Aminchi Tv

Aminchi Tv Islamic Programs | News | Tech | Current Affairs | Entertainment |
(1)

Dan ga ne da harin ranar talata 9 ga watan Satumba 2025 da Isra'ila ta kai a Doha babban birnin Qatar:Masana kan harkoki...
10/09/2025

Dan ga ne da harin ranar talata 9 ga watan Satumba 2025 da Isra'ila ta kai a Doha babban birnin Qatar:

Masana kan harkokin diflomasiya da siyasar duniya sun shaida wa ma nema labarai cewa harin da Isra'ila ta kai kan manyan jagororin Hamas a Doha babban birnin kasar Qatar.

Zai iya lalata ƙoƙarin tsagaita wuta a Gaza tare da yin illa ga alaƙar Amurka a Gabas ta Tsakiya.

Kasar Isra'ila ta bayyana harin da ta kai a tsakiyar birnin Doha a matsayin harin kan shugabannin Hamas.

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya bayyana cewa wannan hari martani ne kan harin bindiga da aka kai a Urushalima a ranar da ta gabata wanda ya kashe mutum shida.

Da kuma yin ruwa da tsaki da Hamas ta taka a hare-haren da aka kai kan Isra'ila a shekaru biyun da su ga bata.

Shin ya ku ganin zai kaya tsakanin Gabas ta Tsakiya da Amurka dan gane da kyakkyawar alaƙarsu da ita???






TV

Muhammad Bin Usman Aminchi Tv

A birnin Kumasi na kasar Ghana, wata kotu ta yanke wa wasu ’yan Najeriya uku hukuncin dauri na tsawon shekaru 96 kowanne...
10/09/2025

A birnin Kumasi na kasar Ghana, wata kotu ta yanke wa wasu ’yan Najeriya uku hukuncin dauri na tsawon shekaru 96 kowannensu, bayan tabbatar musu da laifin satar motoci.

Jami’an tsaro sun bayyana cewa an damke su ne a ranar 20 ga Yuni, 2025, sak**akon bincike kan motocin da s**a ɓace a cikin birnin.

Lamarin na zuwa ne a wani lokaci da ake ƙara nuna damuwa kan karuwar aikata laifuka da ake dorawa bakin haure, musamman daga Najeriya.

Shin irin waɗannan laifuka na da tasiri wajen lalata suna da dangantakar ’yan Najeriya a ƙasashen waje?

Poland ta kira taron gaggawa na NATO bayan da aka gano jiragen dron na Rasha sun kutsa cikin sararin samaniyarta sau 19 ...
10/09/2025

Poland ta kira taron gaggawa na NATO bayan da aka gano jiragen dron na Rasha sun kutsa cikin sararin samaniyarta sau 19 a daren da aka kai hare-hare a Ukraine.

Firayim Minista Donald Tusk ya ce sojojin Poland tare da haɗin gwiwar abokan kawance sun harbo akalla jirage uku, inda ya bayyana lamarin a matsayin babbar barazana ga tsaro.

Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya gargadi cewa wannan abu na iya zama hatsarin da zai shafi dukan Turai, yana mai kira ga ƙasashen Yamma su ɗauki mataki mai ƙarfi.

Poland ta yi amfani da Sashe na 4 na yarjejeniyar NATO, wanda ke bai wa kowace ƙasa mamba damar neman taro idan tana ganin tsaro da cikakken ‘yancinta na cikin haɗari.

Shin kutse na dron ɗin Rasha cikin Poland na iya janyo rikici kai tsaye tsakanin NATO da Rasha?

Wani lauya, Douglas Ogbankwa, ya soki dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan da Majalisar Dattawa ta yi na tsawon wat...
10/09/2025

Wani lauya, Douglas Ogbankwa, ya soki dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan da Majalisar Dattawa ta yi na tsawon watanni shida, yana mai cewa matakin ya saba wa kundin tsarin mulki.

Ya bayyana cewa Sanata ba ma’aikaciyar majalisa bace, illa wakiliyar jama’a, don haka majalisa ba ta da hurumin hana al’umma wakilci. Ogbankwa ya ce hukuncin ya zo ne yayin da batun ke gaban kotu, abin da ya kira nuna son zuciya.

Sai dai ya nuna cewa Sanatar ta yi kuskure wajen kin bin tsarin zauren majalisa lokacin muhawara.

Shin ya dace a hana al’umma wakilcinsu saboda sabani a cikin majalisa?

An sake samun katsewar wutar lantarki a Najeriya a ranar Laraba bayan rushewar layin wutar kasa baki ɗaya. Matsalar ta f...
10/09/2025

An sake samun katsewar wutar lantarki a Najeriya a ranar Laraba bayan rushewar layin wutar kasa baki ɗaya. Matsalar ta faru ne tsakanin ƙarfe 11 na safe zuwa 12 na rana, lamarin da ya janyo raguwa sosai a samar da wuta.

Kamfanonin rarraba wuta irin su AEDC da PHED sun tabbatar da matsalar, inda s**a ce ta shafi jihohin da suke ba da hidima ciki har da Rivers, Bayelsa, Akwa Ibom, Cross River da kuma babban birnin tarayya Abuja.

Sun roki jama’a da su yi haƙuri, tare da bayyana cewa ana ci gaba da kokarin dawo da wutar da zarar an gyara tsarin.

A ganinku Me ke jawo yawaitar faduwar layin wutar lantarki a Najeriya — matsalar fasaha ce, ko rashin ingantaccen tsarin kula da shi?

A jiya talata 9/9/2025 Gwamnatin jahar Kano karkashin mai girma gwamna Abba Kabir Yusuf ta bawa Malama Zainab muƙami.Mal...
10/09/2025

A jiya talata 9/9/2025 Gwamnatin jahar Kano karkashin mai girma gwamna Abba Kabir Yusuf ta bawa Malama Zainab muƙami.

Malama Zainab itace babbar diyar babban malamin addinin Muslunci a Afrika ta yamma wato Sheikh Ja'afar Mahmud Adam (R.H) wanda aka kashe ranar 14/4/2007 sak**akon harin ƴan ta adda. Allah Ya jikansa Ya gafarta masa.

An bata mukami a matsayin mamba a shura council ta jahar kano.

Malama Zainab tayi fice ne wajen karatu da karantarwa a faɗin Nijeriya da sauran kasashen Afrika wanda tafi karkatar da akalar karantarwanta ga mata ƴan' uwanta.

Kafin wannan muƙamin, ita ce shugaban (nisa'us sunnah ta jahar).

ALLAH Ya Taya ta Riƙo Yasa Yazam Silar Alkhairi Gare ta Da Al'umma Baki Ɗaya.

Wacce irin shawara ce za ku bawa Malama akan wannan muƙamin???

Muhammad Bin Usman Aminchi Tv faɗi alkhairi.......

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta kawo karshen matsalar wutar lantarki da ke addabar asi...
10/09/2025

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta kawo karshen matsalar wutar lantarki da ke addabar asibitoci a faɗin Najeriya.

Tinubu, ta bakin SGF Sanata George Akume, ya ce bai k**ata a ci gaba da rasa rayuka saboda katsewar wuta a dakin tiyata, haihuwa da gaggawa ba. Ya tabbatar da cewa gwamnati za ta rungumi sabbin hanyoyi, musamman mak**ashi mai sabuntawa, tare da haɗin gwiwar masu zaman kansu domin samar da tsayayyen wuta a asibitoci.

Sai dai rahotanni sun nuna cewa duk da tallafin wuta da aka sanar, da dama daga cikin asibitoci har yanzu na ci gaba da fama da rashin wuta, lamarin da ke jefa rayukan marasa lafiya cikin haɗari.

Shin ko wani hali na yanayin asibitocin yankunanku ke fuskanta a yauzu? Duba da matakan da gwamnati ke cewa tana dauka?

Isra’ila ta kare kanta kan harin da ta kai wa wasu shugabannin Hamas a Qatar, duk da s**a daga Shugaban Amurka Donald Tr...
10/09/2025

Isra’ila ta kare kanta kan harin da ta kai wa wasu shugabannin Hamas a Qatar, duk da s**a daga Shugaban Amurka Donald Trump, wanda ya ce bai samu sanarwa kafin harin ba.

Qatar ta bayyana cewa ba ta samu wani gargadi daga Amurka ba sai bayan an fara luguden, duk da kasancewarta cibiyar rundunar sojojin Amurka da kuma mai taka rawa wajen sasanta rikicin Gaza.

Isra’ila ta ce ba Qatar ta kai hari ba, sai dai Hamas, inda aka kashe mutane shida ciki har da ɗan babban mai shiga tsakani na ƙungiyar. Firayim Ministan Qatar ya ce wannan hari na iya zama “muƙamin juyin siyasa” a yankin, yayin da Netanyahu ya ce an kai shi ne a matsayin ramuwar gayya kan harin Hamas a Urushalima.

Tun bayan rikicin da Hamas ta tayar a Oktoba 2023, Isra’ila ta kashe sama da 64,000 Falasdinawa a Gaza, mafi yawansu fararen hula.

Shin wannan hari zai iya dagula dangantakar Isra’ila da Qatar da sauran kasashen Larabawa?

Rundunar Sojin Najeriya ta sanar da cewa cikin sa’o’i 48, dakarunta sun ceto mutane tara da aka yi garkuwa da su tare da...
10/09/2025

Rundunar Sojin Najeriya ta sanar da cewa cikin sa’o’i 48, dakarunta sun ceto mutane tara da aka yi garkuwa da su tare da cafke mutane 11 da ake zargi da samar da kayan tallafi ga ‘yan ta’adda.

An kuma kwace shanu 114, tumaki tara, kuɗi sama da naira miliyan ɗaya, bindiga, harsashi, da man fetur a wasu sassan ƙasar.

Hare-haren sojin sun gudana a jihohi da dama ciki har da Borno, Katsina, Ogun, Bayelsa, Edo, Taraba, Filato da Kaduna, inda aka tarwatsa sansanonin masu laifi da kuma k**a wasu da ake zargi da kisan kai da sata.

Sojojin sun jaddada cewa za su ci gaba da ayyukan da nufin hana ‘yan ta’adda da sauran miyagu sararin aikata laifuka a duk fadin ƙasa.

Shin kana ganin irin waɗannan nasarorin da sojojin ke samu za su taimaka wajen kawo ƙarshen ta’addanci a Najeriya?

10/09/2025

Kasashe na cigaba da yin Allah wadai da harin Isra'ila akan Qatar.

Abdullahi Isah Aliyu ne ke dauke da rahoton...



Iran ta fito fili ta soki harin da Isra’ila ta kai birnin Doha na kasar Qatar.Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Es...
09/09/2025

Iran ta fito fili ta soki harin da Isra’ila ta kai birnin Doha na kasar Qatar.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghaei, ya bayyana a wani jawabi cewa wannan hari ya sabawa ka’idojin kasa da kasa tare da keta mutuncin Qatar.

Ya ce wannan lamari ya zama darasi da gargadi ga kasashen yankin da ma sauran duniya, yana mai jaddada bukatar daukar matakan da zasu hana irin hakan a gaba.

A watan Yuni da ya gabata ne Iran da Isra’ila s**a rattaba hannu kan yarjejeniyar tsagaita wuta bayan rikicin da ya dauki kwanaki goma sha biyu.

Shin wannan rikici zai sake tayar da hankalin kasashen Gabas ta Tsakiya?

Sojojin Isra’ila sun ce sun kai hari na musamman kan manyan shugabannin Hamas a ranar Talata, lamarin da ya jawo fashe-f...
09/09/2025

Sojojin Isra’ila sun ce sun kai hari na musamman kan manyan shugabannin Hamas a ranar Talata, lamarin da ya jawo fashe-fashe a Doha, babban birnin Qatar. Rundunar ta ce shugabannin da aka nufa suna da hannu wajen shirya harin 7 ga Oktoba 2023 da kuma ci gaba da yaƙin Gaza.

Harin ya zo ne bayan Isra’ila ta yi alkawarin kai farmaki kan dukkan shugabannin Hamas, ko a cikin Gaza ko a ƙasashen waje. A gefe guda, tattaunawar tsagaita wuta tsakanin Hamas da Isra’ila, wadda Qatar, Masar da Amurka ke shiga tsakani, ta ci gaba da fuskantar cikas.

Fatanmu ga ‘yan Hamas: Allah Ya ba su ƙarfin guiwa da nasara a kan zalunci.

’a

Address

Kano

Telephone

+2347045989882

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Aminchi Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Aminchi Tv:

Share