Jaridar Nagartacciya

Jaridar Nagartacciya Wallafa sahihan labarai shine muradin mu, kuna da damar turo mana abubuwan da suke faruwa a inda kuke a lambar ta Whatsapp 08084944703

Shugaban Kasar Najeriya Bola Tinubu ya taya Al'ummar Musulmi Murnar Mauludi, ya yi Kira ga Jama'a da suyi Koyi da Kyawaw...
25/08/2026

Shugaban Kasar Najeriya Bola Tinubu ya taya Al'ummar Musulmi Murnar Mauludi, ya yi Kira ga Jama'a da suyi Koyi da Kyawawan Ɗabi’un Annabi Muhammad (SAW)

Shugaban Ƙasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya taya al’ummar Musulmi murnar bikin Mauludin Annabi Muhammad (SAW), tare da kira gare su da su yi koyi da kyawawan koyarwa da ɗabi’un Manzon Allah.

A cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Talata, Tinubu ya ce bikin Mauludi ya k**ata ya kasance lokaci na yin tunani, addu’a da ɗaukar darussa daga rayuwar Annabi Muhammad (SAW).

Shugaban Ƙasar ya bayyana cewa rayuwar Annabi Muhammad (SAW) na ƙunshe da darussa masu muhimmanci na ibada, haƙuri, juriya, tawali’u da sadaukar da kai.

Ya kuma yi kira ga shugabannin addini da su ƙarfafa mabiyansu wajen amfani da waɗannan kyawawan halaye wajen yi wa ƙasa hidima.

Tinubu ya buƙaci masu gudanar da bukukuwan Mauludi da su tallafa wa mabukata da marasa galihu, tare da yin addu’o’in kawo ƙarshen matsalar tsaro da sauran ƙalubalen da ke addabar wasu sassan Najeriya.

Shugaban Ƙasar ya yi fatan bikin Mauludin bana zai ƙara ƙarfafa haɗin kai, tausayi da zaman lafiya tsakanin al’ummar Najeriya.

IGP Disu Zai Ƙaddamar da Manhajar NPF Vigilant da MTN CUG Ranar 1 Ga Watan SatumbaBabban Sufeto-Janar na ’Yan Sandan Naj...
25/08/2026

IGP Disu Zai Ƙaddamar da Manhajar NPF Vigilant da MTN CUG Ranar 1 Ga Watan Satumba

Babban Sufeto-Janar na ’Yan Sandan Najeriya, IGP Olatunji Rilwan Disu, zai ƙaddamar da manhajar NPF Vigilant tare da tsarin MTN CUG a ranar 1 ga Satumba, 2026.

Ana sa ran ƙaddamar da shirye-shiryen zai ƙara inganta sadarwa, sa ido da haɗin gwiwa tsakanin jami’an ’yan sanda wajen gudanar da ayyukan tsaro a faɗin ƙasar.

Wane irin saƙo kuka taɓa ba wa jirgin sama a lokacin ƙuruciyarku, kuna tunanin idan ya tashi dawowa zai tawo muku dashi....
25/08/2026

Wane irin saƙo kuka taɓa ba wa jirgin sama a lokacin ƙuruciyarku, kuna tunanin idan ya tashi dawowa zai tawo muku dashi.✈️

Ku bayyana mana a Kwamen...

Muzaharar Maulidi Na ci-gaba da Gudana a Birnin KanoMuzaharar Maulidi na ci gaba da gudana a sassa daban-daban na birnin...
25/08/2026

Muzaharar Maulidi Na ci-gaba da Gudana a Birnin Kano

Muzaharar Maulidi na ci gaba da gudana a sassa daban-daban na birnin Kano, Muzaharar ta samu halartar mabiya Sheikh Ibrahim Zakzaky, ƙarƙashin jagorancin Sheikh Sunusi Abdulkadir Koki.

Ana gudanar da muzaharar domin nuna murna da zagayowar ranar haihuwar shugaba Halitta Annabi Muhammad (SAW).

Faransa da Saudiyya sun Cimma Yarjejeniya Kan Aikin Gine-ginen Guraren Shakatawa na Dala Biliyan 7 a Kusa da Birnin Pari...
25/08/2026

Faransa da Saudiyya sun Cimma Yarjejeniya Kan Aikin Gine-ginen Guraren Shakatawa na Dala Biliyan 7 a Kusa da Birnin Paris

Ƙasar Faransa da Saudiyya sun cimma yarjejeniyar zuba jarin kusan dala biliyan 7 domin gina manyan wuraren shakatawa kusa da birnin Paris na Faransa.

Aikin zai kasance a yankin Cergy-Pontoise, kimanin kilomita 30 daga arewa maso yammacin Paris.

Ana sa ran aikin zai samar da kusan guraben aikin yi 22,000, yayin da kamfanin Qiddiya na Saudiyya zai jagoranci zuba jari da gudanar da aikin.

An cimma yarjejeniyar ne yayin ziyarar Yarima Mai Jiran Gado na Saudiyya, Mohammed bin Salman, zuwa Paris, inda ya gana da Shugaban Faransa, Emmanuel Macron.

Ba a bayyana tak**aiman lokacin kammala aikin ba, yayin da ake sa ran ginin zai ɗauki shekaru.

Amurka ta Kaddamar da Yakin Tattalin Arziki ga Ƙasar IranGwamnatin Shugaban Amurka Donald Trump ta sanar da sabbin takun...
24/08/2026

Amurka ta Kaddamar da Yakin Tattalin Arziki ga Ƙasar Iran

Gwamnatin Shugaban Amurka Donald Trump ta sanar da sabbin takunkuman tattalin arziƙi masu tsauri kan Iran, a wani mataki da ta bayyana da nufin toshe hanyoyin samun kuɗaɗen shiga na Iran da kuma rage alaƙarta da tsarin tattalin arziƙin duniya.

Sabbin matakan sun shafi wasu mutane, kamfanoni da jiragen ruwa da ake zargi da taimaka wa harkokin tattalin arziƙin Iran, musamman a fannonin man fetur, harkokin kuɗi, fasaha da sufuri.

Gwamnatin Amurka ta kuma yi gargadin cewa ƙasashe da kamfanonin da za su ci gaba da yin hulɗa da Iran na iya fuskantar ƙarin takunkuman tattalin arziƙi.

A nata ɓangaren, Iran ta yi tir da matakan Amurka, tare da nuna cewa za ta ɗauki matakan da s**a dace domin kare muradunta da tattalin arziƙinta.

Sabbin takunkuman na ƙara tsananta rikicin da ke tsakanin Washington da Tehran, yayin da ƙasashen duniya ke ci gaba da sanya ido kan yadda lamarin zai shafi tattalin arziƙin duniya da kasuwancin man fetur.

Jami’in KAROTA Ya Samu Karaya Shida Bayan An Buge Shi A KanoWani jami’in Hukumar Kula da zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jih...
24/08/2026

Jami’in KAROTA Ya Samu Karaya Shida Bayan An Buge Shi A Kano

Wani jami’in Hukumar Kula da zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano (KAROTA), Nasiru Abdullahi, wanda aka fi sani da Baba Nasiru, ya samu karaya guda shida a sassa daban-daban na jikinsa bayan wata mota ta buge shi a kan titin Dambatta.

A cewar sanarwar da Mataimaki na Musamman ga Shugaban Hukumar KAROTA kan Harkokin Yada Labarai, Mu’azzam Mansur Kurawa, ya fitar ranar Lahadi 23 ga Agusta, 2026, direban motar ya tsere daga wurin bayan faruwar lamarin a daren Asabar.
Sanarwar ta ce jami’an ’yan sanda sun bi sawun direban, amma ba su samu nasarar k**a shi ba.

A halin yanzu, jami’in na samun kulawa a sashen gaggawa na Asibitin Murtala Muhammad da ke Kano.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa a lokacin da aka kawo jami’in asibiti, babu gado da zai kwanta. Sai dai Manajan Daraktan KAROTA, Injiniya Faisal Mahmud Kabir, ya shiga cikin lamarin tare da tabbatar da samar masa da gado domin ci gaba da samun kulawar lafiya.

Hukumar ta yi addu’ar Allah Ya ba jami’in cikakkiyar lafiya, Ya sauƙaƙa masa, sannan Ya dawo da shi bakin aiki cikin koshin lafiya.

Yan Sanda Sun Gargadi Matasa Kan Amfani da Su Wajen Rikicin SiyasaRundunar ’Yan Sandan Jihar Taraba ta kaddamar da wani ...
24/08/2026

Yan Sanda Sun Gargadi Matasa Kan Amfani da Su Wajen Rikicin Siyasa

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Taraba ta kaddamar da wani kamfen mai taken “My Future Is Greater Than Political and Digital Thuggery”, domin wayar da kan matasa kan illolin ta’addar siyasa, yaɗa labaran ƙarya da kuma amfani da kafafen sada zumunta ba bisa ka’ida ba.

An gudanar da taron a Jalingo, inda aka buƙaci matasa su guji tashin hankali, kada su bari ’yan siyasa su yi amfani da su wajen aikata laifuka, tare da amfani da fasahar zamani cikin hikima.

DCP Umar Shehu Didango, wanda ya wakilci Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Taraba, ya jaddada cewa makomar ƙasa tana hannun matasa, don haka ya k**ata su zaɓi ilimi, zaman lafiya da sana’o’in dogaro da kai.

Rundunar ta ce za a ci gaba da gudanar da irin waɗannan shirye-shirye a sauran sassan jihar domin ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin ’yan sanda da matasa.

Ba zamu Dawo da tsohon tsarin Tallafin Man Fetur ba – Gwamnatin Tarayya Gwamnatin Tarayya ta sake bayyana cewa ba ta gan...
24/08/2026

Ba zamu Dawo da tsohon tsarin Tallafin Man Fetur ba – Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta sake bayyana cewa ba ta ganin ya dace a dawo da tsarin tallafin man fetur da aka kawo ƙarshensa a farkon gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a shekarar 2023.

Shugaba Tinubu ya sha kare matakin cire tallafin, yana mai cewa tsarin ya yi wa tattalin arzikin ƙasa nauyi, kuma cire shi ya taimaka wajen kauce wa matsalar kuɗaɗen gwamnati.

Sai dai cire tallafin ya jawo ƙarin tsadar man fetur da kuma hauhawar kuɗin sufuri da kayan masarufi, lamarin da ya ƙara tsananta matsin rayuwa ga ’yan Najeriya.

Batun dawo da tallafin ya sake tashe ne bayan wasu ’yan siyasa sun fara yin kira da a sake duba tsarin domin rage wa talakawa nauyin tsadar rayuwa.

JARIDAR NAGARTACCIYA TA DAKATAR DA AIKIN SA-KAI NA AMINU LABARAN YAKASAIJaridar Nagartacciya ta sanar da dakatar da aiki...
24/08/2026

JARIDAR NAGARTACCIYA TA DAKATAR DA AIKIN SA-KAI NA AMINU LABARAN YAKASAI

Jaridar Nagartacciya ta sanar da dakatar da aikin sa-kai (Volunteer Service) na Aminu Labaran Yakasai, wanda ya kasance yana aiki a matsayin Editer a jaridar.

A cikin wata takardar sanarwa da Nagartacciya Media Management ta fitar a ranar 24 ga Agusta, 2026, jaridar ta bayyana cewa an yanke shawarar dakatar da aikin sa-kai na Aminu Labaran Yakasai ne bisa wasu sauye-sauye da aka samu a tsarin gudanar da ayyukan jaridar, tare da sake tsara yadda ake gudanar da aikin sa-kai.

Sanarwar ta bayyana cewa matakin ya fara aiki ne daga ranar Litinin, 24/08/2026.

Jaridar ta kuma bayyana godiyarta ga Aminu Labaran Yakasai bisa gudunmawar da ya bayar a lokacin da yake aiki tare da Jaridar Nagartacciya, tare da yaba kokarinsa, jajircewarsa da lokutan da ya sadaukar wajen gudanar da ayyukan jaridar.

Nagartacciya Media Management ta ce gudunmawar da ya bayar ta taimaka wajen bunkasa ayyukan jaridar da kuma isar da sahihan labarai ga al'umma.

A cewar sanarwar, duk da dakatarwar, jaridar ta yi fatan alheri da nasara ga Aminu Labaran Yakasai a rayuwarsa da kuma ayyukan da zai gudanar nan gaba.

Jaridar Nagartacciya ta jaddada cewa wannan sanarwa ce ta gudanarwa, kuma tana daga cikin sauye-sauyen da ake yi domin inganta tsarin aiki da ayyukan jaridar.

Nagartacciya Media Management
Jaridar Nagartacciya – Gaskiya Komai Dacinta

Address

Sharadar Mallam Hauren Wanki Street, Behind Zone 1
Kano
700001

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Nagartacciya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share