Arewa Media Political

Arewa Media Political Fejine Dazai Ringa Kawo Muku Labaran Siyasa Na Arewa A Aharshen Hausa Akoda yaushe. 08062232393

Da ɗumi-ɗumi: Matasa sun yi bore kan zargin kuɗaɗen N84.2bn, sun ƙi amincewa da Garo a matsayin Mataimakin Gwamna.Bayan ...
04/04/2026

Da ɗumi-ɗumi: Matasa sun yi bore kan zargin kuɗaɗen N84.2bn, sun ƙi amincewa da Garo a matsayin Mataimakin Gwamna.

Bayan rahoton da jaridar Mikiya ta wallafa kwanakin baya, inda ta tattara tare da fitar da cikakken lissafin kuɗaɗen da Gwamnatin Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ke zargin su Hon. Murtala Sule Garo da sacewa—wanda adadinsu ya kai kimanin Naira biliyan 84.2bn lamarin ya fara ɗaukar sabon salo a tsakanin jama’a.

A wani sabon yanayi, wasu matasa dauke da rubuce-rubucen saƙonni a hoton banabana sun tarbi Gwamnan a filin sauka da tashin jiragen sama na Malam Aminu Kano, inda s**a fito karara suna nuna adawa da yiwuwar bai wa Murtala Garo mukamin Mataimakin Gwamna.

Matasan sun bayyana cewa ba za su amince da irin wannan mataki ba, musamman duba da cewa gwamnatin jihar ta riga ta shigar da ƙara a kotu kan zarge-zargen da s**a shafi kuɗaɗe masu yawa da s**a haura biliyan 84.2.bn.

Rahoton da Mikiya ta fitar ne ya zama tushen wannan zanga-zanga, inda matasan s**a fara amfani da lissafin da jaridar ta bayyana domin nuna rashin goyon bayansu ga Hon. Murtala Sule Garo.

Lamarin na ƙara ɗaukar zafi yayin da jama’a ke jiran yadda gwamnati da masu ruwa da tsaki za su mayar da martani kan wannan matsin lamba daga matasa…

🚨Amurka ta tabbatar da cewar dakarunta sun shigo Nijeriya. Kwamandan Rundunar Sojin Amurka mai Kula Da Afrika, Janar Dag...
04/02/2026

🚨Amurka ta tabbatar da cewar dakarunta sun shigo Nijeriya.

Kwamandan Rundunar Sojin Amurka mai Kula Da Afrika, Janar Dagvin Anderson ne ya tabbatar da hakan a ranar Talata.

Wannan shine karon farko da aka yarda cewa sojojin Amurka na aiki a Nijeriya tun bayan da Washington ta kai farmaki kan wasu wurare da ake zargin mayakan IS na zaune a ranar 25 ga Disamba.

Anderson yace shigowar sojojin ta biyo bauan tattaunawa tsakanin kasashen biyu kan bukatar karfafa yaki da ta'addanci a Yammacin Afirka.

🚨"Halin da ake ciki yanzu haka a siyasar Jihar Kano." - Aranposu
04/02/2026

🚨"Halin da ake ciki yanzu haka a siyasar Jihar Kano." - Aranposu

Gwamna Abba...Yau bayan dawowar sa Daga Abuja gwamnan Kano Alh Abba Kabir Yusuf yayi tattaki Har gidan mahaifin iyalin n...
21/01/2026

Gwamna Abba...

Yau bayan dawowar sa Daga Abuja gwamnan Kano Alh Abba Kabir Yusuf yayi tattaki Har gidan mahaifin iyalin nan da aka yiwa kisan gilla su 7.
Gwamna ya yi musu ta'aziyya sannan yayi Kira Da a gaggauta gurfanar Da wadanda ake zargi a kotu sannan yayi aljawarin Da zarar kotu ta gama nata Zai dauki matakin ya dace.
Haka kuma gwamna Abba ya baiwa mahaifin wadanda aka kashe kujerar hajji Da sauran alkawura na kwantar Da hankali.
Kuma gwamna yayi alkawarin mayar da gidan da aka yi kisan masallaci Da kuma alkawarin baiwa wannan bawan Allah gida.
Ina rokon Allah ya kara masa hakuri ya Kuma sakawa gwamna da alheri.

🚨Tsohon shugaban majalisar wakilai kuma Sanatan Sokoto ta Kudu, Sanata Aminu Waziri Tambuwal yace matsawar ana son a sam...
13/01/2026

🚨Tsohon shugaban majalisar wakilai kuma Sanatan Sokoto ta Kudu, Sanata Aminu Waziri Tambuwal yace matsawar ana son a samu sahihin zaɓe a 2027 to fa sai manyan ƙasashen duniya sun shigo tare da sanya idanu.

Yace talaka ba shi ke tabbatar da nasarar zaɓuka nagari ba a mafi yawan lokuta, don haka dole ne a ɗauki matakan daƙile magudi da amfani da ƙarfi wajen cin zaɓe a 2027.

Hotuna: Yanzu yanzu Jagoran Jam’iyyar NNPP na kasa, Sen. Rabiu Musa Kwankwaso, ya sauka jihar Kano. 📸 Facebook/Meenan Kw...
13/01/2026

Hotuna:

Yanzu yanzu Jagoran Jam’iyyar NNPP na kasa, Sen. Rabiu Musa Kwankwaso, ya sauka jihar Kano.

📸 Facebook/Meenan Kwankwasiyya

Mai Martaba Sarkin Daura, Alhaji Umar Faruq Umar Tare Da Iyalansa A Kasar Faransa
11/01/2026

Mai Martaba Sarkin Daura, Alhaji Umar Faruq Umar Tare Da Iyalansa A Kasar Faransa

Da ɗumi-ɗumi: Shugaba Tinubu ya matsa lamba Sai Kwankwaso ya shiga jam’iyyar APC baya murna da shigar Gwamna Abba shi ɗa...
11/01/2026

Da ɗumi-ɗumi: Shugaba Tinubu ya matsa lamba Sai Kwankwaso ya shiga jam’iyyar APC baya murna da shigar Gwamna Abba shi ɗaya.

Rahoton da Daily Nigerian ta wallafa ya nuna cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na matsa lamba sosai, yana jaddada cewa **dole sai Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya koma jam’iyyar All Progressives Congress (APC), domin daidaita taswirar siyasa a Kano da Arewa maso Yamma gaba ɗaya.

Wata majiya ta bayyana cewa Kwankwaso na ƙara samun tausayi da goyon baya a faɗin jihar, musamman idan har Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya sauya sheƙa zuwa APC.

Majiyar ta ce idan hakan ta tabbata, ɗan takarar Kwankwaso na iya cin gajiyar ƙuri’un tausayi daga jama’a a zaɓen gaba.

“Kwankwaso na samun tausayi sosai. Idan Abba ya shiga APC, akwai yiwuwar ɗan takarar Kwankwaso ya amfana da ƙuri’un tausayi,” in ji wata majiya.

Wasu 'yan cikin gida da s**a san shirin sauya sheƙar gwamnan sun shaida wa Daily Nigerian cewa martanin jama’a shi ne ya sa ake ƙara yunƙurin ƙarshe na shawo kan Kwankwaso ya koma jam’iyyarAPC.

“Fargabar yadda jama’a ke kallon lamarin ne ya sa ake wannan matsin lamba domin Kwankwaso ya bi sahu,” in ji wata majiya.
Haka kuma, rahoton ya ce gwamnan na shirin yi wa Shugaban Ƙasa bayani kan ganawarsa da tsohon ubangidansa na siyasa da s**a rabu, sannan a tsara sabuwar hanyar tafiyar jam’iyyar bayan sauya sheƙarsa.

Mai Girma Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje OFR, ya halarci bikin makon Hisbah wanda aka gudanar a filin wa...
21/10/2021

Mai Girma Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje OFR, ya halarci bikin makon Hisbah wanda aka gudanar a filin wasa na Sani Abacha dake Kofar Mata, karkashin Jagorancin Shugaban Hukumar, Ustaz Muhammad Ibn Sina.

A Yayin taron, Gwamna Ganduje ya kaddamar da dakarun sakai na Hisbah su dubu biyar da dari bakwai tare da chanjawa jamian na Hisbah Uniform da kuma karin girma ga dukkan jami'an da s**a shekara shida suna aiki.

Gwamnan ya yaba da yadda Yan Hisban suke gudanar da aikin su inda yace za'a duba yiyuwar kara musu albashi Nan Bada Jimawaba.

Shugaban ma'aikata fadar gwamnati jihar Kano gwani Dr. Ali Haruna Makoda ya bada tallafi ga mata dubu ɗayaMai-girma Mai ...
20/10/2021

Shugaban ma'aikata fadar gwamnati jihar Kano gwani Dr. Ali Haruna Makoda ya bada tallafi ga mata dubu ɗaya

Mai-girma Mai Dakin Gwamnan Jihar Kano Farfesa Hafsat Abdullahi Umar Ganduje, Ta Jagorantar bada Tallafin Jari Ga Mata Dubu Daya (1000) na Naira Dubu goma-goma (10,000) Wanda Maigirma Shugaban Ma'aikan Fadar Gwamnati Hon. Dr. Ali Haruna Makoda Ya Samar domin tallafawa Matan Karamar Hukumar Makoda da Jari don Dogaro da kansu, donyi Sana'oin da zasu Taimaki Rayuwar su data Iyalan su.

Address

Zoo Road
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Media Political posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share