Abu Raudah Hausa Tv

Abu Raudah Hausa Tv Sannan Muna editing na bidiyo da audio. Ku neme mu a 07060831504

Abu Raudah Hausa TV kafa ce da za ta riƙa kawo muku sahihan labarai daga sassa daban-daban dake faɗin Duniya, sannan za ku iya ba mu tallan hajarku domin tallatawa.

Takardun sakamakon jarrabawa sun kone yayin da gobara ta tashi a Kwalejin Fasaha ta Kano Wata gobara ta lalata babban da...
13/05/2026

Takardun sakamakon jarrabawa sun kone yayin da gobara ta tashi a Kwalejin Fasaha ta Kano



Wata gobara ta lalata babban dakin karatu na kwalejin fasaha ta Kano wato Kano State Polytechnic, inda ta kone muhimman takardun karatu, bayanan jarabawa, littattafai da kayan aiki a makarantar da ke Kano.

Lamarin ya faru ne ranar Talata, inda gobarar ta shafi manyan sassan dakin karatun kafin jami’an kashe gobara su samu nasarar shawo kanta.

Har yanzu ba a bayyana adadin asarar da aka yi ba.

Rahotanni sun ce daga cikin abubuwan da gobarar ta lalata akwai bayanan jarabawar dalibai, takardun gudanarwa, kayan koyarwa da sauran kayayyaki masu muhimmanci da aka ajiye a dakin karatun.

Lamarin ya haifar da damuwa kan yiwuwar tangardar da zai iya jawo wa harkokin karatu a makarantar.

Hukumomin makarantar da jami’an agajin gaggawa ba su bayyana musabbabin tashin gobarar ba zuwa yanzu, yayin da ake ci gaba da tantance girman barnar da kuma hanyoyin da za a bi wajen dawo da wasu bayanai da kayayyakin da s**a lalace.

Gobarar na zuwa ne yayin da ake ci gaba da samun yawaitar tashin gobara a gine-ginen gwamnati da cibiyoyi daban-daban a fadin Najeriya cikin watannin baya-bayan nan, lamarin da ke kara jawo hankali kan bukatar inganta matakan kariya da tanadin gaggawa.

Daga Daily Nigerian Hausa

An samu sulhun Siyasa a Kano ta Arewa tsakanin Barau I Jibril da kuma AT Gwarzo, a wani zama da Gwamna Abba Kabir ya jag...
13/05/2026

An samu sulhun Siyasa a Kano ta Arewa tsakanin Barau I Jibril da kuma AT Gwarzo, a wani zama da Gwamna Abba Kabir ya jagoranta a Gidan Gwamnatin Kano.

Zaman ya samu halartar tsohon Gwamnan Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje da Mataimakin Gwamnan Kano Hon. Murtala Sule Galadina Garo da Shugaban Jam'iyyar APC ta Jahar Kano Haruna Doguwa da kuma Hon. Abba Bichi Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Bichi.

A yayin zaman dai AT Gwarzo ya bayyana cewar ya janye aniyarsa ta tsayawa takara a shiyyar Kano ta Arewa inda ya goyi bayan Sanata Barau I Jibril Maliya.

Ya kuke kallon wannan sulhu.

RAHOTO DAGA Arewa Updates 👈Gobara ta ƙone Babban Ɗakin Karatu na Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Kano da ke titin Yahaya G...
13/05/2026

RAHOTO DAGA Arewa Updates 👈

Gobara ta ƙone Babban Ɗakin Karatu na Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Kano da ke titin Yahaya Gusau.

Arewa Updates ta rawaito cewa, wannan na cikin sanarwar da Shugaban Ƙungiyar Ma’aikatan Dakin Karatu ta ƙasa reshen Jihar Kano, Malam Nazir Muhammad, ya fitar.

Sanarwar ta bayyana cewa gobarar ta haddasa asarar muhimman littattafai, kayayyakin aiki da sauran bayanai na ilimi, lamarin da ƙungiyar ta ce babbar koma-baya ne ga harkokin koyarwa, bincike da adana ilimi.

Ƙungiyar ta nuna alhini ga ma’aikatan ɗakin karatun, shugabannin makarantar da ɗalibai, tare da jaddada muhimmancin ɗakin karatun wajen tallafa wa karatu da bincike.

Sanarwar ta yi kira ga gwamnati, hukumomin ilimi da sauran masu hannu da shuni da su bayar da gudunmawa domin sake ginawa da inganta ɗakin karatun.

A baya-bayan nan dai an sha samun tashin gobara a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Kanon.

Arewa Updates ta rubuta muku wannan labari da taimakon fasahar AI.

DA DUMI-DUMI: Vijay Ya Lashe Zaben Tamil NaduShahararren jarumin fim, Vijay, ya kafa tarihi bayan da jam’iyyarsa ta Tami...
04/05/2026

DA DUMI-DUMI: Vijay Ya Lashe Zaben Tamil Nadu

Shahararren jarumin fim, Vijay, ya kafa tarihi bayan da jam’iyyarsa ta Tamilaga Vettri Kazhagam (TVK) ta samu gagarumar nasara a zaɓen majalisar dokokin jihar Tamil Nadu na shekarar 2026.

Jam’iyyar TVK ta samu kujeru sama da 100 a majalisar jihar mai kujeru 234, abin da ya ba ta rinjaye mai ƙarfi tare da karya tsohon tsarin siyasa da ya daɗe yana gudana a jihar.

Wannan nasara ta zo da ban mamaki, inda Vijay wanda ya fito daga harkar fim ya zama ɗaya daga cikin sabbin shugabannin da s**a fi tasiri a siyasar Indiya. A yayin da zai zama sabon Shugaban gwamnatin jihar (Chief Minister) bayan wannan gagarumar nasara.

A cikin wannan zaɓe, Vijay ya kuma yi nasara a mazabunsa guda biyu da ya tsaya takara, inda ya doke manyan ‘yan takara tsofaffin jam’iyyu da tazara mai yawa

Nasarar da Vijay ta kawo ƙarshen tsarin siyasar yankin nasu na kusan shekaru 50 da jam’iyyun gargajiya s**a mamaye, tare da nuna sabon salo na siyasa wanda ya haɗa matasa da talakawa.

Wanne fata za ku yi masa?

Asibitin koyarwa na Aminu Kano AKTH ya fara amfani da tsarin ba da katin shaida ga masu zaman jinyar marasa lafiya a asi...
30/04/2026

Asibitin koyarwa na Aminu Kano AKTH ya fara amfani da tsarin ba da katin shaida ga masu zaman jinyar marasa lafiya a asibitin.

Arewa Updates ta rawaito cewa, wannan na cikin sanarwar da sashen yaɗa labarai na asibitin ya fitar.

Sanarwar ta bayyana cewa kowanne mara lafiya zai samu mutum guda da aka ware domin kula da shi, wanda shi ne za a ba katin shaida, kuma za a rika miƙa katin ga wani idan aka sauya mai jinya.

Shugaban asibitin, Abdurrahman Abba Sheshe ya bayyana cewa an ƙaddamar da tsarin ne domin inganta tsaro da sa ido a cikin asibitin, tare da rage cunkoso da ke hana marasa lafiya samun hutu yadda ya kamata.

Shin ya kuke kallon wannan sabon tsari, kuna ganin ya kamata a yi haka a sauran asibitoci?

Arewa Updates ta rubuta muku wannan labari da taimakon fasahar AI.

Wannan rahoton mun same shi ne daga kafar labarai ta Arewa Updates 👈

Ina al'ummar Kano ta Kudu ku zo ga Tambaya...
29/04/2026

Ina al'ummar Kano ta Kudu ku zo ga Tambaya...

Do Allah jama'a ana cigiyar wannan yaron mai suna Ukasha Musa sunan Mahaifiyarsa Hajara, An kawo Shi daga Kachako.Ya bar...
29/04/2026

Do Allah jama'a ana cigiyar wannan yaron mai suna Ukasha Musa sunan Mahaifiyarsa Hajara, An kawo Shi daga Kachako.

Ya bar makarantar Fadimatu Bintu Musa Litahfizil Qur'an Na'ibawa Unguwar Kwari ranar Litinin 6/4/2026.

Idan Allah yasa an gan Shi a tuntuɓi wadannan lambobin
08034338023
08060840000
08032398154
Ko miƙa shi ga hukuma mafi kusa.

Don Allah Jama'a a taimaka da yaɗa wannan saƙo 🙏

An samu 'Sim Cards' guda 28 a wajen Yan Damfara masu muryar tsofi da sunan Malamai ko Aljanu.~Abdullahi Haruna Kiyawa
15/04/2026

An samu 'Sim Cards' guda 28 a wajen Yan Damfara masu muryar tsofi da sunan Malamai ko Aljanu.

~Abdullahi Haruna Kiyawa

Likita ta mutu bayan ta haifi ƴan-uku a Bayelsa Wata likita mai suna Ere Ogbachi ta mutu bayan ta haifi ƴan-uku  a Jihar...
15/04/2026

Likita ta mutu bayan ta haifi ƴan-uku a Bayelsa

Wata likita mai suna Ere Ogbachi ta mutu bayan ta haifi ƴan-uku a Jihar Bayelsa.

Jaridar Punch ta rawaito cewa bayan ta haihu lafiya a asibitin jami'ar Niger Delta, sai jikin ta ya rikice wanda ya sa aka garzaya da ita zuwa sashen kula da rashin lafiya mai tsanani (ICU) a Federal Medical Centre Yenagoa, inda da misalin karfe 2:45 na safiyar jiya Talata, ta ce ga garin ku nan.

Dangin ta sun bayyana cewa likitoci sun yi iya kokarinsu don ceton rayuwarta, amma ta shiga wani mawuyacin hali ne, inda daga ƙarshe ta cika.

Punch ta ce Ere ta mutu ta bar sana'a+santalan jariran mata guda uku rigis, lamarin da ya jefa yan uwan ta da mai gidan ta cikin alhini.

Daily Nigerian Hausa

07/04/2026

Saurara ka ji 👂👈

DA ƊUMI-ƊUMI: Tsohon ɗan takarar gwamnan Jihar Kano a jam’iyyar APC, Nasiru Yusuf Gawuna, ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar ...
31/03/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Tsohon ɗan takarar gwamnan Jihar Kano a jam’iyyar APC, Nasiru Yusuf Gawuna, ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar ADC, tare da karɓar katin jam’iyyar a hukumance a Mazaɓarsa ta Gawuna a yau Talata a gaban Jagoran ɗariƙar kwankwasiyya Rabiu Musa Kwankwaso
Wani fata kuke yi musu...?

Address

Brigade Gama Quarters. .
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Abu Raudah Hausa Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Abu Raudah Hausa Tv:

Share