Jaridar Nagartacciya

Jaridar Nagartacciya Wallafa sahihan labarai shine muradin mu, kuna da damar turo mana abubuwan da suke faruwa a inda kuke a lambar ta Whatsapp 08084944703

Ranar Yancin Yan Jarida ta Duniya: SERAP da NGE Sun Bukaci Tinubu Yakare Yan Jaridu Daga Barazanar Tsaro Da Suke Fuskata...
03/05/2026

Ranar Yancin Yan Jarida ta Duniya: SERAP da NGE Sun Bukaci Tinubu Yakare Yan Jaridu Daga Barazanar Tsaro Da Suke Fuskata.

Kungiyar kare hakkin jama’a ta SERAP da Kungiyar Editocin Najeriya (NGE) sun bukaci gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, gwamnoni da kuma ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, dasu gaggauta daukar matakan kare ‘yancin yan jarida tare da kawo karshen matsalar rashin tsaro da take kara muni a sassan Najeriya.

Kungiyoyin biyu sun bayyana hakan ne a wata sanarwa da s**a fitar domin bikin Ranar yancin yan jarida ta duniya ta shekarar 2026, bayan wani taro da s**a shirya a otal din Radisson Blu dake Ikeja a jihar Legas.

A cewarsu, tabbatar da yancin aikin jarida da kare sahihancin bayanai na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya, tsaro da dorewar dimokuradiyya a Najeriya.

SERAP da NGE sun nuna matukar damuwa kan yadda akeci gaba da fama da kashe kashe, sace sacen mutane, cin zarafin mata, da lalata dukiyoyi a jihohin Benue, Borno, Plateau, Sokoto da Kwara.

Kungiyoyin sun bayyana cewa dubban mutane sun rasa rayukansu yayin da miliyoyin jama’a s**a rasa matsugunansu sak**akon hare hare da rikice rikicen da s**a addabi yankunan karkara, inda mata da yara s**a fi fuskantar wahalhalu.

Sun kuma ce kin cigaba da rashin hukunta masu aikata laifuka na kara raunana amincewar jama’a ga gwamnati tare da kawo barazana ga tsarin dimokuradiyya da kare hakkin bil’adama.

SERAP da NGE sun jaddada cewa gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohi na da nauyin kare ‘yan jarida da sauran jama’a bisa kundin tsarin mulkin Najeriya da kuma dokokin kasa da kasa na kare hakkin dan Adam.

Hakazalika, sun bukaci hukumomi su tabbatar da bincike mai inganci kan take hakkin jama’a tare da hukunta masu hannu a rikice-rikicen da kuma wadanda ke daukar nauyinsu domin tabbatar da adalci ga wadanda abin ya shafa.

Innalillahi wainnailaihi Raji’unAllah yayi wa mahaifin ɗan takarar Sanatan Kano ta Tsakiya, Abdussalam Abdulkarim Zaura ...
03/05/2026

Innalillahi wainnailaihi Raji’un

Allah yayi wa mahaifin ɗan takarar Sanatan Kano ta Tsakiya, Abdussalam Abdulkarim Zaura (A.A. Zaura), Alhaji Abdulkarim Saleh Zaura rasuwa.

Alhaji Abdulkarim Saleh Zaura mai shekaru 108, ya rasu a safiyar Lahadin nan bayan ya sha fama da jinya.

Za a gudanar da jana’izarsa da misalin ƙarfe 1 na rana a garin Zaura da ke ƙaramar hukumar Ungogo.

NDLEA Ta Cafke Wasu Tsofaffin Masu Safarar Miyagun kwayoyi Masu Shekaru 83 Da 78Hukumar Yaki dasha da fataucin miyagun k...
03/05/2026

NDLEA Ta Cafke Wasu Tsofaffin Masu Safarar Miyagun kwayoyi Masu Shekaru 83 Da 78

Hukumar Yaki dasha da fataucin miyagun kwayoyi ta Najeriya, National Drug Law Enforcement Agency (NDLEA), ta sanar da cafke wasu tsofaffin mutane biyu masu shekaru 83 da 78 bisa zargin safarar miyagun ƙwayoyi, yayin da takeci gaba da sumamen da takeyi a sassa daban daban na ƙasar nan.

Mai magana da yawun hukumar, Femi Babafemi, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa daya fitar ranar Lahadi.

A jihar Abia, jami’an NDLEA sun k**a wani dattijo mai shekaru 83 mai suna Pa John Ofiel a yankin Samek dake Aba bayan samun bayanan sirri cewa yana safarar miyagun ƙwayoyi. An kwato gram 700 na skunk da aka rarraba cikin ƙananan buhunhuna daga hannunsa. Tsohon ya bayyana cewa kafin shiga harkar safarar ƙwayoyi yana aikin gyaran takalma.

Haka kuma a jihar Ekiti, an k**a wani dattijo mai shekaru 78 mai suna Ogunjobi Samuel a gidansa da ke Ilupeju-Ekiti tare da gram 350 na tabar wiwi.

A jihar Oyo kuwa, jami’an hukumar sun k**a wasu mata biyu, Rebecca King da Olaniyan Opeyemi, bayan k**a su da kilogram 1.925 na wani nau’in tabar wiwi mai ƙarfi da ake kira Colorado.

Kazalika, jami’an NDLEA sun cafke wani da ake zargi da shahara wajen safarar ƙwayoyi mai suna Taofik Adeyemi a Ibadan tare da wani abokinsa, inda aka samu fiye da kilogram uku na skunk da kuma mota kirar Toyota Camry.

A wasu samame daban daban da aka gudanar a jihohin Osun, Borno, Kaduna, Jigawa, Lagos da Edo, jami’an hukumar sun k**a mutane da dama tare da kwato dimbin tabar wiwi, Tramadol da sauran miyagun ƙwayoyi.

Shugaban NDLEA, Mohamed Buba Marwa, ya yaba wa jami’an hukumar bisa nasarorin da s**a samu wajen rage yawaitar miyagun ƙwayoyi tare daci gaba da wayar dakan al’umma kan illolinsu.

Kamfanin Dangote Ya Musanta Rikici Tsakanin Dangote Da Elumelu Inda, Yayi Barazanar Daukar Matakin Shari’a.Kamfanin Dang...
03/05/2026

Kamfanin Dangote Ya Musanta Rikici Tsakanin Dangote Da Elumelu Inda, Yayi Barazanar Daukar Matakin Shari’a.

Kamfanin Dangote Group ya musanta rade radin dake yawo cewa akwai sabani tsakanin attajirin Afirka Aliko Dangote da shugaban bankin United Bank for Africa, Tony Elumelu, yana mai bayyana labarin a matsayin karya da bata suna.

Rahotannin sun samo asali ne daga wani sako da lya yadu a dandalin X, inda akayi zargin cewa Dangote ya fuskanci matsalar kudi yayin aikin matatar mai ta Dangote a shekarar 2021, kuma ya nemi tallafin wasu attajirai ciki har da Femi Otedola da Abdulsamad Rabiu.

Saidai a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na kamfanin, Anthony Chiejina, ya fitar a ranar Asabar, yace babu gaskiya a zargin, yana mai jaddada cewa Dangote bai taba yin irin wadannan kalamai ba.

Kamfanin ya kuma bayyana cewa aikin matatar man fetur ta Dangote Petroleum Refinery & Petrochemicals ba a gina shi da bashin abokai ba, yana mai cewa dukkan ikirarin da ake yadawa na nufin bata suna ne kawai.

Dangote Group ya kara da cewa dangantaka tsakanin Dangote da Elumelu tana nan daram kuma babu wata matsala a tsakaninsu.

Haka kuma kamfanin ya yi gargadin cewa zai iya daukar matakin shari’a kan duk wanda aka samu da hannu wajen kirkira ko yada bayanan karya da sunan Dangote.

Big shout out to my newest top fans! 💎 Labaran Mukhtar, Jibrin Munirat, Aminu Muhammad SulaimanDrop a comment to welcome...
03/05/2026

Big shout out to my newest top fans! 💎 Labaran Mukhtar, Jibrin Munirat, Aminu Muhammad Sulaiman

Drop a comment to welcome them to our community, fans

Kwankwaso Ya Musanta Jita jitar Hada Kai da Obi, Yace Ba a Yanke Shawara Kan 2027 BaTsohon gwamnan jihar Kano kuma jagor...
03/05/2026

Kwankwaso Ya Musanta Jita jitar Hada Kai da Obi, Yace Ba a Yanke Shawara Kan 2027 Ba

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran siyasar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ya musanta rahotannin dake yawo cewa ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a zaben shekarar 2027.

A wata sanarwa daya fitar a daren Asabar, Kwankwaso ya bayyana karara cewa bai amince da kowane dan takara a matsayin mataimakinsa ba, yana mai cewa dukkan rade radin da ake yadawa basu da tushe.

Jita jitar siyasar Kwankwaso ta kara karfi ne tun bayan taron kolin jam’iyyun adawa da aka gudanar a Ibadan a watan da ya gabata. An dade ana alakanta shi da yiwuwar kafa tikitin hadin gwiwa da Peter Obi domin zaben 2027, inda magoya bayan bangarorin biyu ke yada fastocin yakin neman zabe a kafafen sada zumunta.

Rahotanni sun kuma yi ikirarin cewa Kwankwaso da Obi na dab da ficewa daga jam’iyyar ADC zuwa wata jam’iyya mai suna NDC saboda rikicin cikin gida dake addabar ADC.

Sai dai Kwankwaso yace babu wata matsaya da aka cimma kan makomarsa ta siyasa.

Mun lura da rahotannin kafafen yada labarai da ke nuna yiwuwar sauya sheka a cikin jam’iyyar ADC saboda matsalolin da ke addabar jam’iyyar,” in ji sanarwar.

“Saboda bayanan da ke ta yawo marasa tushe, ina sanar da jama’a cewa babu wata cikakkiyar shawara da aka dauka dangane da makomata ta siyasa ko ta magoya bayana.”

Kwankwaso ya kara da cewa har yanzu jam’iyyar ADC bata yanke hukunci kan yadda za ayi rabon tikitin shugaban kasa na 2027 ba, yana mai jaddada cewa bai bayyana aniyarsa ta tsayawa takara ba kuma bai goyi bayan kowane ba.

Yace duk wani labari dake cewa ya dauki matsaya kan zaben shugaban kasa “gaggawa ne kuma marar tushe.”

A wani bangare kuma, Kotun Koli ta Najeriya a ranar Alhamis ta soke hukuncin Kotun Daukaka Kara da ya bukaci bangarorin da ke rikicin shugabancin ADC su ci gaba da kasancewa yadda suke kafin rikicin ya barke.

Kwamitin alkalai biyar karkashin jagorancin Mohammed Garba ya umurci bangaren da David Mark ke jagoranta da su koma Babbar Kotun Tarayya domin ci gaba da sauraron karar.

Kwankwaso ya bayyana cewa hukuncin ya jefa jam’iyyar ADC cikin wani mawuyacin hali.

“Mun bar NNPP ne saboda matsalolin shari’a da wasu s**a haddasa daga waje, wanda ya sanya ci gaba da zama cikin jam’iyyar ya zama hadari. Yanzu ADC ma ta fada irin wannan yanayi,” in ji shi.

Ya kara da cewa shi da sauran manyan masu ruwa da tsaki sun fara tattaunawa da shugabannin wasu jam’iyyu ciki har da NDC da PRP domin duba mafi kyawun matakin kare muradun dimokuradiyya.

Kwankwaso ya kuma bayyana cewa rashin halartar wasu tarukan ADC na baya-bayan nan ya samo asali ne daga wasu uzurorin kashin kai da ya sanar da shugabancin jam’iyyar tun farko, ba wai saboda yana shirin sauya sheka ba.

A karshe, ya tabbatar da cewa duk wata cikakkiyar matsaya game da makomarsa ta siyasa za a sanar da ita ne ta hanyoyin hukuma.

Barkamu Da Hutun Karshen Mako Tare Dafatan Alheri Gareku Tare Da Jaridar Nagartacciya  Kugaya mana Daga Wacce Jaha Kuke ...
03/05/2026

Barkamu Da Hutun Karshen Mako Tare Dafatan Alheri Gareku Tare Da Jaridar Nagartacciya Kugaya mana Daga Wacce Jaha Kuke Bibiyar Mu A Halin Yanzu Sannan Kuma Mai Yake Faruwa A Yankunan Ku ?

Dakarun Soji Sun Hallaka Fitattun ’Yan Ta’adda Hudu a Katsina, Sun Kwato Mak**ai da KudiDakarun rundunar sojin Najeriya ...
02/05/2026

Dakarun Soji Sun Hallaka Fitattun ’Yan Ta’adda Hudu a Katsina, Sun Kwato Mak**ai da Kudi

Dakarun rundunar sojin Najeriya ta 17 Brigade dake jihar Katsina sun samu gagarumar nasara a wani samame da s**a kai, inda s**a hallaka wasu fitattun ’yan ta’adda hudu tare da kwato mak**ai, babura da kudade masu yawa.

Kwamishinan Harkokin Tsaro da Cikin Gida na jihar Katsina, Dakta Nasir Mu’azu, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa daya fitar, inda yace lamarin ya faru ne ranar Juma’a yayin da dakarun ke gudanar da sintiri na yaki a hanyar Turare zuwa Yantumaki.

A cewarsa, dakarun sun gamu da harin ’yan ta’addan da misalin karfe 11:40 na safe, amma cikin gaggawa s**a mayar da martani tare da bin maharan har s**a hallaka su baki daya ba tare da an samu asarar rai ko rauni a bangaren jami’an tsaro ba.

Dakta Mu’azu ya bayyana sunayen ’yan ta’addan da aka kashe da s**a hada da Bishir Holami, Jamilu Baki, Ibrahim Doro da Abdurraman Maje. Yace mutanen na daga cikin manyan kwamandojin da ake zargi da jagorantar hare hare masu muni a kauyukan Gobirawa, Raddawa, Kuki da sauran yankuna a kananan hukumomin Dutsinma da Matazu.

Ya kara da cewa jami’an tsaron sun kwato bindiga kirar AK-47 guda daya dauke da mujalla da harsasai biyar na musamman kirar 7.62mm, babura guda biyu, wayoyin hannu guda hudu, da wayoyin Android guda uku dake dauke da hotunan ’yan ta’addan sanye da kayan soja, tare da kudade har naira 153,400.

Sanarwar tace an mika wayoyin da aka kwato ga hukumomin da abin ya shafa domin gudanar da binciken fasaha domin gano karin bayanai kan ayyukan kungiyar.

Kwamishinan ya bayyana cewa kashe wadannan kwamandoji babbar illa ce ga shugaban ’yan bindigar nan Muhammadu Fulani, wanda ake zargi da addabar yankunan Matazu, Musawa, Charanchi da Kankia.

Ya ce nasarar ta nuna irin kudurin gwamnatin Gwamna Dikko Umaru Radda na kawo karshen matsalar tsaro da kuma dawo da zaman lafiya a dukkan sassan jihar Katsina.

Gwamnatin jihar baza ta yi kasa a gwiwa ba har sai an tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma gaba daya. Dakarun tsaro naci gaba da kai farmaki, kuma irin wannan nasara na nuna cewa ana samun ci gaba mai ma’ana,” in ji sanarwar.

Haka kuma gwamnatin jihar tayi kira ga al’umma da suci gaba da bai wa jami’an tsaro hadin kai tare da samar da sahihan bayanai, tana mai cewa hakan na taka muhimmiyar rawa wajen samun nasarorin da ake samu a yaki da ’yan ta’adda a jihar.

Harin Drone a Khartoum Ya Hallaka Fararen Hula Biyar Wanda  Kungiyar NGO Ta Zargi RSF Dakai Harin.Akalla fararen hula bi...
02/05/2026

Harin Drone a Khartoum Ya Hallaka Fararen Hula Biyar Wanda Kungiyar NGO Ta Zargi RSF Dakai Harin.

Akalla fararen hula biyar ne s**a rasa rayukansu bayan wani harin jirgi mara matuki (drone) da akace dakarun RSF s**a kai a birnin Khartoum na kasar Sudan, k**ar yadda wata kungiyar kare hakkin bil’adama mai suna Emergency Lawyers ta bayyana.

Kungiyar tace harin, wanda ya faru a ranar Asabar, shine na biyu da aka kai a babban birnin cikin mako guda, duk da cewa birnin ya samu kwanciyar hankali bayan sojojin gwamnati sun sake kwace iko da shi a bara.

Emergency Lawyers ta dora alhakin harin gaba daya kan RSF, tana mai zarginsu da karya dokokin jin kai na kasa da kasa. Kungiyar ta kumace hare haren kan fararen hula naci gaba da karuwa, inda Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa kusan mutane 700 ne s**a mutu sak**akon hare haren drone cikin watanni ukun farkon shekarar nan.

A makon daya gabata ma, wani drone yakai hari kan wani asibiti a yankin Jebel Awliya dake kudancin Khartoum.

Tun bayan barkewar yakin Sudan a watan Afrilun 2023 tsakanin gwamnatin soji da RSF, miliyoyin mutane sun rasa matsugunansu yayin da kasar ke fuskantar mummunan rikici da matsalar jin kai.

An Yi Garkuwa da Tankar Mai dake Kan Hanyar Zuwa Somalia  Yemen.Mahukunta a ƙasar Yemen sun bayyana cewa an yi garkuwa d...
02/05/2026

An Yi Garkuwa da Tankar Mai dake Kan Hanyar Zuwa Somalia Yemen.

Mahukunta a ƙasar Yemen sun bayyana cewa an yi garkuwa da wata babbar tankar dakon mai da ke kan hanyarta ta zuwa ƙasar Somalia, lamarin da ya sake tayar da hankula kan matsalar tsaro a yankin tekun Aden da gabashin Afirka.

Rahotanni sun nuna cewa tankar mai din na dauke da kaya masu muhimmanci lokacin da wasu da ake zargin ‘yan fashin tekune s**a tare shi a cikin ruwa. Har yanzu ba a bayyana adadin ma’aikatan jirgin ko kuma ƙasashen da s**a fito ba.

Jami’an tsaro sunce ana ci gaba da bincike domin gano inda aka kai jirgin tare da tabbatar da lafiyar ma’aikatan dake cikinsa. Haka kuma, hukumomi sun yi gargadin cewa hare haren ‘yan fashin teku da garkuwa da jiragen ruwa na ƙara barazana ga harkokin kasuwanci da sufuri a yankin.

Tekun da ke tsakanin Yemen da Somalia ya dade yana fama da matsalar tsaro, musamman saboda ayyukan ‘yan bindiga da matsalolin rikice-rikicen siyasa da s**a addabi yankin tsawan shekaru.

Obi da Kwankwaso za su fice daga ADC ranar Litinin - Buba GaladimaJigo a jam’iyyar ADC, Buba Galadima, ya bayyana cewa t...
02/05/2026

Obi da Kwankwaso za su fice daga ADC ranar Litinin - Buba Galadima

Jigo a jam’iyyar ADC, Buba Galadima, ya bayyana cewa tsohon gwamnan Anambra, Peter Obi, da tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, za su sanar da ficewarsu daga jam’iyyar ADC tare da komawa wata sabuwar jam’iyya a ranar Litinin.

Galadima ya bayyana hakan ne a wani taron masu ruwa da tsaki na ƙungiyar Obi-Kwankwaso da aka gudanar a Abuja, inda ya ce ana shirin kafa sabuwar haɗaka gabanin zaɓen shekarar 2027.

Jaridar Punch ta rawaito cewa shugabannin biyu na kammala shirin komawa sabuwar jam’iyya mai suna NDC, wadda ake danganta ta da tsohon gwamnan Bayelsa, Seriake Dickson.

~ DCL Hausa

Gwamnan Jihar Sinaloa Ta Kasar Mexico Ya Yi Murabus Bayan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi Daga Amurka.Gwamnan jihar Sinal...
02/05/2026

Gwamnan Jihar Sinaloa Ta Kasar Mexico Ya Yi Murabus Bayan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi Daga Amurka.

Gwamnan jihar Sinaloa da ke kasar Mexico ya sanar da murabus dinsa bayan da hukumomin Amurka s**a danganta shi da zarge zargen hannu a harkar safarar miyagun kwayoyi.

Rahotanni sun bayyana cewa jami’an bincike na Amurka sun fara gudanar da bincike mai zurfi kan alakar wasu manyan jami’an siyasar Mexico da ƙungiyoyin masu safarar miyagun kwayoyi, musamman kungiyoyin da ke aiki a jihar Sinaloa wadda aka dade ana alakanta ta da manyan kartel ɗin miyagun ƙwayoyi.

Murabus din gwamnan na zuwa ne a daidai lokacin da matsin lamba daga gwamnatin Amurka ke karuwa kan Mexico domin daukar mataki mai tsauri kan safarar kwayoyi zuwa Amurka, musamman sinadarin fentanyl daya haddasa mutuwar dubban mutane.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, tsohon gwamnan ya musanta aikata laifin da ake zarginsa da shi, yana mai cewa yayi murabus ne domin baiwa hukumomi damar gudanar da bincike ba tare da katsalandan ba.

Sai dai masu sharhi kan harkokin siyasa na ganin wannan lamari zai iya ƙara dagula dangantakar siyasa tsakanin Mexico da Amurka, musamman wajen yaƙi da ƙungiyoyin masu safarar miyagun ƙwayoyi.

Jihar Sinaloa na ɗaya daga cikin yankunan da s**a fi fuskantar rikice rikicen da ke da alaƙa da kartel ɗin miyagun ƙwayoyi a Mexico, inda aka shafe shekaru ana fama da tashe tashen hankula da kashe kashe masu alaka da safarar kwayoyi.

Address

Sharadar Mallam Hauren Wanki Street, Behind Zone 1
Kano
700001

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Nagartacciya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share