Farar Tantabara

Farar Tantabara we provide justice.

01/12/2024

Ance idan aka cire tallafin man fetur talaka zaiji dadi, shin yanzu dadi mukeji ko wahala❓

Wai mutumin da tun 17 ga Oktoba ya je har Arewa House a Kaduna ya shafe fiye da awa biyu yana maganar tanadinsa ga Arewa...
23/01/2023

Wai mutumin da tun 17 ga Oktoba ya je har Arewa House a Kaduna ya shafe fiye da awa biyu yana maganar tanadinsa ga Arewa shi ne yau bayan wata uku ƴan kasuwar siyasa za su fito su ce bai tanadarwa Arewa komai ba. Ikon Allah! Kowa dai ya tashi shirya gidogarsa sai ya ce yana yi ne saboda mutanen Arewa kai ka ce badakalar kwangilar taki ta zamanin Shekarau da rigima kan Prado Jeeps da sayar da sunan Buhari na tsahon shekaru duk dama hidimar talakan Arewa ce.

A jawababinsa na Arewa House (wanda aka fassara kuma aka buga da Hausa) Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya yi muhimmin bayanai yadda zai warware matsalolin da s**a shafi Arewa k**a daga matsalar tsaro har zuwa ta almajiranci. Kuma bayani ne dalla-dalla. Bayan wancan taron na Arewa House Asiwaju ya ƙaddamar da kundin tsarin ayyukan da ya tanadarwa Nijeriya (Renewed Hope). Masana sun haƙƙaƙe cewa a wannan kakar zaben babu ɗan takara da kundinsa ya fi na Tinubu bayanin yadda za a warware matsalolin ƙasa dalla-dalla. Wannan kundi yana nan available ga duk mai son dubawa.

Maganar farfaganda ta cewa Tinubu ba zai iya riƙe kofi ba wannan yarfe ne na wanda s**a saba cin abinci da yarfen siyasa. Mutumin da ba zai iya riƙe kofin shayi ba ta ya zai iya riƙe abin magana (makirfo) na tsahon lokaci? Ko jiya a gaba na a nan Bauchi haka ya shafe tsahon lokaci yana jawabi riƙe da abin magana. Haka nan, a gaba na a kuma gaban mutane da dama jiya ya ci abincin dare da cokali (fork) da wuƙa ta hanyar amfani da duka hannayensa biyu, amma mai ƙarya da sharri tana can tana soki-burutsu!

Ba a hana mutum bin ra'ayinsa a siyasa ba ko kuma ma karɓar ƴan canji don sauya layi amma a sani idan mafaɗin magana wawa ne, majiyi ba lallai ne ya zama wawa ba.

✍🏼 Abdul'aziz

Barkanmu Da Safiya Abokai.
18/01/2023

Barkanmu Da Safiya Abokai.

A shekaru 61 da kasarmu Nigeria tasamu 'yancin kanta daga turawan mulkin mallaka na burtaniyya. Tabbas ansamu cigaba tar...
01/10/2021

A shekaru 61 da kasarmu Nigeria tasamu 'yancin kanta daga turawan mulkin mallaka na burtaniyya. Tabbas ansamu cigaba tare da samun sauye-sauye da dama daga cikin al'anuran gudanarwa na yau da kullum, Sannan munfuskanci nakasu tare da koma baya tabangaren cigaban da zamani yazomana dashi, babu shakka koma bayan da kasata ta samu acikin wannan shekarun sunyi tasiri matukar gaske inda tasirin ya mamaye nasarar da Nigeria ta samu acikin Wannan shekarun.

Tabbas idan mukayi nazari da wasu kasashen damuka sami 'yanci atare dasu kokuma muka sami 'yanci kafin su samu, sunsami cigaba tare da gina kasashensu ta yadda babu yadda za'ayi yanzu kace zaka hada kanka dasu, Dayawa daga cikin kasashen sun gina kasashensu daga cikin dan arzukin da Allah ya wadata Nigeria itakuma ta taimaka musu.

Amma mu munkasa sanin inda kasar tamu ta dosa baki daya, A tsarin da Nigeria take Kai yanzu bawaei tsarine na gina kasaba tsarine wanda idan ba'ayi da gaskeba nan da dan karamin lokacin komai zai iya kasancewa acikin wannan kasar tamu ta Nigeria wanda ba babu wanda zaiji dadin abinda zaikasance daga kasar har wa'yanda suke rayuwa acikin kasar.

Babu abunda jagororin wannan kasar suke kudurcewa a ransu k**ar, Kassara Arzukin kasa, sace kudin talakawa, Cin hanci da rashawa, tsadar kayan abinci, talauci, rashin aikinyi ga matasa, lalacewar ilimi, wuta, ruwa, matsalar tsaro kashe kashan rayukan da basujiba basu ganiba, sace mutane da neman kudin fansa, fadan boko haram,.......😭😭
Tabbas naso ace ina daya daga cikin masu farincikin da wannan rana sedai Zuciyar takasa gasgata cewar talaka me 'yan cine a kasata Nigeria.

Bazan gusheba daga yiwa kasata Addu'ar samun nasara, Ubangiji kadubeta da kallo na rahama kasanya wannan kuncin da radadain da mukeji yazamto tarihi acikin rayuwarmu, duk masu burin durkusar da kasata Allah kada kabasu iko akanta. Allah Kadaga Kasata Nageri. 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
💪🏼💪🏼💪🏼 Long Life My Mother Land 💪🏼💪🏼💪🏼

Jama'ar jihar Kano kuzo kuyi alkalanci akan masu wakiltarku a majalisun tarayya, akan kudurin da s**a gabatar daga 2019 ...
17/09/2021

Jama'ar jihar Kano kuzo kuyi alkalanci akan masu wakiltarku a majalisun tarayya, akan kudurin da s**a gabatar daga 2019 zuwa yanzu.

- MAJALISAR DATTIJAI

1. Sanatan Kano ta Arewa, Barau Jibril Maliya, ya gabatar da kuduri guda 13

2. Sanatan Kano ta tsakiya, Malam Ibrahim Shekarau, bai samu gabatar da kuduri ko daya ba

3. Sanatan Kano ta kudu, Kabiru Ibrahim Gaya, ya gabatar da kuduri guda 3

- YAN MAJALISAR WAKILAI NA KASA

1. Dan majalisar wakilai ta kasa mai wakiltar karamar hukumar Kumbotso, Manniru Babba Dan Agundi, ya gabatar da kuduri guda 7

2. Dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Wudil da Garko, Ali Muhammad Wudil, ya gabatar da kuduri guda 6

3. Dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomi Doguwa da Tudun Wada, Alhassan Ado Doguwa, ya gabatar da kuduri guda 3

4. Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Tarauni, Hafizu Muhammad Kawu, ya gabatar da kuduri guda 3

5. Dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Karaye da Rogo, Haruna Isa Dederi, ya gabatar da kuduri guda 3

6. Dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Rano, Kibiya da Bunkure, Kabiru Alasan Rurum, ya gabatar da kuduri guda 2

7. Dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Kunchi da Tsanyawa, Sani Bala, ya gabatar da kuduri guda 2

8. Dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Takai da Sumaila, Shamsuddeen Bello Dambazau, ya gabatar da kuduri guda 2

9. Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Fagge, Aminu Sulaiman Goro, ya gabatar da kuduri guda 2

10. Dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Gezawa da Gabasawa, Nasiru Abduwa, bai samu gabatar da kuduri ko guda daya ba

11. Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Gwale, Abdullahi Lawan Ken-Ken, bai samu gabatar da kuduri ko guda daya ba

12. Dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Gwarzo da Kabo, Musa Umar Garo, bai samu gabatar da kuduri ko guda daya ba

13. Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Birni, Sha'aban Ibrahim Sharada, bai samu damar gabatar da kuduri ko guda daya ba

14. Dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu, Abdullahi Mahmud Gaya, bai samu gabatar da kuduri ko guda daya ba

15. Dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Kiru da Bebeji, Ali Datti Yako, bai samu gabatar da kuduri ko guda daya ba

16. Dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Kura, Madobi da Garun Malam, Kabiru Idris, bai samu gabatar da kuduri ko guda daya ba

17. Dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Ungoggo da Minjibir, Sani Ma'aruf, bai samu damar gabatar da kuduri ko guda daya ba

18. Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Dala, Babangida Alhassan Yakudima, bai samu gabatar da kuduri ko guda daya ba

19. Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Bichi, Abubakar Kabir Bichi, bai samu gabatar da kuduri ko guda daya ba

20. Dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Bagwai da Shanono, Ahmad Yusuf Badau, bai samu damar gabatar da kuduri ko guda daya ba

21. Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Nasarawa, Nasiru Ali Ahmad, bai samu damar gabatar da kuduri ko guda daya ba

22. Dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Dambatta da Makoda, Badamasi Ayuba, bai samu damar gabatar da kuduri ko guda daya ba

23. Dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Tofa, Rimin Gado da Dawakin Tofa, Tijjani Abdulkadir Jobe, bai samu gabatar da kuduri ko guda daya ba

24. Dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Dawakin Kudu da Warawa, Mustapha Bala, bai samu gabatar da kuduri ko guda daya ba

Wannan rahoton Order Paper ne da ta fitar, daga watan June na shekarar 2019 zuwa watan May na shekarar 2021, a saboda haka jaridar Kano Online News ke bukatar ku bayyana ra'ayoyinku.

Kowa ya fadi sunansa, karamar hukumarsa, da sunan wakilinsa, da kuma makin dazai iya bashi, banza zagi don Allah.

Daga: Kano Online News
17/9/2021

GYARA KAYANKA................Kada kataba daukar wanda yace ka gyara yadda kake tafiyar da rayuwarka a matsayin makiyinka...
15/09/2021

GYARA KAYANKA................

Kada kataba daukar wanda yace ka gyara yadda kake tafiyar da rayuwarka a matsayin makiyinka koda ace ba shiri kukeyi da shiba...

Maganar da Me dakin Shugaba Muhammadu Buhari Tayi akwanakin nan damuke ciki nauyine daya rataya akanta, ta fada, kuma tayi se dai jama'a zasu iya fadar a bubuwa da yawa akanta sedai kada kumanta da Idan sanin dadin mulkine babu wanda yakaita sak**akon mijintane yake jagorantar Kasar.

Babu maganar bakin ciki ko hassada kokuma ace adawar siyyasa a shekarun baya tasha bitowa tafadi gaskiya Amma se makauniyar soyayya tasa mukakasa fahimtar inda tunaninta yakeso ya kaimu.

Ire-iren ta dasu me martaba sarkin Kano me murabus sunsha yin rubuce rubuce dan ganin anyi gyara acikin yadda ake tafiyar da gwamnatin tarayyar Nejeria karkashin jagorancin Shugaba Buhari.

Afito Afadi gaskiya.......🧏🏽‍♂️

Haryanzu lokaci be kureba, Malamai Sarakuna, 'Yan siyyasa Da Attajirai da duk wanda Allah Yabaiwa dama koda ta rubutuce akafar sadarwa ta Facebook mufito mufadawa Gwamnati gaskiya domin wallahi Muma akwai hakki akanmu kuma wajibine afito ayi magana domin a gyara.

Kasa ta ko ina babu dadi Yara da manya tare da matasa da kananan yara kowa kuka yake mutane kadanne suke sarrafa rayuwar mutane Millions a Nigeria 😭 tabbas gwamnati Uwar kowace duk abinda taso zata cimma nasara akai seda idan bata soba. Missali Samar da tsaro a Jihar zamfara ayau duk adawarka da gwamnati dole kayabamata

Amma me gwamnati take domin ganin ta cire yankasa daga cikin halin talaucin da bara zanar rayukansu da suke ciki a Nigeria.🧏🏽‍♂️❓

we provide justice.

Operation Girbi Abinda ka Shuka! Wannan operation din zai maida hankaline gurin zakulo irin gudunmawar da wasu su ka bay...
04/08/2021

Operation Girbi Abinda ka Shuka!

Wannan operation din zai maida hankaline gurin zakulo irin gudunmawar da wasu su ka bayar a zaben inconclusive na Kano da kuma irin yadda su ke girbe abubuwan da su ka shuka. Sai dai operation din zai dagawa wadanda su ka mutu kafa. Da fari dai mu fara da wannan:

1. Ministan da ya baiwa IG umarnin ayi rashin arzikin, ya bar kujrrar.

2. IG din da aka baiwa umarnin, ya bar kujerar.

3. DIG (dan giya) din da aka aiko shima ya bar kujerar.

4. Abba Kyari da su ka taimakawa DIG shima an dakatar da shi.

5. Singham da aka hana yin aikin sa sabo da shi mai gaskiya ne, ya yi ritaya cikin aminchi kuma yanzu ya na rike da kujerar mai baiwa gwamnan Gombe shawara akan harkokin tsaro.

A saurari sako na gaba.

Kabir Dakata

Mutuwar Laftanar Janar Attahiru Bakaramin Rashi bane Ga Nigeria Da Yankin Arewa Tare Da Rundunar Sojoji Bakidaya Tabbas ...
22/05/2021

Mutuwar Laftanar Janar Attahiru Bakaramin Rashi bane Ga Nigeria Da Yankin Arewa Tare Da Rundunar Sojoji Bakidaya Tabbas Munyi Rashi.😭

Babban hafsan sojin Najeriya Laftanar Janar Ibrahim Attahiru ya rasu sak**akon hadarin jirgin saman soji a Kaduna.

Mai magana da yawun rundunar sojin, Birgediya Janar Mohammed Yarima ne ya tabbatar da manema labarai faruwar lamarin.

Bayanai sun ce jirgin saman na soji ya fadi ne a kusa da filin tashi da saukar jiragen sama na Kaduna mutum takwas ne a cikin jirgin lokacin da hadarin ya faru.

Laftanar Janar Ibrahim Attahiru shi ne ya maye gurbin Janar Tukur yusuf Buratai babban hafsan sojan kasan Nigeria.

An haifi Janar Attahiru a 1966 a jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya.

Ya taba jagorantar yaki da ƙungiyar Boko Haram amma a shekarar 2017 ne Janar Tukur Buratai ya sauke shi daga muƙamin bayan wasu hare-hare da 'yan bindiga s**a kai inda aka kashe wasu mutane 50 a lokacin da suke sallah a masallaci.

Kafin ba shi wannan muƙamin, Laftanar Janar Attahiru shi ne shugaban runduna ta 82 a rundunar sojin Najeriya.

Ranar 26 ga watan Janairun 2021 ne Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya naɗa shi a matsayin Babban Hafsan Sojin ƙasar.

Janar Attahiru shi ne babban Hafsan Sojin Najeriya na 21.

Wannan ne haɗarin jirgin sojin saman Najeriya na uku cikin wannan shekarar ta 2021.

Muna addu'ar Ubangiji Ya Jaddada Rahama Agareshi Tare Da Sauran Abokanan Aikinsa Das**a Rasu Acikin Wannan Hadarin, Ubangiji Kacigaba Dabaiwa Kasata Nageri Kariya Daga Sharrin Miyagu Tare Da Masu Bukatar Ganin Kasar Ta Durkushe,

Allah Kabamu Shuwa Gabanni Nagari Masu Kishin Kasar Da Gaskiya.

✍🏽✍🏽 Farar Tantabara🕊️🕊️

22/05/2021

CIKAR IMANI SHINE ❣️❣️❣️

Ka Yadda Da Allah (SWT) Shike Kashewa, Shike Rayawa, Shike Azurtawa, Kuma Shike Talautawa, Idan Kasamu Allah, Idan Karasa Allah, Kuma Kasowa Dan Uwanka Abinda Kake Sowa Kanka.

Ya Allah Muna Rokonka Da Katsare Mana Imanin Mu A Duk Inda Muke.

Barkanmu Da Wannan Lokaci 'Yan Uwa Al'ummar Annabi Mohammad (S.A.W) 🤝🤝🤝

Duk Shugaban Da Bazai Gina Na Kasa Dashi Sunzo Sun Wuce Shi Ba, To Ba Shugaban Bane ~ KwankwasoTsohon Gwamnan Jihar Kano...
14/12/2020

Duk Shugaban Da Bazai Gina Na Kasa Dashi Sunzo Sun Wuce Shi Ba, To Ba Shugaban Bane ~ Kwankwaso

Tsohon Gwamnan Jihar Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Bayyana Cewa Babban Burinsa Shine Idan Kana Dan Aike (Masinja) Ya Dagaka Zuwa Babban Mataki Kololuwa Na CEO (Chief Executive Officer), Hakan Shine Zaisa Yaji Dadi Yayi Farin Ciki.

Kwankwaso, Ya Bayyana Hakan Ne Cikin Wata Tattaunawa Da Sashen Gidan Talabijin Na Kwankwasiyya Reporters Yayi Dashi, Wani Lokaci A Gidansa Dake Birnin Kano, Harma Ya Bayyana Yadda Tafiyar Siyasar Kwankwasiyya Take Kokarin Janyo Na Kasa Zuwa Matakin Sama.

"Burina Idan Muna Tare Dakai Naga Ka Wadata, Idan Naje Gidanka Naga Yafi Nawa, Don Bazai Yiwu Naje Gidanka Na Zauna A Tafarfara Ni Kuma Ina Gidan Siminti Ba, Burina Inje Ofishinka Naga Yafi Nawa, Duk Shugaban Da Bazai Gina Na Kasa Dashi Sunzo Sun Kaishi Ko Sun Wuce Shi Ba, To Ba Shugaban Bane.

"Mu Burinmu Shine Muyi Ta Inganta Rayuwar Al'umma, Wasu Suna Siyasa Suna Tunanin Idan Sun 'Daga Wani, Watarana Zai Zare Takobi Ya Saresu, Amma Ni Ba Haka Nake Ba, Tsarinmu Na Kwankwasiyya Ba Haka Yake Ba, Mu Zamu 'Daga Na Kusa Damu, Suma Su 'D**o Na Kasa Dasu, Haka Dai Kamar Kafar Bene."

Rahoto:
Kwankwasiyya Reporters TV 📺
Sun, Dec 13, 2020.

Address

Kano

Telephone

+2348137446665

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Farar Tantabara posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Farar Tantabara:

Share