GSN Hausa

GSN Hausa Dinga ziyartar shafin GSN Hausa domin samun ingantattun labarai daga sassan duniya baki ɗaya. Musamman na Nigeria, Niger, da kuma Ghana!

Ka danna mana LIKE da kuma FOLLOW, mungode.

Da Dumi Dumi: An K**a Matashin Da Ya Kashe Mahaifiyarsa A Kano..A jiya 4 ga Mayu, 2023 da misalin karfe 10 na dare, an k...
05/05/2023

Da Dumi Dumi: An K**a Matashin Da Ya Kashe Mahaifiyarsa A Kano..

A jiya 4 ga Mayu, 2023 da misalin karfe 10 na dare, an k**a Ibrahim Musa, mai shekaru 22 a wani maboyar masu laifi a karamar hukumar Dawakin Tofa, jihar Kano bayan ya daba wa mahaifiyarsa mai shekaru 50 wuka wadda ta mutu har lahira a Rimin Kebbe Quarters, Nassarawa LGA, Kano State.

Wanda ake zargin ya amsa laifin da ake zarginsa da aikatawa, sannan kuma ya amsa laifinsa na shan miyagun kwayoyi. Za a gurfanar da shi gaban kotu bayan kammala bincike. Kwamishinan ’Yan sandan Jihar Kano, CP Mohammed Usaini Gumel, FIPMA, psc ya yaba wa wadanda s**a taimaka da bayanan da s**a kai ga k**a shi, ya kuma yaba wa rundunar ‘yan sandan da s**a tabbatar da an k**a mai laifin.

Kakakin Rundunar'Yan Sanda Na Jihar Kano Abdullahi Haruna Kiyawa

27/01/2023

Yadda dan takarar Shugaban Kasa na jam'iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya kaddamar da yakin neman zabensa a Jihar Benue.


📸 Bola Ahmed Tinubu

27/01/2023

Akalla mak**ai masu linzami 55 Rasha ta harba a kazamin harin da ta kai wa Ukraine.

27/01/2023




Gwamnatin Kano Karkashin Jagorancin Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje tayi Wani zaman gaggawa da Malaman Jihar Kano da s**a futa daga bangarorin Qadiriyya da Tijjaniya da Izala kan karancin sabon Kudi da yadda abun ya shafi rayuwa da kasuwanci a Jihar.

Gwamnati da Malaman sun bukaci Babban Bankin 'kasa na CBN daya Kara wa'adin daina karbar Tsohon Ku'di saboda rashin wadatar Tsohon a Kano baki 'daya.

27/01/2023

"Ba zan sake sace akwatin zaɓe ba," a cewar Goje bayan ya shafe shekaru a gidan maza yana cin gabza da zama da kwarkwata.

29/12/2022

Fitaccen dan wasan kwallon kafa Pele ya rasu a Brazil yana da shekaru 82 a duniya.

28/12/2022

Shugaban jam’iyyar APC na Kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya ce abin kunya ne ga Shugaba Muhammadu Buhari ya mika ragamar shugabancin Najeriya ga jam’iyyar adawa a 2023.

28/12/2022

Wani babban likita a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jihar Legas ya ce gwajin budurci da ake yi wa mata a asibiti don tantance ko sun taba tarayya da maza nau’i ne na cin zarafi kuma ya saba doka.

04/12/2022

Shugaban Majalisar Koli kuma Babban Limamin Masallacin Haramin, Sheikh Abdul Rahman Sudais ya jagoranci taron yi wa nakasassu tanade-tanade na musamman a Masallacin Haramin, albarkacin zagayowar Ranar Nakasassu ta Duniya.

Hoto: Twitter/Reasah Alharmain

19/11/2022

Mawaƙi kuma Jarumi a Kannywood Adamu Hassan Nagudu ya ce, bai ga dalilin da ƴan Social Media za su riƙa haɗa kansu da ƴan Film ba.

Nagudu ya ce, tasirin da ƴan Film ke dashi ya ninninka na ƴan Social Media shi ya sa ma ƴan siyasa ke rububinsu.

Sai dai ko da Freedom Radio ta tambaye shi kan rashin ganin ƴan Film suna kaɗa ƙuri'a ya ce, wani lokacin rashin tsaro ne ke sanya hakan domin saboda shahararsu dole sai da masu basu kariya.

Ga ƙarin bayanin da ya yi a kai.

19/11/2022

Jarumar Kannywood Aisha Bloody da aka fi sani da Hajara Ƴar Matawalle a shirin Izzar So ta bayyana halin da ta shiga bayan rasuwar Darakta Nura Mustapha Waye.

Bloody ta ce, soyayya da maganar aure a tskaninsu ta yi ƙarfi kafin rasuwarsa.

Ku kalli cikakkiyar tattaunawar inda ta soma da bada tarihin rayuwarta tun farko.

Muna masu farin cikin sanar da masoya shafinnan namu cewa "GSN Hausa ta dawo aiki gadan gadan kuma zaku samu sabbin laba...
12/11/2022

Muna masu farin cikin sanar da masoya shafinnan namu cewa "GSN Hausa ta dawo aiki gadan gadan kuma zaku samu sabbin labaran mu a wannan website ɗin na ƙasa."

Siyasa Tarihin mutumin da Atiku ya zaba a matsayin mataimakin shugaban kasa a PDP June 16, 2022 📝 Comr Nura Siniya Ifeanyi Okowa Shine Wanda Atiku Abubakar Ya Zaba A Matsayin…

Filin Jirgin Tashi Da sauka Na Jomo Kenyatta Shine Mafi Girma a Gabashin afrika.Daga Salisu A FaroukFilin jirgin sama na...
21/07/2022

Filin Jirgin Tashi Da sauka Na Jomo Kenyatta Shine Mafi Girma a Gabashin afrika.

Daga Salisu A Farouk

Filin jirgin sama na Kenya's Jomo Kenyatta International Airport shine filin jirgin sama mafi aiki da girma da jigila a gabashin Afirka.

Ya na ɗaukar fasinjoji 126 a kullum yayin da ya zo na huɗu a filayen jiragen sama Mafiya ayyuka a Afirika.

Madogara : Iconic Africa.

Gwamnatin Zamfara Ta Hana Sarakuna Nadin Sarauta Ba Tare Da Amincewarta BaSaga sani abubakar dutse.Gwamnan jihar Zamafar...
21/07/2022

Gwamnatin Zamfara Ta Hana Sarakuna Nadin Sarauta Ba Tare Da Amincewarta Ba

Saga sani abubakar dutse.

Gwamnan jihar Zamafara da ke arewa maso yammacin Najeriya Bello Matawalle, ya hana Sarakunan jihar nadin sarauta har sai sun samu amincewar gwamnatin jihar.

A wata sanarwa da mai taimaka wa gwamnan kan kafofin yada labari da sadarwa Zailani Bappa ya fitar, gwamnan ya ce ''Daga yanzu an umarci duk Sarakuna, da Hakimai, da Dagatai da ke jihar da su nemi amincewar gwamnatin jihar kafin su nada kowa, a kowanne mukami na Sarautar gargajiya''.

Sanarwar ta ci gaba da cewa ''umarnin ya zama wajibi ne domin kauce wa gurbata tsarin sarautar gargajiya, daga yanzu babu Sarki, ko Hakimi ,ko Dagacin da zai nada kowanne mukamin Sarauta, ba tare da samun amincewa da sahalewar gwamnatin jiha ba''.

''Bin wannan doka ya zama wajibi, domin kuwa gwamnati ta tanadi kwakkwaran mataki ga duk wanda ya saba wa dokar'', in ji sanarwar.

WASANNI : Kungiyar Kwallon Kafa ta PSG ta bayyana a ƙasar japan.Kungiyar kwallon ƙafa ta PSG ta sauka a ƙasar japan domi...
21/07/2022

WASANNI : Kungiyar Kwallon Kafa ta PSG ta bayyana a ƙasar japan.

Kungiyar kwallon ƙafa ta PSG ta sauka a ƙasar japan domin fara fafata wasan sada zumunta.

Kungiyar tayi taron manema labarai,sannan ta zanta ta tsohon ɗan kwallon Japan mai shekaru 55, Kazuyoshi Miura.

Mai rahoto :- Usman Idris Zannuraini

Da Dumi-DumiA hukumance, Tinubu ya sanar da Kashim Shettima, tsohon gwamnan Borno a matsayin mataimakinsa a takarar shug...
10/07/2022

Da Dumi-Dumi

A hukumance, Tinubu ya sanar da Kashim Shettima, tsohon gwamnan Borno a matsayin mataimakinsa a takarar shugabancin Najeriya a APC. Wakilin DW, Ubale Musa, ya ce Tinubun ya fadi haka ne bayan ganawar da ya yi da Shugaba Buhari a garin Daura a dazu-dazun nan.

Daga sani abubakar dutse.

Address

Tudun Wada, Nassarawa
Kano
700282

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GSN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share