimanin kilomita 30 (mil 20) daga arewacin banban birnin Reykjavik, k**ar yadda Matthias Alfredsson, wani masanin ilimin ƙwari a wata cibiyar ilimin kimiyyar ƙasar ya faɗa.

Bayan nahiyar Antarctica, Iceland ta jima da kasancewa ɗaya daga cikin ɗaiɗaikun wurare a duniya da sam babu sauro.

Mai binciken ya ce babu mamaki sauron ya ɓulla cikin ƙasar ta dalilin jiragen ruwa ko kwantenonin da aka shigo da su daga wata ƙasar, sannan za su ci gaba da saka ido da bincike domin gano yaɗuwarsu a gaba.

Mataimakin Shugaban Najeriyar ya bayyana ƙudirin gwamnatin Tinubu na inganta karatun yara mata da kuma ƙarfafa mata a ha...
21/10/2025

Mataimakin Shugaban Najeriyar ya bayyana ƙudirin gwamnatin Tinubu na inganta karatun yara mata da kuma ƙarfafa mata a harkar shugabanci.

A ɓangarenta, matashiya Joy Ogah ta ce mata na iya zama shugabanni idan hukumomi da masu ruwa da tsaki s**a aiwatar da matakan da s**a dace.

21/10/2025

AUREN MAI WUSHIRYA: Gaskiyar Abinda Ya Faru A Kotu.

"Har Yanzu Kwankwaso Shago ne a Fagen Siyasar Najeriya"Daga Rahma AbdulmajidInji Shugaba Tinubu a wasikar taya murnar za...
21/10/2025

"Har Yanzu Kwankwaso Shago ne a Fagen Siyasar Najeriya"

Daga Rahma Abdulmajid

Inji Shugaba Tinubu a wasikar taya murnar zagayowar ranar haihuwar Sanata
A wani baitin ma cewa yake
"Kwankwaso yana nan a matsayin aboki kuma takwaran aikina tun muna yan majalisar tarayya a 1992 sannan a matsayin gwamnoni a 1999"

"Har ila yau, mun yi aiki tare a yayin gwagwarmayar kafa Jam'iyyar All Progressives Congress (APC). Duk da cewa daga baya ya bar APC don kafa tasa Jam’iyyar ta New Nigeria Peoples Party (NNPP), amma abu mafi muhimmanci shine kasancewarsa jigo a sahun gaba a bangaren siyasa,”

Shugaban ya yi wa Kwankwaso fatan alheri, ɗorewar lafiya, da kuma karin shekaru masu amfani cikin hidimar al’umma.

Address

Maiduguri Road, Tarauni LGA
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when SARAUNIYA NEWS posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to SARAUNIYA NEWS:

Share