SARAUNIYA NEWS

SARAUNIYA NEWS SARAUNIYA NEWS Sahihiyar Jarida Ce Da Take Kawo Ingantattun Labarai, Siyasa, Rahotanni, Wasanni, Nis

An Rufe Gidajen Gala A Jihar Kano Hukumar tace fina-finai da Dab'i ta Jahar Kano karkashin jagorancin Alh. Abba El-musta...
21/05/2025

An Rufe Gidajen Gala A Jihar Kano

Hukumar tace fina-finai da Dab'i ta Jahar Kano karkashin jagorancin Alh. Abba El-mustapha ta soke lasisin wasu gidajen wasannin gala har guda 8 bisa samunsu da laifin karya dokokin ta.

A wata sanarwa da jami'an yada labaran Hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ya fitar Jim kadan bayan kammala taro da manya jami'an Hukumar, ya bayyana cewa gidajen wasannin da aka rufe sun hada da

1. HAMDALA ENTERTAINMENT (Ungoggo)
2. LADY J ENTERTAINMENT (SanyaOlu)
3. DAN HAUSA ENTERTAINMENT (Sanya Olu)
4. NI'IMA (Zungeru)
5. ARIYA ENTERTAINMENT ( Abedi sabon gari)
6. BABBANGIDA ENTERTAINMENT (Balatus)
7. HARSASHI ENTERTAINMENT ( Ebedi sabon gari)
8. WAZOBIYA (Sanya Olu)

Abdullahi Sani ya Kara da cewa doka ce ta bawa Hukumar damar saka ido tare da tabbatar da masu gidajen wasanni basu ketare iyaka ba inda ya bayyana cewa dokar ta kara bawa Hukumar damar ladaftar da duk wani gida ko dan wasa data samu da aikata laifi.

Idan ba'a mantaba a kwanakin baya Hukumar tayi gargadi tare da dakatar da wasu gidajen wasannin gala tare da soke lasisin wasu daga cikinsu biyo bayan samun su da laifi.

Abba El-mustapha ya yi kira ga jami'an tsaro dasu cigaba da bawa Hukumar hadin Kai sau da kafa domin tabbatar da ana bin doka yadda ya k**ata.

21/05/2025

"Ƴan siyasa da sojoji na daga cikin masu ba wa Boko Haram bayanai".

- Gwamnan jihar Borno Babagana Zulum

Babu Wacce Ta Zo Kannywood A Cikakkiyar Budurwa - Sallau Dadin Kowa Jarumin shirin Daɗin Kowa Umar Jigirya da aka fi san...
16/05/2025

Babu Wacce Ta Zo Kannywood A Cikakkiyar Budurwa - Sallau Dadin Kowa

Jarumin shirin Daɗin Kowa Umar Jigirya da aka fi sani da Sallau a shirin Daɗin Kowa na tashar Arewa 24 ya bayyana cewa, yana da yakini sannan kuma yana zargin babu wacce ta shigo masana'antar Kannywood tana matsayin cikakkiyar budurwa.

Zargin Basarake a Masarautar Daura da Garkuwa da Matar Aure, Fyade da Karɓar Kudin Fansa Naira Miliyan 20 ya Janyo Zanga...
16/05/2025

Zargin Basarake a Masarautar Daura da Garkuwa da Matar Aure, Fyade da Karɓar Kudin Fansa Naira Miliyan 20 ya Janyo Zanga-zanga a Baure

Zaharaddeen Ishaq Abubakar | Katsina Times

Wani Basarake a karkashin Masarautar Daura, Iliya Mantau, (Dagachin Mantau) wanda shi ne mai rikon sarautar garin Yan Maulu a ƙaramar hukumar Baure, Jihar Katsina, yana fuskantar zargin hannu dumu-dumu a cikin garkuwa da wata matar aure tare da ɗanta ɗan wata uku da kuma yi mata fyade duk da an biya kuɗin fansa har Naira miliyan 20.

Rahotanni sun bayyana cewa, lamarin ya faru ne kusan shekara guda da ta gabata, inda wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne s**a sace Zulaihatu Sidi da jaririnta. Bayan mako guda da sace su, an sake su bayan an biya kuɗin fansa, amma duk da haka sai da aka yi wa matar fyade.

Wannan lamari ya tayar da kura a garin Yanmaulu dake ƙarƙashin Masarautar Daura, inda matasa s**a fito zanga-zanga domin neman a tabbatar da adalci ga Zulaihatu da yaronta.

Jagoran zanga-zangar, Muhammad Abdullahi, ya shaida wa manema labarai cewa, “A yanzu shekara ɗaya kenan da Zulaihatu da ɗanta s**a shiga hannun masu garkuwa. Koda aka biya kuɗin fansa, sai da aka ci zarafinta ta hanyar fyade. Muna da tabbacin cewa akwai wasu jiga-jigan mutanen da ke da hannu cikin wannan aika-aika, ciki har da Dagachin garin mu na Mantau Ilya mai rikon sarautar garin 'Yan Maulu.”

Muhammad ya ƙara da cewa, mutane takwas ne aka k**a da hannu a lamarin, kuma yawancinsu daga ƙauyen Mantau ne. Ya ce daga cikin waɗanda ake zargi akwai Iliya Mantau, wanda ke matsayin wakilin Hakimin Yanmaulu kuma wanda ake zargin ya shugabanci masu garkuwa da mutane a yankin.

Sai dai, masu zanga-zangar sun bayyana damuwa da cewa, duk da an gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban kotu, Masarautar Daura na ƙoƙarin ganin an saki Dagachin da ake zargi, lamarin da ya tayar musu da hankali.

“A saboda haka muka fito domin mu bayyana damuwarmu game da yunkurin da Masarautar Daura ke yi na shawo kan shari’ar domin a saki Dagachin,” in ji Muhammad.

Sun yi kira ga Gwamna Dikko Umar Radda da ya shiga cikin lamarin kai tsaye domin tabbatar da an yi wa Zulaihatu da ɗanta adalci, tare da gurfanar da duk masu hannu a gaban shari’a ba tare da wata rufa-rufa ba.

Har zuwa yanzu, babu wata sanarwa daga Masarautar Daura dangane da zargin da ake yi wa Iliya Mantau, wanda ke tsare tare da wasu da ake zargi da hannu a garkuwa da mutane da cin zarafin mata.

A cewar wasu daga cikin mazauna garin Mantau, har yanzu babu wata takarda daga hukumomi da ke nuna cewa an dakatar da mai garin daga mukaminsa, duk da cewa jami’an tsaro sun gudanar da bincike kuma sun tsare shi tare da sauran mutane da ake zargi.

Mazauna yankin da masu fafutukar adalci sun ce dole ne a cire siyasa da shisshigi daga wannan lamari domin ganin gaskiya ta samu nasara, musamman ganin cewa lamarin ya shafi basarake a wani babban yanki na masarauta.

Ana fargabar kusan mutane 20 sun rasu a wani hatsarin babbar mota da ya faru a gadar Muhammadu Buhari dake Hotoro a Kano...
14/02/2025

Ana fargabar kusan mutane 20 sun rasu a wani hatsarin babbar mota da ya faru a gadar Muhammadu Buhari dake Hotoro a Kano.

Hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:30 na daren jiya, inda motar ɗauke da Awaki da mutane ta faɗi sak**akon gudun wuce ƙima k**ar yadda shaidun gani da ido s**a bayyana.

SERAP Ta Maka Gwamnatin Tarayya da NCC A Kotu Kan Ƙarin Kuɗin Waya Daga Yasir Kallah Kungiyar SERAP, mai fafutukar yaƙi ...
26/01/2025

SERAP Ta Maka Gwamnatin Tarayya da NCC A Kotu Kan Ƙarin Kuɗin Waya

Daga Yasir Kallah

Kungiyar SERAP, mai fafutukar yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya ta maka gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da Hukumar Sadarwa ta Nijeriya, NCC, a kotu kan ƙarin kashi 50 cikin ɗari na cajin waya, saƙon tes, da data a Nijeriya, inda ta yi zargin cewa ƙarin ya saɓa wa kundin tsarin mulkin ƙasar, da tsarin doka, kuma babu hankali da adalci a ciki.

A kwanakin nan ne hukumar NCC ta amince da ƙarin kuɗin, wanda ya ɗaga cajin minti ɗaya na waya daga ₦11 zuwa ₦16.5, farashin data 1GB daga ₦287.5 zuwa ₦431.25, sannan saƙon tes na SMS daga ₦4 zuwa ₦6.

Ƙarin kuɗin ya jawo ce-ce-ku-ce da s**a mai yawa ga hukumar NCC ɗin da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, inda ita ma ƙungiyar SERAP ta ruga kotu domin a dakatar da ƙarin.

A ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/111/2025 wadda ta shigar a gaban Babbar Kotun Tarayya, SERAP ta koka a kan ƙarin kuɗin ya keta haƙƙin al'umma na ƴancin magana da samun bayanai k**ar yadda kundin tsarin mulkin Nijeriya da dokokin duniya s**a ƙunsa.

SERAP ɗin ta roƙi kotun da ta bayyana cewa ƙarin kuɗin ya saɓa wa kundin tsarin mulkin Nijeriya da dokokin duniya na ƴancin ɗan'adam, sannan ta dakatar da aiwatar da ƙarin tare da soke shi baki ɗaya.

Boko Haram Ta Hallaka Sojoji 18 da Kwamanda Ɗaya A Borno Daga Yasir Kallah Aƙalla sojoji 19, ciki har da kwamanda ɗaya, ...
26/01/2025

Boko Haram Ta Hallaka Sojoji 18 da Kwamanda Ɗaya A Borno

Daga Yasir Kallah

Aƙalla sojoji 19, ciki har da kwamanda ɗaya, ne s**a rasa ransu a sa'ilin da mayaƙan Boko Haram s**a kai musu farmaki a sansanin sojin da ke Malam-Fatori, ƙaramar hukumar Abadam ta jihar Borno.

Malam-Fatori gari ne da ke kan iyakar Nijeriya da Nijar.

Majiyoyi masu tushe sun yi rahoton cewa maharan sun kai wa bataliyar ta 149 farmakin a ranar Juma'a, 24 ga Janairun 2025.

Majiyoyin sun tabbatar da cewa ƴan ta'addan sun isa sansanin a kan manyan motoci masu bindiga, inda s**a ƙone gine-gine da motocin sojojin a lokacin farmakin.

"Sojoji masu yawa sun samu mummunan rauni yayin da har yanzu ba a ga wasu ba," wata majiya ta bayyana wa gidan talabijin ɗin Channels.

"Kwamandan bataliyar, wanda Laftanal Kanal ne, da wasu manyan hafsoshi guda biyu, ciki har da daraktan lafiyar sansanin, na cikin waɗanda aka kashe a farmakin."

Wannan farmakin ya zo baya ƴan kwanaki kaɗan da ƙungiyar Boko Haram ɗin ta kai mummunan farmaki a kan wani sansanin sojin da ke Damboa, inda ta kashe tarin sojoji da ba a gama tantance yawansu ba.

Kotu Ta Hukunta Budurwa Da Ta Saɓa Alƙawarin Kai Wa Saurayinta Ziyara Wata kotun majistare a Ilesa, jihar Osun, ta umarc...
25/01/2025

Kotu Ta Hukunta Budurwa Da Ta Saɓa Alƙawarin Kai Wa Saurayinta Ziyara

Wata kotun majistare a Ilesa, jihar Osun, ta umarci wata budurwa mai suna Rhoda Audu da ta biya saurayinta mai suna Eru Dupe Naira 150,000 a matsayin diyya sak**akon karɓar Naira 3000 da ta yi a wajensa a matsayin kuɗin motar kai masa ziyara amma daga ƙarshe ta cinye kuɗin tare da saɓa alƙawarin zuwa.

An fara samun saɓanin a lokacin da Eru Dupe ya tura wa Rhoda kuɗin motar, inda ita kuma daga baya ta kashe wayarta tare da ƙin zuwa. Ganin cewa ta damfare shi ne ya ɓata masa rai, inda kai-tsaye ya kai ƙara ofishin ƴan sandan Ayeso, su kuma ƴan sanda ba su yi ƙasa a gwiwa ba s**a je s**a kamo Rhoda sannan s**a gurfanar da ita a kotu.

Yayin gabatar da shari'ar, Eru ya gabatar wa da kotun shaida, ciki har da shaidar tura kuɗin ta waya da kuma saƙonnin WhatsApp tsakanin shi da Rhoda.

A hukuncin da ta yanke, Mai Shari'a Okogun Oludare ta umarci Rhoda da ta biya Eru Naira dubu ukunsa da kuma ƙarin Naira 100,000 ta laifin saɓa yarjejeniya, da kuma ƙarin wata Naira 50,000 a matsayin diyyar sa shi a cikin damuwa.

Kotun ta kuma jaddada cewa ta yanke hukuncin domin ya zama izina ga masu irin wannan halin cin amanar.

– Yasir Kallah

TUNAWA DA GWARZO Daga Muhammad Saliadeen CisseA ranar 25 ga watan Junairu 2017. Yakubu Muhammad Fannami ɗan aji 1 wato S...
25/01/2025

TUNAWA DA GWARZO

Daga Muhammad Saliadeen Cisse

A ranar 25 ga watan Junairu 2017. Yakubu Muhammad Fannami ɗan aji 1 wato SS1 a makantar (Darussalam Science and Islamic Academy) ya ceci rayukan jama'a masu yawa a wani Masallaci da ke Kaleri a jihar Borno.

A inda yayi kukan-kura ya tunkari yar kunan bakin-kake da ta nufi Masallacin yayin da mutane ke tsaka da Ibada, a In da bam din jikanta ya tarwatse tare da shi, ya ceci rayukan wadanda suke cikin Masallacin.

Allah Ya jiƙan Yakubu Muhammad Fannami.

25/01/2025

Malamai Na Ci Gaba Da Yi Wa Shugaban Izala Sheikh Bala Lau Raddi Akan Taron Bikin Alkur'ani

DA ƊUMI-ƊUMI.....Shugaban ƙasa Ahmad Bola Tinubu ya naɗa Shugaban jam‘iyyar APC Abdullahi Umar Ganduje  zai rike mukamin...
24/01/2025

DA ƊUMI-ƊUMI.....

Shugaban ƙasa Ahmad Bola Tinubu ya naɗa Shugaban jam‘iyyar APC Abdullahi Umar Ganduje zai rike mukamin shugaban hukumar gudanarwa wato Board Chairman na hukumar FAAN mai lura da tashoshin jiragen sama.

24/01/2025

Tarihin Asalin Bikin Alkur'ani (Qur'an Festival) Daga Bakin Sheikh Ahmad Gumi

Address

Maiduguri Road, Tarauni LGA
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when SARAUNIYA NEWS posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to SARAUNIYA NEWS:

Share