14/04/2026
NUKILIYA WAJIBI IRAN TA MALLAKA.
📍|| LABARIN GAGGAWA‼️
Sabon jagoran addini na Iran, Sayyid Mojtaba Khamenei, ya bayyana cewa ya soke hukuncin da mahaifinsa Ayatollah Ali Khamenei ya kafa dangane da batun makaman nukiliya. Ya ce samar da makaman nukiliya ga Iran lamari ne na rayuwa da mutuwa, ba abu ne da za a tattauna a kai ba.
Ya kuma jaddada cewa a lokacin da duniya take karkashin ikon masu ɗagawa (’yan danniya) maimakon bin doka, hanya daya tilo da za a kare kai daga wanda ya zo mamaye kasa da kwashe dukiyarta ita ce Iran ta mallaki makaman nukiliya.
Mojtaba Khamenei ya ce ya kamata makiyan su fahimci cewa Iran na da ikon kera makaman nukiliya cikin kwanaki kadan idan bukatar hakan ta taso. An kuma ruwaito cewa ya bayar da umarni ga rundunar tsaron kasa ta Iran IRGC da su gaggauta samar da wadannan makamai cikin kankanin lokaci.
Kamfanin dillancin labarai na gwamnati IRNA ya ruwaito cewa kasashe kamar Russia, China da North Korea sun yi alkawarin ba Iran tallafi da goyon baya cikin gaggawa domin cimma wannan buri na makaman nukiliya.
Tambaya: Yaya kake kallon yadda sabon jagoran, Ayatollah Mojtaba, ya soke shawarar mahaifinsa tare da daukar sabuwar matsaya? Ka bar ra’ayinka a sharhi.