Fatika TV Hausa

Fatika TV Hausa EDUCATIVE,ENLIGHTEN AND ENTERTAINMENT PROGRAMMES
(2)

FATIKA TV Hausa Shafi ne da aka samar dashi a ranar 01 ga watan Janairu 2026 don wallafa Labarai da Rahotanni, shirye shirye masu Ilimantarwa da Nishadantarwa a cikin harshen Hausa, domin talla ku tuntube mu kai tsaye ta Whatsapp no:+234912 943 7857 .

Rahoton Ni daga jihar Katsina na cewa ,An sace tsohon babban jami’in sojan Najeriya kuma tsohon Daraktan Yada Labaran Ts...
31/05/2026

Rahoton Ni daga jihar Katsina na cewa ,An sace tsohon babban jami’in sojan Najeriya kuma tsohon Daraktan Yada Labaran Tsaro, Manjo janar Rabe Abubakar, tare da matarsa a jihar Katsina da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Rahotanni sun ce an yi garkuwa da su ne a ranar Asabar yayin da suke kan hanyar zuwa wani bikin aure, inda ‘yan bindiga s**a tare motarsu a yankin Matazu.

Mai magana da yawun sojojin Najeriya, Michael Onoja, ya tabbatar da faruwar lamarin ga BBC a ranar Lahadi, yana mai cewa ana ci gaba da kokarin ceto su tare da bin diddigin wadanda s**a sace su.

Wata majiya ta ce direban motar ya samu nasarar tserewa duk da raunin harbin bindiga da ya samu, yayin da ma’auratan aka tafi da su zuwa cikin dazukan da ke kusa da yankin.

Lamarin ya sake bayyana matsalar tsaro da ke addabar sassan arewa maso yammacin Najeriya, inda ake yawan samun garkuwa da mutane, satar shanu da hare-hare kan kauyuka daga ‘yan bindiga.

Jihar Katsina na daga cikin yankunan da s**a fi fuskantar wannan matsala a shekarun baya-bayan nan, lamarin da ke ci gaba da janyo damuwa a fadin kasar.

Wannan hari ya biyo bayan wani hari da aka kai a kauyen Kiliya da ke karamar hukumar Dutsinma, inda aka kashe aƙalla mutane 16 a ranar Juma’a, yayin bukukuwan Sallar Layya.

Source BBC Hausa
Fatika TV Hausa

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta cika kusan kashi 90 cikin 100 na alƙawuran da ta yi...
31/05/2026

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta cika kusan kashi 90 cikin 100 na alƙawuran da ta yi wa al’ummar jihar cikin shekaru uku a kan mulki.

Ya yi wannan bayani ne yayin da ya karbi bakuncin Sarkin Rano, Ambasada Muhammad Isa Umaru, wanda ya kai masa ziyarar Sallah a Fadar Gwamnatin Kano a ranar Asabar.

A cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, ya ce gwamnatin Yusuf ta mayar da hankali kan aiwatar da ayyukan raya kasa da manufofi da s**a shafi rayuwar al’umma kai tsaye a fannoni daban-daban.

Ya bayyana cewa an samu ci gaba a fannonin ilimi, lafiya, ababen more rayuwa, noma, samar da ruwa, tallafawa matasa da bunkasa tattalin arziki, tare da cewa duk wadannan na nufin inganta rayuwar jama’a da kuma ciyar da Kano gaba mai dorewa.

A nasa bangaren, Sarkin Rano ya yaba wa gwamnan bisa abin da ya kira manyan nasarori cikin shekaru uku, inda ya ambaci kammala hanyoyi mai tsawon kilomita biyar a Rano, Kibiya da Bunkure, da kuma ci gaban aikin ruwa na Kaluwaiwai.

30/05/2026

Saurari Shirin Ƙasar Mu a Mako na yau Asabar 30ga May 2026, ku garzaya manhajar YouTube yanzu haka, shirin yana nan a tashar mu mai suna Fatika TV Hausa.

Duba comment section 👇

Muna me bada hakuri na rashin kawo maku cikaken shirin a shafin mu na,Facebook akan lokaci hakan yasamo asali ne sakamakon wata matsala da muka fuskanta, amma yanzu komai ya daidaita

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya ce matakin da gwamnatinsa ta ɗauka na cire tallafin man fetur ya ceci Najeriya daga fa...
30/05/2026

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya ce matakin da gwamnatinsa ta ɗauka na cire tallafin man fetur ya ceci Najeriya daga fadawa cikin matsananciyar matsalar tattalin arziƙi, tare da shimfiɗa tubalin farfaɗowar tattalin arzikin ƙasar.

Shugaban ya bayyana hakan ne a ranar Juma'a yayin da ya karɓi bakuncin wasu gwamnoni da s**a kai masa ziyarar taya murnar bikin babbar Sallah da kuma cika shekara uku da hawansa mulki.

Ya ce duk da cewa cire tallafin ya jawo wa 'yan Najeriya ƙalubale da raɗaɗi, matakin ya zama dole domin ceto ƙasar daga durƙushewar kuɗaɗenta da kuma dawo da daidaito a tattalin arziki.

Tinubu ya ce "tsawon shekaru Najeriya na kashe kuɗaɗe masu yawa wajen biyan tallafin man fetur wanda a cewarsa ya fi amfanar kaɗan daga cikin jama'a, yayin da muhimman fannoni kamar noma da ababen more rayuwa s**a rasa jarin da suke buƙata. "

Ya ƙara da cewa "tattalin arzikin ƙasar na nuna alamun farfaɗowa, inda noma da ayyukan gine-gine ke ci gaba da bunƙasa."

Shugaban ya kuma yaba wa gwamnonin jihohi bisa haɗin kai da goyon bayan da s**a ba gwamnatinsa wajen aiwatar da sauye-sauyen tattalin arziki.

Ya ce "a yanzu jihohi ba sa fama da matsalar neman tallafi daga gwamnatin tarayya domin biyan albashi kamar yadda aka saba a baya."

A nasa ɓangaren, Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya yaba wa jajircewar Tinubu wajen tinkarar matsalolin da ke tattare da tallafin mai, yana mai cewa shugaba ya nuna ƙarfin hali wajen ɗaukar matakan gyaran tattalin arzikin ƙasar.

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin na ƙasa (NGF) kuma gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana cewa gwamnoni na ...
30/05/2026

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin na ƙasa (NGF) kuma gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana cewa gwamnoni na nazarin yiwuwar ɗaga mafi ƙarancin albashin ƙasa zuwa Naira 100,000, kamar yadda jaridar Punch ta rawaito.

AbdulRazaq ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya ce hauhawar farashi, tsadar rayuwa da matsin tattalin arziƙi da ma'aikata ke fuskanta ne s**a sa ake duba batun.

Ya ce gwamnatocin jihohi na tattaunawa da gwamnatin tarayya da kuma ƙungiyoyin ƙwadago domin cimma matsaya kan sabon tsarin albashi da zai inganta rayuwar ma'aikata tare da tabbatar da cewa jihohi za su iya ɗaukar nauyin biyan albashin.

A cewarsa, manufar ita ce ƙara ƙarfin sayen kayan masarufi na ma'aikata tare da bai wa gwamnatoci damar ci gaba da aiwatar da ayyukan raya ƙasa da hidimomin jama'a.

A halin yanzu, mafi ƙarancin albashi a Najeriya na tsaye ne a kan naira 70,000 a wata, yayin da wasu jihohi ke biyan fiye da hakan.

Fatan alheri a gareku masu bibiyar tashar Fatika TV Hausa , muna fata kun tashi lafiya.
30/05/2026

Fatan alheri a gareku masu bibiyar tashar Fatika TV Hausa , muna fata kun tashi lafiya.

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya bayyana cewa gwamnatinsa na warware ƙangin da ɓangaren lantarkin ƙasa  ke ciki ta hanyar ƙa...
29/05/2026

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya bayyana cewa gwamnatinsa na warware ƙangin da ɓangaren lantarkin ƙasa ke ciki ta hanyar ƙarfafa kayan samar da lantarki da kuma zuba jari a ɓangaren makamashi maras guraɓata muhalli.

A wani bayani da Tinubu ya fitar na cika shekara uku bayan hawa kan mulki, shugaban ya ce “babu wata ƙasa da za ta bunƙasa a cikin duhu.

“A duk lokacin da lantarki ta bunƙasa, harkokin kasuwanci za su haɓɓaka, masana’antu za su bunƙasa sannan za a samu ayyukan yi kuma iyali za su shiga walwala,” a cewar Tinubu.

Najeriya na fama da matsanancin ƙarancin wutar lantarki na tsawon shekaru, wanda hakan ya janyo durƙushewar masana’antu da rasa ayyukan yi.

Jumaatu Mubarak ga daukacin al'ummar musulmi na duniya, dafatan anyi juma'a lafiya.
29/05/2026

Jumaatu Mubarak ga daukacin al'ummar musulmi na duniya, dafatan anyi juma'a lafiya.

Tsohon gwamnan Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya sanar da zaɓar Kwamared Aminu Abdussalam G...
29/05/2026

Tsohon gwamnan Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya sanar da zaɓar Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo a matsayin wanda zai yi wa jam'iyyar NDC takarar gwamna a zaɓen 2027.

Kwankwaso ya faɗi haka ne a saƙon da ya wallafa a shafinsa na X inda ya ce Dakta Nasiru Yusuf Gawuna kuma zai nemi kujerar sanata don wakiltar al'ummar Kano ta Tsakiya.

Ya ce an ɗauki matakin bisa gaskiya da biyayya da kuma ƙwarewa - ɗabi'un da har yanzu ginshiƙai ne a ci gaba da haɗin kan jam'iyyarmu da kuma Kwankwasiyya.

Sanarwar ta zo ne bayan shafe kwanaki ana tattaunawar sirri a tsakanin mambobin Kwankwasiyya da kuma tuntuɓar manyan ƴan siyasa.

Kwamared Gwarzo ya sauka daga muƙaminsa na mataimaki gwamnan jihar Kano a watan Maris sakamakon rikicin siyasa tun bayan da gwamna Abba Kabir Yusuf ya fice daga NNPP ya koma jam'iyyar APC mai mulki.

Shugaba Bola Tinubu ya ce ya fahimci irin sadaukarwar da iyalai s**a yi a shekarun baya-bayan nan inda kuma ya bayyana f...
29/05/2026

Shugaba Bola Tinubu ya ce ya fahimci irin sadaukarwar da iyalai s**a yi a shekarun baya-bayan nan inda kuma ya bayyana fatansa na samun ci gaba a Najeriya.

Ya kuma ce har yanzu tsaro na kan gaba a manufofin gwamnatinsa yayin da ƙasa ke ci gaba da tunkarar ƙalubale gadan-gadan kuma ana samun ci gaba yana mai bai wa ƴan Najeriya tabbacin cewa ba zai yi ƙasa a gwiwa ba wajen ganin ƴan Najeriya suna harkokinsu ba tare da zullumi ba.

Shugaba Tinubu ya bayyana haka ne a jawabinsa na bikin shekara uku kan mulki inda ya ce gwamnatinsa ba ta kai ga magance matsalolin ƙasar ba amma sun dasa tubalin samun ci gaba.

Ya ce aikin da ke gabansu shi ne tabbatar da cewa al'ummar Najeriya sun amfana daga sauye-sauyen da gwamnatinsa ke yi.

Shugaban ya kuma ce gwamnatinsa za ta ci gaba da tabbatar da cewa farashin kayan masarufi da ya sauka tun 2023/2024 bai tashi ba.

Ya kuma ce yana aiki don rage kuɗin sufuri kasancewar masu ababen hawa na mayar da motocinsu zuwa masu amfani da iskar gas da motoci masu amfani da lantarki.

Address

Dorayi
Kano
700241

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fatika TV Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Fatika TV Hausa:

Share

Category