31/05/2026
Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta sanar da k**a harsasai 380 na bindigogin soja a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna, tare da miƙa wanda ake zargi da kayayyakin da aka k**a ga hukumomin tsaro domin ci gaba da bincike.
A cewar hukumar, jami’an ta sun k**a wani mutum mai suna Sunusi Musa mai shekaru 30 a yankin Jere da ke kan hanyar Abuja zuwa Kaduna a ranar 24 ga Mayu, 2026, kuma ana zargin sa da ɗaukar harsasan zuwa jihar Katsina.
Mai magana da yawun NDLEA, Femi Babafemi, ya bayyana cewa harsasan da aka k**a nau'in 7.62mm ne, waɗanda ake amfani da su a bindigun sojoji.
Ya ce wannan nasarar na daga cikin ƙoƙarin hukumomin tsaro na dakile yaduwar mak**ai da harsasai ba bisa ka’ida ba.
A wani samame daban a jihar Kaduna, jami’an NDLEA sun k**a wasu ma’aurata, Musa Sunday da Mercy Sunday, tare da wani mutum mai suna Salomi Ezekiel bayan sun kwace buhuna 100 na tabar wiwi masu nauyin kilogram 1,246 a yankin Gonin Gora.