Abu Raudah Hausa Tv

Abu Raudah Hausa Tv Muna editing na bidiyo da audio. Ku neme mu a 07060831504

Abu Raudah Hausa TV kafa ce da za ta riƙa kawo muku sahihan labarai daga sassa daban-daban dake faɗin Duniya, sannan za ku iya ba mu tallan hajarku domin tallatawa.

DA DUMI-DUMI: Jam’iyyar ADC ta fara zawarcin manyan jiga-jigan siyasar Najeriya gabanin zaɓen 2027. Daga cikin sunayen d...
14/01/2026

DA DUMI-DUMI: Jam’iyyar ADC ta fara zawarcin manyan jiga-jigan siyasar Najeriya gabanin zaɓen 2027. Daga cikin sunayen da ake ambata akwai Goodluck Jonathan, Bukola Saraki, Rabiu Musa Kwankwaso da Seyi Makinde, tare da wasu fitattun ‘yan siyasa a faɗin ƙasar.

Abba Sani Pantami

An sake samun wasu sabbin hare-haren ƴan bindiga a sassan jihar Katsina dai dai lokacin da ake jita-jitar cewa gwamnatin...
13/01/2026

An sake samun wasu sabbin hare-haren ƴan bindiga a sassan jihar Katsina dai dai lokacin da ake jita-jitar cewa gwamnatin jihar na wani shirin sakin ɗimbin ƴan bindigar da ake tsare da su bayan k**a su a lokuta da dama, sakin da mahukuntan ke cewa na ƙarƙashin yarjejeniyar da aka ƙulla a shirin zaman lafiyar jihar.

Me za ku ce.

13/01/2026

NIGERIA 🇳🇬 - 🇲🇦 MOROCCO

Yaya kuke hasashen wasan da za a fafata tsakanin waɗannan ƙungiyoyi guda biyu a gobe Laraba ?

Amurka ta fara turowa Najeriya kayan tallafi na kayan yaƙi.
13/01/2026

Amurka ta fara turowa Najeriya kayan tallafi na kayan yaƙi.

DA DUMI-DUMI: Hukumar EFCC za ta kashe sama da Naira biliyan uku wajen gyaran Ofishin ta, feshin maganin kwari, Abinci d...
12/01/2026

DA DUMI-DUMI: Hukumar EFCC za ta kashe sama da Naira biliyan uku wajen gyaran Ofishin ta, feshin maganin kwari, Abinci da sauran abubuwa, a cikin bajat din 2026.

INEC ta dawo da yin rajistar katin zaɓe a faɗin ƙasaHukumar zaɓe mai zaman kanta ta Ƙasa (INEC) ta sake dawo da yin raji...
05/01/2026

INEC ta dawo da yin rajistar katin zaɓe a faɗin ƙasa

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Ƙasa (INEC) ta sake dawo da yin rajistar masu zaɓe ta dindindin a faɗin Najeriya, inda hakan ke nuna fara zango na biyu na aikin.

INEC ta ce an dawo da aikin ne bayan kammala zangon farko da ya ƙare a ranar 10 ga Disamba, 2025.

A cewar hukumar, sama da ’yan Najeriya miliyan 9.8 ne s**a fara rajistar yanar gizo a zangon farko, yayin da kusan miliyan 2.57 ne aka kammala rajistarsu gaba ɗaya.

Hukumar ta bayyana cewa an yi amfani da tazara tsakanin zangon biyu wajen gudanar da ayyukan doka, ciki har da nuna kundin masu zaɓe domin karɓar ƙorafe-ƙorafe da ƙin amincewa.

INEC ta buƙaci ’yan Najeriya da s**a cancanta su yi amfani da damar da aka samu wajen yin rajista, sauya wurin zaɓe ko sabunta bayanansu. Haka kuma ta nemi waɗanda s**a yi rajista a zangon farko su ci gaba da tantance bayanansu tare da kai rahoton duk wani kuskure.

Sai dai hukumar ta ce har yanzu an dakatar da rajistar masu zaɓe a Jihar Anambra da Abuja sak**akon ci gaba da harkokin zaɓe, inda ta ƙara da cewa za a sanar da sabbin ranakun sake farawa nan gaba.

Daily Nigerian Hausa

05/01/2026

Daga Farkon Shekarar 2026 Zuwa Yanzu, Wani Abin Alkhairi Ka Gamu da shi, Mene ya Ɓata Maka Rai ?

DA DUMI-DUMI: NNPC ta sake rage farashin man fetur inda lita ɗaya ya koma ₦815 daga ₦835 a baya. Wannan shi ne rage fara...
05/01/2026

DA DUMI-DUMI: NNPC ta sake rage farashin man fetur inda lita ɗaya ya koma ₦815 daga ₦835 a baya. Wannan shi ne rage farashi karo na biyu cikin ‘yan makonnin nan, bayan rage ₦80 da aka yi a Disamba 2025.

Rage farashin na zuwa ne sak**akon gasa mai zafi da ta barke bayan shigowar Matatar Dangote, inda wasu gidajen mai k**ar MRS Oil ke sayar da fetur kan ₦739 kowace lita.

Me za ku ce?

Abba Sani Pantami

Kwankwaso ga Abba Gida-Gida: Ka ajiye mana kujerar gwamna sannan ka yi tafiyar ka zuwa APCJagoran Tafiyar Kwankwasiyya k...
04/01/2026

Kwankwaso ga Abba Gida-Gida: Ka ajiye mana kujerar gwamna sannan ka yi tafiyar ka zuwa APC

Jagoran Tafiyar Kwankwasiyya kuma tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bukaci Gwamna Abba Kabiru Yusuf da ya bar kujerar gwamna idan har yana shirin ficewa daga jam’iyyar NNPP.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne yayin wani taro da magoya baya da masu ruwa da tsaki a Kano, a daidai lokacin da ake rade-radin cewa gwamnan na shirin sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Ya ce ba daidai ba ne a kwace wa tafiyar Kwankwasiyya kujerar gwamna daya tilo da take da shi a fadin kasar.

“Idan APC tana da kusan gwamnoni 30, me ya sa sai gwamnan Kano? Shi ne kadai ya rage mana,” in ji Kwankwaso, yana mai cewa duk wanda ke tursasa gwamnan ya sauya sheka ya k**ata ya gaya masa ya bar kujerar gwamna ya tafi.

Tsohon gwamnan ya bayyana halin da ake ciki a siyasar Kano a matsayin abin tayar da hankali, yana mai gargadin cewa rikicin ba zai amfani jihar ba.

Ya ce yana kokarin sasanta al’amura a bayan fage domin hana jihar fadawa matsala.

Kwankwaso ya jaddada cewa gwamnatin NNPP har yanzu tana da lokaci ta yi wa al’umma aiki, yana mai kira da a hada kai maimakon rikici. Ya kuma soki kiran komawa abin da ya kira “Gandujiyya”, yana mai cewa hakan ya nuna rarrabuwar siyasa a jihar.

Ya karyata ikirarin cewa NNPP ba ta da karfi a Kano, yana mai cewa jam’iyyar ce mafi rinjaye.

A karshe, ya gargadi shugabancin APC da kada su raina Kano, yana mai cewa jihar na da muhimmanci kuma ya k**ata a rika mu’amala da ita cikin taka-tsantsan.

Daily Nigerian Hausa

04/01/2026

🥰🥰🥰

Gwamna Yusuf zai sauya sheka zuwa APC a ranar Litinin - RahotoGwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, zai shiga jam’iyya mai mul...
02/01/2026

Gwamna Yusuf zai sauya sheka zuwa APC a ranar Litinin - Rahoto

Gwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, zai shiga jam’iyya mai mulki ta APC a hukumance a ranar Litinin, k**ar yadda DAILY NIGERIAN ta rawaito.

Abba Yusuf, wanda shi kaɗai ne gwamna a jam’iyyar NNPP, ya riga ya isa Abuja domin kammala shirye-shiryen sauya shekar tasa.

Majiyoyi da ke da masaniya kan shirin sauya shekar gwamnan sun shaida wa DAILY NIGERIAN cewa Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, da Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Yitwalda Nentawe, ne za su karɓi gwamnan a Abuja.

Tuni dai an dawo da jagoran APC a Kano, Abdullahi Ganduje, daga wata tafiya da yake yi a Dubai. Haka kuma an umarci shugaban jam’iyyar APC na jihar, Abdullahi Abbas, da ya taƙaita tafiyarsa ta Umara domin ya miƙa katin zama ɗan APC ga gwamnan a mazabarsa ta Diso, da ke Karamar Hukumar Gwale a Jihar Kano, a cikin makon nan.

Daily Nigerian Hausa

A yau ne dai aka gudanar da taron masu ruwa da tsaki na jam'iyyar NNPP tsagin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso a faɗar Ɗariƙa...
02/01/2026

A yau ne dai aka gudanar da taron masu ruwa da tsaki na jam'iyyar NNPP tsagin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso a faɗar Ɗariƙar Kwankwasiyya dake gidan Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da ke Kano, an hangi fuskar Sanata Rufa'i Sani Hanga.

Haka zalika wasu cikin yan majalisun tarayya da Kwamishinonin gwamnatin Kano sun halarci taron.

Kuma an ruwaito cewa a yayin da ake taken jam'iyyar ba a ambaci Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ba.

Hakan dai na ƙara tabbatar da zargi na jan zare tsakanin Madugun da Gwamna Abba.

Address

Brigade Gama Quarters. .
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Abu Raudah Hausa Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Abu Raudah Hausa Tv:

Share