Jaridar Nagartacciya

Jaridar Nagartacciya Wallafa sahihan labarai shine muradin mu

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Anambra zata fara Fallasa masu Yada Ƙarya da Nufin Tayar da Hankalin Jama’aRundunar ‘Yan Sand...
23/07/2025

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Anambra zata fara Fallasa masu Yada Ƙarya da Nufin Tayar da Hankalin Jama’a

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Anambra ta bayyana cewa za ta fara gano da fallasa mutane da ƙungiyoyin da ke yada bayanan tsaro marasa tushe a kafafen sada zumunta da nufin tayar da hankalin jama’a da bata sunan jami’an tsaro.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SP Tochukwu Ikenga, ya ce irin wannan aiki na iya janyo tangarda ga tsare-tsaren tsaro ya ce rundunar za ta bi duk hanyoyin doka ciki har da tanadin dokar Cybercrime ta 2015 don hukunta masu laifi.

Rundunar ta bukaci jama’a da su rika tantance bayanai kafin yada su, tare da yin hadin gwiwa da ‘yan sanda ta hanyar kai rahoton duk wani abu da ke da alaƙa da barazana ga tsaro.

’Yan Sanda Sun K**a Masu Safarar Mak**ai a Benue, Sun Kwato Bindigu da HarsashiRundunar ’Yan Sandan Najeriya ta cafke wa...
23/07/2025

’Yan Sanda Sun K**a Masu Safarar Mak**ai a Benue, Sun Kwato Bindigu da Harsashi

Rundunar ’Yan Sandan Najeriya ta cafke wasu da ake zargi da safarar mak**ai zuwa hannun ’yan bindiga a Benue da wasu jihohin Arewa ta Tsakiya. Jami’an FID-IRT sun kai samame a iyakar Nasarawa da Benue, inda s**a kwato bindigu GPMG 2, AK-47 guda 12 da harsashi 2,222.

An k**a wasu mutane uku, ciki har da Abubakar Isah da Ibrahim “Chelsea”, da kuma babban dillalin mak**ai Jacob Adikwu, wanda aka same shi da bindigu da roket launcher. An tabbatar da cewa mak**an na daf da kaiwa hannun wani shugaban ’yan bindiga mai suna Dan Hassan.

Sufeto Janar, IGP Kayode Egbetokun, ya jinjinawa jami’an, tare da tabbatar da ci gaba da yaki da ta’addanci a fadin Najeriya.

YANZU- YANZU: An k**a wani mahauci yana shirya naman kare a matsayin tsire a Kano, kusa da Sakatariyar Audu Bako.
23/07/2025

YANZU- YANZU: An k**a wani mahauci yana shirya naman kare a matsayin tsire a Kano, kusa da Sakatariyar Audu Bako.

Gwamna Namadi ya sanya hannu kan dokar kafa Hukumar Hisbah a JigawaGwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya sanya hannu kan...
23/07/2025

Gwamna Namadi ya sanya hannu kan dokar kafa Hukumar Hisbah a Jigawa

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya sanya hannu kan dokar da ta kafa Hukumar Hisbah a matsayin hukuma ta doka a jihar.

An gudanar da bikin sanya hannun ne a Dutse, babban birnin jihar, tare da halartar Mataimakin Gwamna Aminu Usman, da wasu jiga-jigan majalisar dokoki ta jihar.

Wannan doka za ta bai wa hukumar Hisbah cikakken ikon aiwatar da ayyukanta na ƙarfafa tarbiyya, inganta ɗabi’a da adalci a cikin al’umma.

Gwamna Namadi ya ce kafa hukumar zai taimaka wajen ganin an samu zaman lafiya da daidaiton zamantakewa. Ya bukaci jami’an Hisbah da su gudanar da aikinsu cikin gaskiya, adalci da tsoron Allah.

Wannan mataki na zuwa ne bayan fiye da watanni takwas da aka fara nazarin kudirin dokar tun daga shekarar 2024.

Gwamna Uzodimma Ya Kaddamar da Kwamitin kula da Iyaka a Jihar ImoGwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, ya kaddamar da kwamit...
22/07/2025

Gwamna Uzodimma Ya Kaddamar da Kwamitin kula da Iyaka a Jihar Imo

Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, ya kaddamar da kwamitin iyaka mai mambobi 15 tare da umartar su da su tabbatar da zaman lafiya a yankunan da rikicin iyaka ke haddasa tashin hankali.

Mataimakiyar Gwamna, Lady Chinyere Ekomaru, ita ce shugabar kwamitin da aka kaddamar a dakin taro na New Exco Chambers, dake Gidan Gwamnati Owerri.

Gwamna Uzodimma ya jaddada cewa kwamitin na da tushe a kundin tsarin mulki, kuma ya bukaci mambobin da su yi amfani da doka wajen warware matsalolin iyaka cikin lumana da adalci.

Kungiyar Dillalan Motoci ta kai ziyara ga Mataimakin Babban Sufeton Ƴan Sanda mai kula da Shiyya ta daya Kungiyar dillal...
22/07/2025

Kungiyar Dillalan Motoci ta kai ziyara ga Mataimakin Babban Sufeton Ƴan Sanda mai kula da Shiyya ta daya

Kungiyar dillalan motoci ta jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin shugabanta Alhaji Madugu Ibrahim Madugu, ta kai ziyarar girmamawa ga mataimakin Babban Sufeton ‘Yan Sanda na shiyyar ta daya AIG Ahmed Garba, a ofishinsa.

Ziyarar ta gudana ne da nufin neman haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro da masu kasuwanci domin tabbatar da tsari da doka a harkar kasuwancin motoci a jihar.

A yayin tattaunawar, Alhaji Madugu ya bayyana cewa sun zo ne domin ƙarfafa dangantaka da ‘yan sanda da kuma neman goyon bayansu wajen magance kalubalen da ke fuskantar harkar dillancin motoci. Ya jaddada muhimmancin samun tsaro da doka a kasuwannin mota domin amfanin dukkan masu ruwa da tsaki.

Da yake nasa jawabin, AIG Ahmed Garba ya yaba da wannan ziyara tare da ƙarfafa musu gwiwa wajen ci gaba da nuna irin wannan jajircewa. Ya ba da shawarar cewa kungiyar ta yi amfani da lauyoyi don tabbatar da bin ka’ida da doka a kasuwancin su. Haka kuma, ya bukaci su rika bai wa ‘yan sanda hadin kai da kai rahoton duk wani abu da ke nuna alamar barazana.

Ya ce rundunar ‘yan sanda ta shiyya ta daya za ta ci gaba da ba da goyon baya don tabbatar da zaman lafiya da kare martabar sana’ar dillancin mota a jihar Kano da kewayenta.

An kammala taron da gabatar da kyautar girmamawa daga shugaban kungiyar zuwa ga AIG, a matsayin alamar godiya da yabo bisa shugabancinsa da kyakkyawan fata ga cigaban kasuwanci mai tsafta.

Kungiyar 'Yan Jaridu ta Abuja ta Karrama Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar Anambra CP Orutugu da lambar Yabo ta Gwarzon Sheka...
22/07/2025

Kungiyar 'Yan Jaridu ta Abuja ta Karrama Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar Anambra CP Orutugu da lambar Yabo ta Gwarzon Shekara

Rundunar 'yan sanda ta jihar Anambra ta bayyana jin daɗinta kan yadda Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar, CP Ikioye Orutugu fwc, MNIPS, PhD, ya samu lambar yabo ta “Best Crime Fighter – Man of the Year 2025” daga kungiyar 'yan jarida ta Najeriya (NUJ), reshen babban birnin tarayya, Abuja.

An karrama CP Orutugu ne a wani taro na musamman da aka gudanar a dakin taro na Transcorp Hilton Hotel dake Abuja.

A cewar NUJ FCT, CP Orutugu ya cancanci wannan lamba bisa kwazonsa wajen jagorantar yaki da aikata laifuka a jihar Anambra, inda aka samu nasarori masu yawa wajen murkushe miyagun laifuka, rushe kungiyoyin ta’addanci, da ƙarfafa tsarin hulɗa da al’umma da sauran hukumomin tsaro.

Cikin sanarwar da kakakin rundunar ‘yan sanda na jihar Anambra, SP Tochukwu Ikenga, ya fitar, rundunar ta bayyana wannan karramawa a matsayin gagarumin nasara ga rundunar baki ɗaya, ba wai CP Orutugu kaɗai ba.

Yayin karɓar lambar yabon CP Orutugu ya sadaukar da ita ga dakarun sa masu sadaukarwa da ƙwazo, yana mai nanata aniyar sa na ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a a jihar.

Taron ya samu halartar wakilin Sufeto Janar na 'Yan Sanda, wanda Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ƴan sanda na kasa, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya wakilta, tare da wasu manyan jami’ai daga Shiyya ta 7, da kuma wakilai daga hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki a sha’anin tsaro.

Nan kamfanin kera boma-bomai ne na atilare, a Chilwell (UK). wanda mata zalla ne ke aiki a kamfanin a lokacin yakin duni...
22/07/2025

Nan kamfanin kera boma-bomai ne na atilare, a Chilwell (UK). wanda mata zalla ne ke aiki a kamfanin a lokacin yakin duniya na farko shekarar 1916.

Daga : Muhammad Cisse

YANZU YANZU- Hauwa Halliru Gwangwazo ta bayyana damuwa kan yadda ake buɗe shafukan Facebook na ƙarya da ke amfani da sun...
22/07/2025

YANZU YANZU- Hauwa Halliru Gwangwazo ta bayyana damuwa kan yadda ake buɗe shafukan Facebook na ƙarya da ke amfani da sunanta da hotunanta ba tare da izininta ba.

Ta jaddada cewa shafinta na gaskiya guda ɗaya tilo shine:

Hauwa Halliru Gwangwazo – mai mabiya sama da 200,000.

“Ban da alaƙa da kowanne shafi da ba nawa ba. Ina roƙon jama’a su kauce wa shafukan bogi tare da gujewa amsa duk wata hulɗa daga gare su,” in ji ta.

Hauwa na cikin shirin tantance (verifying) shafinta domin hana ruɗani, kuma ta gode wa jama’a bisa goyon baya da fahimtarta.

Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Kano Ya Jaddada Kudirin yin Aiki Tare da Al’ummaKwamishinan Ƴan Sanda na Jihar Kano, CP Ib...
22/07/2025

Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Kano Ya Jaddada Kudirin yin Aiki Tare da Al’umma

Kwamishinan Ƴan Sanda na Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, PhD, ya karɓi baƙuncin Shugabanni daga Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (CCB), kungiyar Mu Hadu Mu Gyara, da kuma shugabannin makarantar Police Children School (PCS) da ke Bompai, Kano.

Ziyarar da ta gudana a ranar Talata, 22 ga Yuli, 2025 a ofishin Kwamishinan ‘Yan Sandan da ke Bompai, inda aka tattauna batutuwa da dama da s**a shafi haɗin gwiwa da kyautata alakar aiki tsakanin rundunar.

Babbar Daraktar CCB a Kano, Hajiya Hadiza Larai Ibrahim, ta bayyana cewa manufar ziyarar ita ce kara karfafa alaƙar aiki tsakanin hukumar da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da gaskiya, rikon amana da yaki da cin hanci a cikin gwamnati. Ta ce akwai bukatar hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu domin tabbatar da bin ka’ida da ladabtar da jami’an gwamnati.

Shi ma Shugaban kungiyar Mu Hadu Mu Gyara, Alhaji Sunusi Balarabe, ya jinjinawa Kwamishinan bisa kokarinsa na tabbatar da tsaro da kyautata alaƙar ‘yan sanda da al’umma. Ya bayyana cewa an samu sauye-sauye da dama da s**a habaka zaman lafiya da fahimtar juna a tsakanin jami’an tsaro da al’umma.

A nasa bangaren, Shugaban makarantar PCS, Malam Hassan Abu Sadiq, ya ce sun kawo ziyarar ne domin gaishe da sabon kwamishina da kuma tattauna hanyoyin inganta walwala da ilimin ‘ya’yan ‘yan sanda a makarantar. Ya yaba da irin jagoranci da sauye-sauyen da CP Bakori ke kawo wa a rundunar.

A cikin jawabinsa na maraba, CP Ibrahim Adamu Bakori ya nuna godiya ga baƙin nasa bisa irin goyon bayan da suke bai wa rundunar. Ya bayyana cewa rundunar na ci gaba da aiwatar da tsare-tsaren community policing, tare da jan hankalin al’umma domin samar da ingantaccen tsaro, k**ar yadda umarnin Sufeto Janar na Ƴan Sanda, IGP Kayode Egbetokun, ya tanada.

Nan ba da daɗewa ba kamfanin Coca Cola zai samar da coca cola wacce za'a yi ta da rake. Amma za'a fara sayar da ita a Am...
22/07/2025

Nan ba da daɗewa ba kamfanin Coca Cola zai samar da coca cola wacce za'a yi ta da rake. Amma za'a fara sayar da ita a Amurka, sannan sauran ƙasashe su biyo baya.

Sukari a Amurka ya yi muguwar tsadar da zai sa dole a koma sarrafa rake don yin abubuwa masu zaƙi a ƙasar.

Hussaini Umar Najiddah

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Nagartacciya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share