Abba Go Again 2027.

Abba Go Again 2027. Agriculture 💯

Majalisar Dokoki ta nemi Gwamnatin Kano ta gyara babban masallacin jihar Majalisar dokokin jihar Kano ta nemi Gwamnatin ...
24/09/2025

Majalisar Dokoki ta nemi Gwamnatin Kano ta gyara babban masallacin jihar

Majalisar dokokin jihar Kano ta nemi Gwamnatin jihar ta gyara Babban Masallacin cikin Gari mai cike da tarihi.

Freedom Radio ta rawaito cewa a zaman majalisar jihar da aka gudanar yau, ɗan majalisar Birni, Aliyu Yusuf Daneji, ya sake kira ga gwamnati da ta gaggauta fara aikin gyaran masallaci da aka riga aka gabatar mata a baya, amma har yanzu ba a aiwatar ba.

Haka kuma, ɗan majalisar da ke wakiltar ƙaramar hukumar Rano, Ibrahim Muhammad Malami Rano, ya bukaci gwamnati ta gyara muhimman hanyoyin cikin garin Rano.

Yan majalisun biyu sun bayyana cewa gyaran masallacin da kuma hanyoyin na da matuƙar muhimmanci ga rayuwar al’umma, tare da roƙon gwamnati da ta ɗauki matakin gaggawa.

Shaye-shaye barazana ce ga goben Nijeriya, Buba Marwa ya gargaɗi matasa Shugaban Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun...
23/09/2025

Shaye-shaye barazana ce ga goben Nijeriya, Buba Marwa ya gargaɗi matasa

Shugaban Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA), Manjo Janar Buba Marwa (mai ritaya), ya bayyana cewa shan miyagun ƙwayoyi a tsakanin matasa na daga cikin manyan abubuwan da ke yi wa makomar Najeriya barazana.

Marwa ya yi wannan gargadi ne a Abuja yayin wani shirin kwallon ƙafa na wayar da kan matasa kan illolin miyagun ƙwayoyi mai taken “Kick Out Drug Abuse” (KODA), wanda Richy Gold International Ltd ta shirya tare da haɗin gwiwar NDLEA.

Ya ce matasa na ta amfani da ƙwayoyi irin su taba, giya, wiwi, tramadol, codeine da hodar iblis a makarantu da yankunan al’umma, abin da ke illa ga lafiyarsu da makomarsu.

“Waɗannan ƙwayoyi na jawo rugujewar iyalai, ɓata tunani, tashin hankali da ƙaruwar aikata laifuka,” in ji shi.

Shugaban NDLEA ya jaddada cewa rigakafi shi ne mafi ingancin kariya, inda ya yaba da amfani da kwallon ƙafa wajen jawo matasa zuwa hanyar kirki da nisantar da su daga miyagun ɗabi’u.

Ya kuma yi kira ga matasa da su rungumi taken “Kick Out Drug Abuse” a matsayin hanyar rayuwa, yana mai jaddada cewa babu ɗan kwallon da zai iya dorewa a wasa da rayuwa idan yana shan miyagun ƙwayoyi.

Shi ma Babban Daraktan Richy Gold International Ltd, Jude Onwusonye, ya bayyana cewa shirin KODA ba aiki ba ne kawai, illa dai kira ne na kare makomar matasa da kuma gina al’umma mai koshin lafiya da ci gaba.

Mun shirya dakon mai kyauta daga matatar Dangote - Ƙungiyar dillalan mai na Arewa Ƙungiyar Dillalan Mai da Iskar Gas ta ...
23/09/2025

Mun shirya dakon mai kyauta daga matatar Dangote - Ƙungiyar dillalan mai na Arewa

Ƙungiyar Dillalan Mai da Iskar Gas ta Arewa (AROGMA) ta bayyana cewa mambobinta sun shirya fara ɗebo kayayyakin mai daga matatar Dangote domin amfana daga shirin dakon mai kyauta.

Shugaban AROGMA, Bashir Danmallam, ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar a Kano a ranar Talata, bayan ziyarar da ƙungiyar ta kai wa Halima Dangote, Babban Darakta (Harkokin Kasuwanci) na matatar Dangote, a gidanta da ke Kano a ranar Lahadi.

A cikin sanarwar, Danmallam ya tabbatar da cewa mambobin AROGMA za su fara ɗebo kayayyakin man daga masana’antar nan ba da jimawa ba.

A cewarsa, wannan damar ta isar da kayayyakin kyauta ba wai mambobin ƙungiyar kaɗai za ta amfani ba, har da mabukata a fadin ƙasar.

“Wannan dama ce, kuma muna kira ga mambobinmu su yi amfani da ita wajen samun kayayyakin ba tare da biyan kuɗin dako ba a halin yanzu.

“Wannan dama ba wai ga mambobin AROGMA kaɗai ba ce, har ma ga mabukata da jama’ar Najeriya baki ɗaya,” in ji shi.

Shugaban AROGMA ya jaddada cewa ƙoƙarin Dangote na kafa masana’antar mai abin yabo ne kuma na kishin ƙasa, domin ya ceci ƙasar daga matsalar mak**ashi da ta musayar kuɗi ta hanyar kawo ƙarshen dogaro da shigo da mai daga waje.

Ya ƙara da cewa a yayin ziyarar, shugabannin AROGMA sun tattauna sosai kan yadda za su ɗebo mai ga mambobinsu, inda Babban Darakta ta amince cewa yin rajista da ɗebo kayayyakin zai kasance kyauta a halin yanzu.

22/09/2025
22/09/2025
Da Dumi-DumiGwamnan Kano ya sauya wa kwamishinan shari'a Barr. Haruna Isa Dederi wurin aiki, ya mayar da shi ma'aikatar ...
22/09/2025

Da Dumi-Dumi

Gwamnan Kano ya sauya wa kwamishinan shari'a Barr. Haruna Isa Dederi wurin aiki, ya mayar da shi ma'aikatar kula da harkokin sufuri

Sanarwar da Sanusi Bature Dawakin Tofa, mai magana da yawun gwamnan Kano ya fitar ta ce gwamnan ya kuma umurci babban sakatare na ma'aikatar shari'ar Barr. Mustapha Nuruddeen Muhammad ya koma aiki a ma'aikatar kula da muhalli. Gwamnan na Kano ya ce wannan umurni ne na nan take, inda ya bukaci daga ranar Talata 23 ga watan Satumba manyan jami'an su k**a aiki a ma'aikatun da ya tura su.

21/09/2025
TA LEƘO TA KOMA: Ba mu baiwa Rarara digirin girmamawa ba, ƴan damfara ne su ka bashi - Jami'ar European-American Jami’ar...
21/09/2025

TA LEƘO TA KOMA: Ba mu baiwa Rarara digirin girmamawa ba, ƴan damfara ne su ka bashi - Jami'ar European-American

Jami’ar European-American ta fitar da sanarwa da ta ke barranta kan ta da digirin girmamawa da aka baiwa shahararren mawaki, Dauda Kahutu Rarara ba, inda ta ce ba da izinin ta kuma ba ta yarjewa kowa ya bada digiri ga mawaƙin ba.

A wani taro da aka shirya a otal din Nicon Luxury a Abuja a jiya Asabar, wanda gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya halarta tare da wasu manyan baki, an baiwa Rarara wannan digiri na girmamawa ta hannun wasu mutane da s**a nuna kansu a matsayin wakilan jami’ar.

Amma a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafin ta na yanar gizo, muhukuntan jami’ar sun nisanta kan su da Rarara da kuma jami’an da s**a nuna kansu a matsayin wakilan jami’ar.

"Jami’ar ba ta ba da izinin gudanar da wani bikin kammala karatu a wannan wuri a yau ba, kuma wannan taron an shirya shi ne ta hanyar damfara ba tare da sanin jami’ar ba ko amincewarta.

" Wadanda s**a shirya wannan taron sun yaudari wasu mutane cewa su ne wakilan Jami’ar European-American, amma wannan ba gaskiya ba ne, kuma ba su da wani hurumin yin hakan ko karbar kudi a madadin jami’ar," in ji sanarwar.

DA ƊUMI-ƊUMI: Tinubu ya janye dokar-ta-ɓaci a jihar Rivers tare da umartar Fubara ya dawo aiki Shugaban kasa Bola Ahmed ...
17/09/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Tinubu ya janye dokar-ta-ɓaci a jihar Rivers tare da umartar Fubara ya dawo aiki

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kawo ƙarshen dokar-ta-baci da ya kakaba a Jihar Rivers daga daren yau Laraba, 17 ga Satumba, 2025.

Tinubu, a wata sanarwar da kakakin da, Bayo Onanuga ya fitar, ya umarci Gwamna Fubara, mataimakiyar sa Ngozi Nma Odu da kakakin majalisar Martins Amaewhule tare da sauran ‘yan majalisa da su koma bakin aiki daga Laraba, 18 ga Satumba, 2025.

Tinubu ya bayyana cewa ya ayyana dokar ta-baci a ranar 18 ga Maris, 2025 ne bayan rikicin siyasa tsakanin Gwamna Siminalayi Fubara da majalisar dokokin jihar ya haifar da durƙushewar ayyukan gwamnati.

Ya ce dokar-ta-bacin ta zama dole ne domin hana jihar fadawa cikin tarzoma, inda aka dakatar da gwamna, mataimakiyar gwamna da ‘yan majalisa na tsawon watanni shida.

Ya yi kira ga shugabannin siyasa a duk fadin kasar da su tabbatar da zaman lafiya da kyakkyawar alaka tsakanin bangarorin gwamnati domin bai wa jama’a damar amfana da dimokuradiyya.

24/09/2024
Bankin CBN ya kara kudin ruwa zuwa 27.25%Ku bayyana mana ra’ayinku.
24/09/2024

Bankin CBN ya kara kudin ruwa zuwa 27.25%
Ku bayyana mana ra’ayinku.

Shugaban rukunin kamfanonin BUA Alhaji Abdul Samad Rabiu ya ba da gudunmawar naira biliyan biyu don tallafa wa mutanen d...
24/09/2024

Shugaban rukunin kamfanonin BUA Alhaji Abdul Samad Rabiu ya ba da gudunmawar naira biliyan biyu don tallafa wa mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a birnin Maiduguri na jihar Borno.

Shafin X na rukunin kamfanonin ya wallafa a shafinsa a ranar Talata cewa, wakilan Alhaji Abdul Samad ne s**a bayyana haka yayin ziyarar jaje da s**a kai wa gwamna Babagana Umara Zulum a Maiduguri.

Sanarwar ta ce gudunmawar ta hada da tsabar kudi naira biliyan daya da kuma kayan abinci da darajarsu ta kai ta naira biliyan daya su ma.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Abba Go Again 2027. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share