25/08/2026
Shugaban Kasar Najeriya Bola Tinubu ya taya Al'ummar Musulmi Murnar Mauludi, ya yi Kira ga Jama'a da suyi Koyi da Kyawawan Ɗabi’un Annabi Muhammad (SAW)
Shugaban Ƙasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya taya al’ummar Musulmi murnar bikin Mauludin Annabi Muhammad (SAW), tare da kira gare su da su yi koyi da kyawawan koyarwa da ɗabi’un Manzon Allah.
A cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Talata, Tinubu ya ce bikin Mauludi ya k**ata ya kasance lokaci na yin tunani, addu’a da ɗaukar darussa daga rayuwar Annabi Muhammad (SAW).
Shugaban Ƙasar ya bayyana cewa rayuwar Annabi Muhammad (SAW) na ƙunshe da darussa masu muhimmanci na ibada, haƙuri, juriya, tawali’u da sadaukar da kai.
Ya kuma yi kira ga shugabannin addini da su ƙarfafa mabiyansu wajen amfani da waɗannan kyawawan halaye wajen yi wa ƙasa hidima.
Tinubu ya buƙaci masu gudanar da bukukuwan Mauludi da su tallafa wa mabukata da marasa galihu, tare da yin addu’o’in kawo ƙarshen matsalar tsaro da sauran ƙalubalen da ke addabar wasu sassan Najeriya.
Shugaban Ƙasar ya yi fatan bikin Mauludin bana zai ƙara ƙarfafa haɗin kai, tausayi da zaman lafiya tsakanin al’ummar Najeriya.