
10/09/2025
Dan ga ne da harin ranar talata 9 ga watan Satumba 2025 da Isra'ila ta kai a Doha babban birnin Qatar:
Masana kan harkokin diflomasiya da siyasar duniya sun shaida wa ma nema labarai cewa harin da Isra'ila ta kai kan manyan jagororin Hamas a Doha babban birnin kasar Qatar.
Zai iya lalata ƙoƙarin tsagaita wuta a Gaza tare da yin illa ga alaƙar Amurka a Gabas ta Tsakiya.
Kasar Isra'ila ta bayyana harin da ta kai a tsakiyar birnin Doha a matsayin harin kan shugabannin Hamas.
Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya bayyana cewa wannan hari martani ne kan harin bindiga da aka kai a Urushalima a ranar da ta gabata wanda ya kashe mutum shida.
Da kuma yin ruwa da tsaki da Hamas ta taka a hare-haren da aka kai kan Isra'ila a shekaru biyun da su ga bata.
Shin ya ku ganin zai kaya tsakanin Gabas ta Tsakiya da Amurka dan gane da kyakkyawar alaƙarsu da ita???
TV
Muhammad Bin Usman Aminchi Tv