03/05/2026
Ranar Yancin Yan Jarida ta Duniya: SERAP da NGE Sun Bukaci Tinubu Yakare Yan Jaridu Daga Barazanar Tsaro Da Suke Fuskata.
Kungiyar kare hakkin jama’a ta SERAP da Kungiyar Editocin Najeriya (NGE) sun bukaci gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, gwamnoni da kuma ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, dasu gaggauta daukar matakan kare ‘yancin yan jarida tare da kawo karshen matsalar rashin tsaro da take kara muni a sassan Najeriya.
Kungiyoyin biyu sun bayyana hakan ne a wata sanarwa da s**a fitar domin bikin Ranar yancin yan jarida ta duniya ta shekarar 2026, bayan wani taro da s**a shirya a otal din Radisson Blu dake Ikeja a jihar Legas.
A cewarsu, tabbatar da yancin aikin jarida da kare sahihancin bayanai na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya, tsaro da dorewar dimokuradiyya a Najeriya.
SERAP da NGE sun nuna matukar damuwa kan yadda akeci gaba da fama da kashe kashe, sace sacen mutane, cin zarafin mata, da lalata dukiyoyi a jihohin Benue, Borno, Plateau, Sokoto da Kwara.
Kungiyoyin sun bayyana cewa dubban mutane sun rasa rayukansu yayin da miliyoyin jama’a s**a rasa matsugunansu sak**akon hare hare da rikice rikicen da s**a addabi yankunan karkara, inda mata da yara s**a fi fuskantar wahalhalu.
Sun kuma ce kin cigaba da rashin hukunta masu aikata laifuka na kara raunana amincewar jama’a ga gwamnati tare da kawo barazana ga tsarin dimokuradiyya da kare hakkin bil’adama.
SERAP da NGE sun jaddada cewa gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohi na da nauyin kare ‘yan jarida da sauran jama’a bisa kundin tsarin mulkin Najeriya da kuma dokokin kasa da kasa na kare hakkin dan Adam.
Hakazalika, sun bukaci hukumomi su tabbatar da bincike mai inganci kan take hakkin jama’a tare da hukunta masu hannu a rikice-rikicen da kuma wadanda ke daukar nauyinsu domin tabbatar da adalci ga wadanda abin ya shafa.