22/07/2025
Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Kano Ya Jaddada Kudirin yin Aiki Tare da Al’umma
Kwamishinan Ƴan Sanda na Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, PhD, ya karɓi baƙuncin Shugabanni daga Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (CCB), kungiyar Mu Hadu Mu Gyara, da kuma shugabannin makarantar Police Children School (PCS) da ke Bompai, Kano.
Ziyarar da ta gudana a ranar Talata, 22 ga Yuli, 2025 a ofishin Kwamishinan ‘Yan Sandan da ke Bompai, inda aka tattauna batutuwa da dama da s**a shafi haɗin gwiwa da kyautata alakar aiki tsakanin rundunar.
Babbar Daraktar CCB a Kano, Hajiya Hadiza Larai Ibrahim, ta bayyana cewa manufar ziyarar ita ce kara karfafa alaƙar aiki tsakanin hukumar da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da gaskiya, rikon amana da yaki da cin hanci a cikin gwamnati. Ta ce akwai bukatar hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu domin tabbatar da bin ka’ida da ladabtar da jami’an gwamnati.
Shi ma Shugaban kungiyar Mu Hadu Mu Gyara, Alhaji Sunusi Balarabe, ya jinjinawa Kwamishinan bisa kokarinsa na tabbatar da tsaro da kyautata alaƙar ‘yan sanda da al’umma. Ya bayyana cewa an samu sauye-sauye da dama da s**a habaka zaman lafiya da fahimtar juna a tsakanin jami’an tsaro da al’umma.
A nasa bangaren, Shugaban makarantar PCS, Malam Hassan Abu Sadiq, ya ce sun kawo ziyarar ne domin gaishe da sabon kwamishina da kuma tattauna hanyoyin inganta walwala da ilimin ‘ya’yan ‘yan sanda a makarantar. Ya yaba da irin jagoranci da sauye-sauyen da CP Bakori ke kawo wa a rundunar.
A cikin jawabinsa na maraba, CP Ibrahim Adamu Bakori ya nuna godiya ga baƙin nasa bisa irin goyon bayan da suke bai wa rundunar. Ya bayyana cewa rundunar na ci gaba da aiwatar da tsare-tsaren community policing, tare da jan hankalin al’umma domin samar da ingantaccen tsaro, k**ar yadda umarnin Sufeto Janar na Ƴan Sanda, IGP Kayode Egbetokun, ya tanada.