31/05/2026
Rahoton Ni daga jihar Katsina na cewa ,An sace tsohon babban jami’in sojan Najeriya kuma tsohon Daraktan Yada Labaran Tsaro, Manjo janar Rabe Abubakar, tare da matarsa a jihar Katsina da ke arewa maso yammacin Najeriya.
Rahotanni sun ce an yi garkuwa da su ne a ranar Asabar yayin da suke kan hanyar zuwa wani bikin aure, inda ‘yan bindiga s**a tare motarsu a yankin Matazu.
Mai magana da yawun sojojin Najeriya, Michael Onoja, ya tabbatar da faruwar lamarin ga BBC a ranar Lahadi, yana mai cewa ana ci gaba da kokarin ceto su tare da bin diddigin wadanda s**a sace su.
Wata majiya ta ce direban motar ya samu nasarar tserewa duk da raunin harbin bindiga da ya samu, yayin da ma’auratan aka tafi da su zuwa cikin dazukan da ke kusa da yankin.
Lamarin ya sake bayyana matsalar tsaro da ke addabar sassan arewa maso yammacin Najeriya, inda ake yawan samun garkuwa da mutane, satar shanu da hare-hare kan kauyuka daga ‘yan bindiga.
Jihar Katsina na daga cikin yankunan da s**a fi fuskantar wannan matsala a shekarun baya-bayan nan, lamarin da ke ci gaba da janyo damuwa a fadin kasar.
Wannan hari ya biyo bayan wani hari da aka kai a kauyen Kiliya da ke karamar hukumar Dutsinma, inda aka kashe aƙalla mutane 16 a ranar Juma’a, yayin bukukuwan Sallar Layya.
Source BBC Hausa
Fatika TV Hausa