GSN Hausa

GSN Hausa Ziyarci GSN Hausa don labarai ingantattu daga Najeriya, Nijar, Kamaru da Ghana, tare da sauran duniya baki daya. Kada ka manta da LIKE da FOLLOW. Mungode!

Me ya ja hankalina game da FasCoin Network?Ba wai dan mining ne da ake samun kuɗi masu yawa ba… A’a!Ba kuma saboda an ƙe...
11/02/2026

Me ya ja hankalina game da FasCoin Network?

Ba wai dan mining ne da ake samun kuɗi masu yawa ba… A’a!
Ba kuma saboda an ƙera app ɗin da kyau ba… A’a!

Abin da ya fi ɗaukar hankalina shi ne:

FasCoin ba kawai app na kuɗi ba ne — app ne da aka gina domin al’umma su taimaki juna da yaƙi da zalunci a duniya.

A cikin FasCoin Network, mutum zai iya:
✅ Kai rahoton zalunci a garinsa ko ƙasarsa
✅ Bayar da labarin cin hanci, damfara, fyade, wariyar launin fata, ko cin zarafi
✅ Rahoton zai kasance a bayyane ga jama’a amma ba wanda zai san wanda ya shigar da shi
✅ Ana iya rubuta rahoto da kowane yare — muddin rahoton na gaskiya ne.

Misali: idan an damfare ka, za ka iya shigar da rahoto domin jama’a su yi hattara, sannan kuma FasCoin Network zasu taimaka ma wajen neman maka haƙƙinka.

👉 Duk rahoton da ka shigar, za a baka 50 FasCoin.

Ba Iya haka kaɗai ba — idan kana son samun kudi masu yawa:

⛏️ Claiming 5 FasCoin duk awa 6

📺 Tasks na kallon ads:
• Duk minti 20 = 5 FasCoin
• Duk awa 1 = 8 FasCoin

Wannan app an gina shi ne domin inganta al’umma da dawo da gaskiya a duniya.

👉 Idan kana son buɗe account: duba link ɗin da ke comment section ko ku mana magana ta private
👉 Kar ka manta amfani da referral code ɗinmu:

gsnhausa

Tabbas — Gaskiya tana da daraja!

04/02/2026

Wani Dan Gwagwarmayar Siyasa Kenan Da Yace Ya Kashewa Gomna Abba Kudi Ba Adadi Amma Ya Juya Musu Baya Ya Koma APC.

Labari mai ɗaukar hankali!Farfesa Isa Ali Pantami, CON, ya sabunta rajistar kasancewarsa memba na jam’iyyar APC a yanzu,...
04/02/2026

Labari mai ɗaukar hankali!

Farfesa Isa Ali Pantami, CON, ya sabunta rajistar kasancewarsa memba na jam’iyyar APC a yanzu, inda ya sake jaddada biyayyarsa da ci gaba da jajircewarsa ga hangen nesan jam’iyyar, tare da yin alƙawarin cikakken goyon baya ga gwamnatin APC da ƙoƙarinta na bunƙasa ƙasa, haɗin kai, da shugabanci na ci gaba a Nijeriya.

RAYUWA KENAN! Innalillahi wa Inna ilaihi raaji'un!Allah Ya yi wa shahararren malamin addinin Muslunci, Sheikh Usman Kusf...
02/02/2026

RAYUWA KENAN! Innalillahi wa Inna ilaihi raaji'un!

Allah Ya yi wa shahararren malamin addinin Muslunci, Sheikh Usman Kusfa Zariya, wanda aka fi sani da Rigi-Rigi, rasuwa a daren ranar Lahadi 1 ga Fuburairun 2026, k**ar yadda majiyoyi na kusa da ahalin s**a tabbatar.

Sheikh Usman Kusfa, wanda ya shahara a kafafen sada zumunta saboda salon wa’azinsa, ana sa ran za a gudanar da jana’izarsa a yau Litinin, a gidansa da ke Zariya.

Har Yanzu Ana Ta Shirin Tarbar Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf zuwa Jam'iyyar APC inda Aka Haka Ganduje Ya Sauka A J...
26/01/2026

Har Yanzu Ana Ta Shirin Tarbar Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf zuwa Jam'iyyar APC inda Aka Haka Ganduje Ya Sauka A Jirgi Domin Halartar Wannan Taro.

Kurunkus! Gwamna Abba Kabir Yusuf zai shiga APC gobe Litinin, 26/01/2026 — in ji Sunusi Bature Dawakin Tofa.An tabbatar ...
25/01/2026

Kurunkus! Gwamna Abba Kabir Yusuf zai shiga APC gobe Litinin, 26/01/2026 — in ji Sunusi Bature Dawakin Tofa.

An tabbatar da cewa Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, zai sauya sheka zuwa jam’iyyar APC gobe Litinin, 26 ga Janairu, 2026.

Wannan bayani ya fito ne daga Babban Daraktan Yada Labaran Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, wanda ya bayyana cewa dukkan shirye-shiryen sauyin jam’iyyar sun kammala.

Rahotanni sun nuna cewa wannan mataki na Gwamna Abba na iya sauya yanayin siyasar Kano, tare da haifar da sabbin sauye-sauye a tafiyar jam’iyyun siyasa a jihar da ma kasa baki ɗaya.

Ana sa ran manyan jiga-jigan APC da sauran masu ruwa da tsaki za su halarci taron karɓar Gwamnan a hukumance.

25/01/2026

Me Kuka Fahimta A Wannan Bidiyon?

An tsinci jariri sabuwar haihuwa a Tudun Murtala, Kano — lamarin ya tayar da hankalin jama’a.An tsinci jariri sabuwar ha...
24/01/2026

An tsinci jariri sabuwar haihuwa a Tudun Murtala, Kano — lamarin ya tayar da hankalin jama’a.

An tsinci jariri sabuwar haihuwa a safiyar yau a yankin Tudun Murtala, kusa da makabarta da ke cikin birnin Kano.

Wata mazauniyar yankin, Ummulkhair Ayuba Musa, ta shaida wa Freedom Radio Nigeria cewa sun wayi gari da ganin wani abu a nannade cikin leda a gefen makabartar. Bayan an duba abin, sai aka gano jariri ne mace, sabuwar haihuwa.

Rahotanni sun nuna cewa har yanzu ba a yi mata cikakken kulawar haihuwa ba, lamarin da ya nuna jaririyar ta zo duniya ne a cikin yanayi mai tayar da hankali.

A halin yanzu, ana sa ran za a yi mata sallah a binne ta k**ar yadda addini ya tanada.

Malam haruna ya bada gidansa ayi masallaci ko makaranta sadakatujjariya ga iyalansa da aka yiwa ki*_*_san gilla….!!!Baya...
23/01/2026

Malam haruna ya bada gidansa ayi masallaci ko makaranta sadakatujjariya ga iyalansa da aka yiwa ki*_*_san gilla….!!!

Bayan KYAUTAR gida daya samu daga hannun gomna, ya yanke shawarar bayar da gidansa domin a gina masallaci koh makaranta a matsayin sadaka mai gudana ga iyalansa..!!

Allah ya haskaka qabarinsu da rahama 🤲🏿🤲🏿🤲🏿

Muna addu'a Allah ya hakur kurtar da malam haruna, Allah ya bashi dangana, iyalanshi Allah ya basu Aljanna Madaukakiya, Amen ya rabb.🤲🏿

Ta faru ta ƙare Gwamna Abba na jihar Kano ya fice daga jam'iyyyar NNPP Sauran bayani na nan tafe!Wace jam'iyya kuke tuna...
23/01/2026

Ta faru ta ƙare Gwamna Abba na jihar Kano ya fice daga jam'iyyyar NNPP

Sauran bayani na nan tafe!

Wace jam'iyya kuke tunanin zai koma?

ALHAMDULILLAHI: Yansanda Sun Cafke Mutane Uku Kan Kisan Uwa da ’Ya’yanta a Dorayi ChiranchiRundunar ’Yansanda ta Jihar K...
18/01/2026

ALHAMDULILLAHI: Yansanda Sun Cafke Mutane Uku Kan Kisan Uwa da ’Ya’yanta a Dorayi Chiranchi

Rundunar ’Yansanda ta Jihar Kano ta k**a mutane uku da ake zargi da hannu a kisan gillar wata uwa da ’ya’yanta shida da aka yi a unguwar Dorayi Chiranchi cikin birnin Kano.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar a ranar Lahadi.

Kamen ya biyo bayan wani aiki na musamman bisa bayanan sirri, wanda aka gudanar bisa umarnin Sufeto Janar na ’Yansanda, Kayode Egbetokun, tare da kulawar Kwamishinan ’Yansanda na Jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori.

🕒 Lokaci da Yadda Aka Yi Kamen

A cewar rundunar, an k**a waɗanda ake zargin ne a wani samame da aka gudanar daga ƙarfe 10:00 na dare ranar 17 ga Janairu zuwa 4:00 na asubahin 18 ga Janairu, 2026.

Mutanen da aka k**a sun haɗa da:

- Umar Auwalu, mai shekaru 23, daga unguwar Sabuwar Gandu

- Isyaku Yakubu (Chebe), mai shekaru 40, daga unguwar Sagagi

- Yakubu Abdulaziz (Wawo), mai shekaru 21, daga unguwar Sabon Gida Sharada

🔍 Abin da Bincike Ya Nuna

’Yansanda sun ce Umar Auwalu, wanda ake zargi da jagorantar laifin kuma ɗan ’yar uwar marigayiyar, ya amsa aikata laifin. Haka kuma, ya bayyana cewa sun aikata wasu laifuka masu tsanani a wasu sassan Kano a baya-bayan nan.
Daga cikin abubuwan da aka kwato daga hannun waɗanda ake zargin akwai:

- tufafi masu tabon jini
- wayoyin salula biyu na marigayiyar
- kuɗi da ake zargin an kwace a wajen da abin ya faru
- da wasu kayayyaki masu haɗari
Do
Rundunar ta ce bincike na ci gaba domin gano duk wanda ke da hannu a lamarin.

🛡️ Tabbacin ’Yansanda

Rundunar ’Yansanda ta Jihar Kano ta yaba wa jami’an da s**a gudanar da aikin, tare da gode wa al’umma bisa addu’o’i, goyon baya da haɗin kai. Ta kuma tabbatar wa jama’a cewa za ta gurfanar da duk masu aikata laifi a gaban kotu, ba tare da nuna son rai ba.

Address

Tudun Wada, Nassarawa
Kano
700282

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GSN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share