Aminchi Tv

Aminchi Tv Labarai • Addini • Ilimi • Siyasa • Nishadi
(5)

Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, ya bukaci tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan, da kada ya amince da ti...
31/05/2026

Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, ya bukaci tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan, da kada ya amince da tikitin takarar shugaban ƙasa da wani ɓangare na jam’iyyar PDP ya ba shi domin zaɓen 2027.

Keyamo ya ce wannan ɓangaren jam’iyyar ba ya da sahalewar hukumomin da s**a dace, yana mai gargadin cewa amincewa da irin wannan tikiti na iya haifar da ruɗani da ce-ce-ku-ce a harkokin siyasa.

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya bayyana cewa Rabiu Musa Kwankwaso ba zai zama mai kallo a gefe...
31/05/2026

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya bayyana cewa Rabiu Musa Kwankwaso ba zai zama mai kallo a gefe ba idan s**a samu nasara a zaɓen 2027.

Obi ya ce mataimakin shugaban ƙasa zai kasance muhimmin abokin aiki a tafiyar da mulki da yanke manyan shawarwari, domin tabbatar da haɗin kai da ingantaccen shugabanci a ƙasar nan.

Ƙungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) ta bayyana cewa shirin ƙara mafi ƙarancin albashi zuwa Naira 100,000 ba zai wadatar w...
31/05/2026

Ƙungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) ta bayyana cewa shirin ƙara mafi ƙarancin albashi zuwa Naira 100,000 ba zai wadatar wajen magance matsalolin rayuwar ma’aikata ba, tana mai cewa abin da ya dace da halin tattalin arzikin ƙasar yanzu shi ne biyan ma’aikata akalla Naira miliyan ɗaya a wata.

Mai magana da yawun NLC, Benson Upah, ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi yayin da yake mayar da martani ga shawarar da gwamnoni ke nazarin yi na ƙara mafi ƙarancin albashi zuwa N100,000.

Tun da farko, shugaban kungiyar gwamnoni kuma gwamnan Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana cewa gwamnoni na tattaunawa kan yiwuwar sake duba mafi ƙarancin albashi saboda hauhawar farashi da tsadar rayuwa da ma’aikata ke fuskanta.

Sai dai Upah ya ce duk da cewa shawarar ta nuna an damu da walwalar ma’aikata, adadin Naira 100,000 bai kai matsayin da zai iya biyan buƙatun rayuwa a halin yanzu ba.

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta sanar da k**a harsasai 380 na bindigogin soja a kan hany...
31/05/2026

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta sanar da k**a harsasai 380 na bindigogin soja a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna, tare da miƙa wanda ake zargi da kayayyakin da aka k**a ga hukumomin tsaro domin ci gaba da bincike.

A cewar hukumar, jami’an ta sun k**a wani mutum mai suna Sunusi Musa mai shekaru 30 a yankin Jere da ke kan hanyar Abuja zuwa Kaduna a ranar 24 ga Mayu, 2026, kuma ana zargin sa da ɗaukar harsasan zuwa jihar Katsina.

Mai magana da yawun NDLEA, Femi Babafemi, ya bayyana cewa harsasan da aka k**a nau'in 7.62mm ne, waɗanda ake amfani da su a bindigun sojoji.

Ya ce wannan nasarar na daga cikin ƙoƙarin hukumomin tsaro na dakile yaduwar mak**ai da harsasai ba bisa ka’ida ba.

A wani samame daban a jihar Kaduna, jami’an NDLEA sun k**a wasu ma’aurata, Musa Sunday da Mercy Sunday, tare da wani mutum mai suna Salomi Ezekiel bayan sun kwace buhuna 100 na tabar wiwi masu nauyin kilogram 1,246 a yankin Gonin Gora.

Gwamnatin Ostiraliya ta amince da sayen jiragen ruwa na yaki masu amfani da mak**ashin nukiliya guda uku da aka riga aka...
31/05/2026

Gwamnatin Ostiraliya ta amince da sayen jiragen ruwa na yaki masu amfani da mak**ashin nukiliya guda uku da aka riga aka yi amfani da su, a karkashin sabuwar yarjejeniyar tsaro ta AUKUS da ke tsakaninta da Amurka da Birtaniya.

A tsarin farko na yarjejeniyar, an tsara cewa Ostiraliya za ta karɓi jirgi biyu da aka yi amfani da su daga Amurka, sannan kuma ta samu guda ɗaya sabo daga nau’in Virginia-class. Sai dai sabon tsari da aka yi wa kwaskwarima yanzu ya sauya wannan shiri, inda aka fi karkata ga sayen jiragen da aka riga aka yi amfani da su.

Wannan mataki na daga cikin ƙoƙarin ƙarfafa tsaron yankin Indo-Pacific, tare da ci gaba da haɗin gwiwar soji tsakanin ƙasashen uku domin daidaita ƙarfin tsaro a yankin.

Gwamnatin Norway ta bayyana cewa ta yi wa Malaysia uzuri dangane da matakin da ta dauka na soke lasisin fitar da makami ...
31/05/2026

Gwamnatin Norway ta bayyana cewa ta yi wa Malaysia uzuri dangane da matakin da ta dauka na soke lasisin fitar da makami na Naval Strike Missile (NSM) da aka shirya kai wa rundunar sojin ruwan Malaysia. Sai dai ta jaddada cewa har yanzu tana kan matsayinta na dakatar da yarjejeniyar.

Ministan Tsaron Malaysia, Mohamed Khaled Nordin, ya bayyana cewa Oslo ta yi bayanin dalilan da s**a sa ta soke lasisin fitar da mak**an, inda ta ce matakin ya samo asali ne daga sabon tsauraran dokokin fitar da wasu fasahohin mak**ai masu matukar muhimmanci.

A cewar rahotanni, an riga an biya kusan kashi 95 cikin 100 na kudin yarjejeniyar tun kafin a dakatar da ita, lamarin da ya jawo cece-kuce da kuma matukar damuwa a Malaysia, musamman ganin cewa mak**an na da muhimmiyar rawa a shirin sabunta sojojin ruwan kasar.

Malaysia na ci gaba da nuna rashin amincewa da wannan mataki, tare da nazarin yiwuwar neman diyya ko daukar matakin shari’a kan lamarin.

A nata bangaren, Norway ta ce matakin ya shafi tsare-tsaren tsaro ne da kuma takaita fitar da fasahohin mak**ai zuwa wasu kasashe, tare da jaddada cewa tana son ci gaba da kyakkyawar dangantaka da Malaysia duk da wannan sabani.

Shin kuna ganin ya dace ƙasa ta soke yarjejeniyar mak**ai bayan an kusa kammala biyan kuɗi, ko kuwa hakan rashin adalci ne ga ƙasa mai saye?

Kasar Korea ta Kudu ta bayyana cewa ta gudanar da tattaunawa da Japan kan wata sabuwar yarjejeniya da za ta tanadi yadda...
31/05/2026

Kasar Korea ta Kudu ta bayyana cewa ta gudanar da tattaunawa da Japan kan wata sabuwar yarjejeniya da za ta tanadi yadda kasashen biyu za su rika musayar tallafin soji da kuma jigilar kayan aikin tsaro a tsakaninsu.

Rahotanni sun bayyana cewa wannan mataki na daga cikin kokarin karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu a fannin tsaro, musamman a yankin Asiya da ke fuskantar kalubalen tsaro daga wasu bangarori.

Korea ta Kudu ta kara da cewa har yanzu ana ci gaba da nazari kan batun, kuma ba a kammala cimma matsaya ta karshe ba.

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta yi kira ga ’yan Najeriya da su ci gaba da kasancewa masu fata na gari...
31/05/2026

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta yi kira ga ’yan Najeriya da su ci gaba da kasancewa masu fata na gari da kuma addu’a duk da matsalolin tsaro da ake fuskanta a wasu sassan ƙasar nan.

Ta bayyana hakan ne a ranar Asabar, yayin wani taron mata da aka gudanar a dandalin Ekitikete Pavilion da ke Ado Ekiti, inda ta tabbatar wa jama’a cewa gwamnatin tarayya tare da hukumomin tsaro da kuma abokan hulɗar ƙasa da ƙasa suna aiki domin magance matsalolin tsaron da ake fama da su.

Mahukuntan Iran na ci gaba da shirye-shiryen gudanar da wata gagarumar jana’iza ta kasa domin karrama marigayi Jagoran J...
31/05/2026

Mahukuntan Iran na ci gaba da shirye-shiryen gudanar da wata gagarumar jana’iza ta kasa domin karrama marigayi Jagoran Juyin Juya Halin Kasar, Ayatullah Ali Khamenei, wanda ya rasu sak**akon hare-haren hadin gwiwar Amurka da Isra’ila da s**a tayar da rikici a yankin.

Rahotanni daga kafafen yada labaran gwamnati sun bayyana cewa an kafa kwamitin musamman da zai jagoranci dukkan shirye-shiryen jana’izar, tare da hada kai da hukumomi daban-daban domin tabbatar da an gudanar da taron cikin tsari da inganci.

Tun bayan mutuwarsa, an sha dage ranar jana’izar saboda matsalolin tsaro da kuma rikice-rikicen da s**a biyo bayan yakin. Sai dai jami’ai sun ce ana ci gaba da shirye-shiryen kammala dukkan matakan da s**a dace kafin sanar da ranar gudanar da ita.

Ayatullah Ali Khamenei, wanda ya kasance Jagoran Kolin Iran na fiye da shekaru 30 bayan juyin juya halin Musulunci na shekarar 1979, ya kasance daya daga cikin fitattun shugabannin siyasa da addini a tarihin kasar.

Mahukuntan Iran na sa ran miliyoyin mutane za su halarci jana’izar da zarar an bayyana ranar gudanar da ita, lamarin da zai iya sanya ta cikin manyan jana’izun gwamnati mafi girma a tarihin kasar.

Wasu da ake zargin ƴan daba ne sun tarwatsa taron shugabannin jam'iyyar PDP ƙarƙashin jagorancin Kabiru Turaki a cibiyar...
31/05/2026

Wasu da ake zargin ƴan daba ne sun tarwatsa taron shugabannin jam'iyyar PDP ƙarƙashin jagorancin Kabiru Turaki a cibiyar taruka ta A-Class Event Centre da ke Abuja.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne jim kaɗan bayan shugabannin ɓangaren jam'iyyar sun koma wurin domin ganawa da jami'an tsaro da aka girke a wajen.

Tun da farko, ɓangaren PDP na Kabiru Turaki ya gudanar da Babban Taron Musamman na Ƙasa a ofishin sa da ke Area 10 a Abuja, inda ya amince da tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar a zaɓen 2027.

Shugabannin jam'iyyar sun bayyana cewa sun koma ofishin Area 10 ne bayan jami'an tsaro sun toshe hanyar shiga cibiyar taron ta A-Class Event Centre, wadda aka shirya gudanar da taron a cikin ta.

Bayan kammala bikin amincewa da Jonathan, shugabannin jam'iyyar sun koma cibiyar taron domin abin da s**a bayyana a matsayin tattaunawa da jami'an 'yan sanda da ke wurin.

Sai dai jim kaɗan bayan Kabiru Turaki ya kammala jawabin sa, wasu matasa da s**a iso cikin motocin bas guda biyu dauke da manyan sanduna s**a kai farmaki kan jami'an jam'iyyar yayin da suke komawa motocin su.

Harin ya tilasta wa shugabannin jam'iyyar, 'yan jarida da sauran mahalarta taron tserewa domin tsira da rayukansu.

Daga bisani, jami'an 'yan sanda da sauran hukumomin tsaro sun dawo da zaman lafiya a wurin.

Address

Kano

Telephone

+2347045989882

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Aminchi Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Aminchi Tv:

Share