Aminchi Tv

Aminchi Tv Islamic Programs | News | Tech | Current Affairs | Entertainment |
(1)

Jam’iyyar ADC ta zargi gwamnatin Shugaba Tinubu da amfani da mutuwar Muhammadu Buhari a matsayin dabara ta siyasa domin ...
19/07/2025

Jam’iyyar ADC ta zargi gwamnatin Shugaba Tinubu da amfani da mutuwar Muhammadu Buhari a matsayin dabara ta siyasa domin gyara hotonta musamman a Arewacin ƙasa.

Jam’iyyar ta ce girmamawar da gwamnati ta nuna k**ar zaman majalisar ministoci da bayyana ɗan Buhari a bainar jama’a ba ta fito daga zuciya ba, illa wani salo ne na yaudara da neman karɓuwa bayan ta jima tana s**ar Buhari da manufofinsa.

ADC ta ce al’umma sun fahimci wannan makirci, kuma ba zai iya gyara hoton gwamnati da ke fuskantar ƙalubale ba.



Sanata Natasha Ta Sanar Za Ta Koma Majalisa A Ranar Talata Mai Zuwa, Duk Da Daukaka Ƙarar AkpabioSanata mai wakiltar Kog...
19/07/2025

Sanata Natasha Ta Sanar Za Ta Koma Majalisa A Ranar Talata Mai Zuwa, Duk Da Daukaka Ƙarar Akpabio

Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta tabbatar da cewa zata koma zaman Majalisar Dattawa a ranar Talata, 22 ga Yuli, 2025, bisa hukuncin kotu, duk da cewa Shugaban Majalisa, Godswill Akpabio, ya ɗaukaka ƙara domin kalubalantar wannan hukunci.

Yayin da take jagorantar wani shirin horar da matasa a mazabarta ranar Asabar, Natasha ta bayyana cewa ta riga ta rubuta wasiƙa zuwa Majalisa don sanar da shirin dawowarta a hukumance.

A cewarta, tana da cikakken kwarin gwiwa cewa doka za ta yi tasiri, kuma zata ci gaba da wakiltar al’ummarta da amana da rikon gaskiya.

Tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya isa garin Daura da ke Jiha...
19/07/2025

Tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya isa garin Daura da ke Jihar Katsina domin yin ta’aziyya kan rasuwar tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari.

Kwankwaso ya isa jihar ne a cikin kwanciyar hankali, inda ya zarce kai tsaye zuwa gidan marigayin domin jajanta wa iyalai da dangin shugaban a madadin kansa da kuma al’ummar jam’iyyar NNPP.

Ziyarar tasa ta zo ne kwanaki bayan rasuwar Buhari a Birtaniya, wacce ta girgiza Najeriya da ma duniya baki ɗaya. Kwankwaso ya bayyana marigayin a matsayin mutum mai tarihi wanda ya taka rawar gani a mulkin soja da na dimokuraɗiyya.

“A irin lokutan nan ne ake bukatar jajircewa da ɗaukaka zumunci. Mun zo ne domin mu nuna jimami da girmamawa,” in ji Kwankwaso yayin ziyarar.

Ziyarar ta ja hankalin jama’a, inda ake kallon ta a matsayin ɗaya daga cikin manyan alamun mutunta juna tsakanin shugabannin Najeriya — duk da bambancin siyasa.

A ganinka, ya dace da al’ada ne ko kuma siyasa ce ke tura manyan ‘yan siyasa zuwa irin waɗannan ziyarce-ziyarcen?

Wani ɗan gajeren hutu da tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, ya je Birtaniya domin duba lafiyarsa, ya ƙare da al...
19/07/2025

Wani ɗan gajeren hutu da tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, ya je Birtaniya domin duba lafiyarsa, ya ƙare da alhini bayan rasuwarsa a asibitin London Clinic da ke birnin Landan a ranar Lahadi, 13 ga Yuli, 2025.

Rahotanni sun bayyana cewa kafin mutuwarsa, Buhari yana cikin yanayi na murmurewa har ma da annashuwa a ranar Asabar, 12 ga Yuli — inda ake sa ran zai samu sallama cikin kwanaki masu zuwa. Sai dai daga bisani, lafiyarsa ta ɗauki wani sabon salo a tsakiyar Lahadi, wanda hakan ya kai ga rasuwarsa.

Tsohon shugaban mulkin soja, Janar Abdulsalami Abubakar, wanda shi ma yana kwance a wannan asibiti a lokacin, ya samu sauƙi kuma aka sallame shi kafin wannan ibtila’i ya afku ga abokinsa.

Dan uwan marigayin, Mamman Daura, ya tabbatar da cewa Buhari yana cikin koshin lafiya da annashuwa kafin al’amura su canza. A cewarsa, “Yana cikin nishadi a ranar Asabar. Mun yi fatan zai fito nan da kwanaki kaɗan. Amma ranar Lahadi lafiya ta sake tabarbarewa.”

Buhari ya bar gida Najeriya tun watan Afrilu don ci gaba da jinya, wacce ya jima yana karɓa a ƙasashen waje, musamman Birtaniya.

Ina Ne London Clinic?

London Clinic wani katafaren asibiti ne mai zaman kansa da ke tsakiyar birnin Landan, wanda aka kafa tun 1932. Asibitin ya shahara wajen kula da cututtuka masu tsanani k**ar ciwon daji (cancer), cututtukan ciki, tiyata da kuma sashin kulawa na musamman (ICU).

An fi ganinsa a matsayin wurin da manyan ’yan siyasa da mashahurai ke zuwa domin samun ingantacciyar lafiya. Har ila yau, wasu daga cikin dangin gidan sarautar Ingila sun taba karɓar jinya a nan.

Wani likitan Najeriya da ke aiki a Landan ya bayyana cewa asibitin na da kayan aiki na zamani da ƙwararrun likitoci daga sassa daban-daban na duniya. Ya ce farashin jinya a nan ba ƙarami ba ne – ganin likita na iya kaiwa daga £100 zuwa £750, yayin da tiyatar manyan cututtuka ke kaiwa daga £10,000 zuwa £13,000. Haka kuma kwana guda a sashen ICU yana kaiwa £3,500!

Yaushe Asibitocin Najeriya Za Su Habaka?

Rasuwar Buhari a irin wannan asibiti na ƙasashen waje ya sake tada muhawarar da ake ta yi tsawon shekaru a Najeriya — shin me ya sa shugabanninmu ke yawan barin ƙasar domin neman lafiya? Menene makomar cibiyoyin lafiyar cikin gida?

Wannan mutuwa ta bar darussa masu yawa ga ƙasa da kuma masu riƙe da madafun iko. Sai dai lokaci ne kaɗai zai nuna ko darasin zai zama koyi.

Tambaya ta musamman: Shin ya dace a sake duba tsarin kiwon lafiya na Najeriya bayan wannan al’amari?

Ku faɗi ra’ayinku.

Matasan jam’iyyar NNPP da na APC sun fara jayayya da nuna bajinta, inda kowanne bangare ke taƙama da cewa su ne s**a fi ...
19/07/2025

Matasan jam’iyyar NNPP da na APC sun fara jayayya da nuna bajinta, inda kowanne bangare ke taƙama da cewa su ne s**a fi nuna ƙauna da girmamawa ga shugaban ƙasa a lokacin zuwansa jihar.

A wasu hotuna da bidiyo da ke yawo a intanet, an ga dandazon jama’a suna tarba, amma kowanne bangare na cewa nasu ne ya fi yawa, tsari da kuzari. Wasu matasa na jam’iyyar APC sun bayyana cewa ganin yadda Tinubu ya samu karɓuwa da kuma tarba mai armashi a hannun gwamnati mai ci a jihar ne ke tabbatar da nasarar jam’iyyar a Kano.

A daya hannun kuma, matasan NNPP sun ce kasancewar jama’ar gari da dama s**a fito daga kwaryar birnin Kano don tarbar shugaban, duk da cewa su ba jam’iyyar APC ba ne, alama ce ta irin girman mutuncin da suke da shi ga Tinubu.

To sai dai tambayar da ake ci gaba da yi yanzu ita ce: Su wa ne s**a fi nuna bajinta da ƙauna ga shugaban ƙasa — matasan NNPP ko na APC?

A matsayinka na ɗan Najeriya ko ‘yar Najeriya, kai wa kake ganin ya fi nuna bajinta a wajen tarbar shugaban kasa a Kano?

A wani muhimmin taro da kwamitin zartarwa na ƙasa (NEC) na jam’iyyar Labour Party ya gudanar a birnin Abuja, an zaɓi San...
19/07/2025

A wani muhimmin taro da kwamitin zartarwa na ƙasa (NEC) na jam’iyyar Labour Party ya gudanar a birnin Abuja, an zaɓi Sanata Nenadi Usman a matsayin Shugabar Jam’iyyar ta riko a matakin ƙasa.

Haka kuma, an naɗa Sanata Darlington Nwokocha a matsayin Sakatare Janar na riko, tare da wasu sabbin shugabannin da za su jagoranci jam’iyyar har zuwa lokacin babban taron gangami da za a gudanar domin zaɓar sabbin shugabanni na dindindin.

An shirya cewa wannan kwamiti na riko zai kula da dukkan harkokin jam’iyyar daga yanzu har zuwa lokacin da za a kammala zaɓukan matakin mazabu, kananan hukumomi, jihohi, yankuna da kuma ƙasa baki ɗaya.

Kwamitin ya kuma amince da jadawalin gudanar da zaɓuka daga matakin ƙasa har zuwa tushe, inda aka umurci sakatariyar jam’iyyar da ta fitar da cikakkun ƙa’idoji da lokacin da za a bi don tabbatar da sahihin zaɓe mai cike da adalci da gaskiya.

Shugaban ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa (NLC), Mista Joe Ajaero, da Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti – wanda shi ne gwamnan jam’iyyar LP kaɗai a halin yanzu – sun halarci taron tare da wasu jiga-jigan jam’iyyar.

A jawabin sa, Joe Ajaero ya bayyana Labour Party a matsayin jam’iyyar talakawa, yana mai ƙarfafa mambobin jam’iyyar da su ci gaba da jajircewa duk da ƙalubalen da ake fuskanta.

“Duk wanda ba ya tare da mu, kuma ba ya aiki da masu fafutukar ƙwadago, amma ya ce shi ne shugaban jam’iyyar – wallahi yana mafarki ne kawai. Lokacin da ranar ƙididdiga ta zo, za mu ce ba mu san shi ba,” in ji Gwamna Otti.

Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo, ya bayyana cewa tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaɓen ...
19/07/2025

Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo, ya bayyana cewa tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023, Mista Peter Obi, ba zai ƙara samun damar shigowa jihar ba sai da cikakken izinin hukumomin tsaro.

Gwamnan ya fadi haka ne ranar Juma’a yayin da yake tofa albarkacin bakinsa kan ziyarar da Peter Obi ya kai garin Benin a ranar 7 ga Yuli, inda ya bai wa makarantar horar da nas da ke asibitin St Philomena kyautar Naira miliyan 15 domin kammala ayyukan ci gaba a makarantar.

Okpebholo ya bayyana damuwarsa da cewa ziyarar Obi ta zo dai-dai da lokacin da aka samu sake fitowar rikice-rikice da tashe-tashen hankula a wasu sassan jihar. Ya ce:

“Mutumin da ke cewa ba shi da ko sisi, amma sai ga shi ya ajiye Naira miliyan 15. Daga bisani kuma aka kashe mutane uku bayan tafiyarsa. Saboda haka, daga yanzu, ba zai ƙara shigowa Edo ba tare da cikakken izinin tsaro ba.”

A cewar gwamnan, jihar na fuskantar barazanar rashin zaman lafiya, kuma hakan ba zai ƙara samun gurbi ba a cikin shugabancinsa.

A wani ɓangare na jawabin nasa, Gwamna Okpebholo ya bayyana sauya sheƙar tsohon shugaban majalisar jihar, Marcus Onobun, daga jam’iyyar PDP zuwa APC a matsayin “ƙarshe kuma cikakken ciwo” ga jam’iyyar adawa a jihar.

Ya jaddada cewa jam’iyyar APC ta ƙwace cikakken mulkin jihar, kuma zuwa zaɓen 2027, babu wani ragowar jam’iyyar hamayya da zai rage a Edo.

Sakatare Janar Na Majalisar Dinkin Duniya, Guterres, Ya Karrama Buhari, Ya Nuna Jimamin RasuwarsaA jiya Juma'a, Sakatare...
19/07/2025

Sakatare Janar Na Majalisar Dinkin Duniya, Guterres, Ya Karrama Buhari, Ya Nuna Jimamin Rasuwarsa

A jiya Juma'a, Sakataren Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, António Guterres, ya ziyarci gidan Najeriya da ke birnin New York, inda ya girmama marigayi tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, tare da isar da sakon ta'aziyya ga gwamnatin Najeriya da al’ummar ƙasa.

Guterres ya bayyana Buhari a matsayin jagora mai kishin ƙasa, wanda sadaukarwarsa ga Najeriya, nahiyar Afirka da haɗin gwiwar duniya zai kasance abin tunawa har abada.

Saban Shugaban mabiya addinin kirista, Paparoma Leo na XIV ya yi kira da a kare wuraren ibada, yayin wata ganawa ta waya...
18/07/2025

Saban Shugaban mabiya addinin kirista, Paparoma Leo na XIV ya yi kira da a kare wuraren ibada, yayin wata ganawa ta waya da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, bayan harin da ya kashe mutane uku a cocin Katolika guda daya tilo da ke birnin Gaza.

A wata sanarwa da fadar Vatican ta fitar ranar Juma’a, an bayyana cewa Netanyahu ne ya fara kiran Paparoman, domin tattaunawa bayan harin da ya haifar da kakkausar s**a daga kasashen duniya.

Paparoman ya sake nanata bukatarsa ta a koma teburin sulhu, a samu tsagaita wuta da kuma kawo karshen yaki da ke janyo asarar rayuka da durkushewar rayuwar al’umma. Ya ce lamarin da ke faruwa a Gaza musamman yana da tsanani, inda yara, tsofaffi da marasa lafiya ke shiga cikin mawuyacin hali.

Ya kuma jaddada muhimmancin kare wuraren ibada da tabbatar da tsaron rayukan mabiya addinai da sauran jama’a a yankunan Falasdinu da Isra’ila baki ɗaya.

Netanyahu, a nasa bangaren, ya nuna “matukar nadama” bisa harin da ya afkawa cocin, yana mai cewa harin ba a nufin haka ba ne. Kakakinsa ya bayyana cewa tattaunawar tsakanin shugaban biyu ta kasance cikin nutsuwa, kuma sun amince da haduwa a wani lokaci mai zuwa.

Majalisar Dinkin Duniya Ta Gargadi Isra’ila Kan Ta Tsayar Da Halaka Mutanen GazaMajalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ta bukaci ...
18/07/2025

Majalisar Dinkin Duniya Ta Gargadi Isra’ila Kan Ta Tsayar Da Halaka Mutanen Gaza

Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ta bukaci Isra’ila da ta gaggauta dakatar da hare-haren da take kai wa Gaza, tana mai bayyana barnar da aka yi a yanzu a matsayin “abin ƙi.

A wani taron manema labarai a yau Juma’a, mai magana da yawun MDD, Farhan Haq, ya ce:

> “Mun yi gargaɗi cewa ba abin yarda ba ne yadda gine-gine ke rushewa, mutane da dama sun rasa matsuguninsu kuma an kore su daga gidajensu — ba sau ɗaya ba, sau da dama cikin shekaru biyu da s**a wuce.”

MDD ta ce ta bi sawun asarar dukiyoyi da rayuka tun daga watan Oktoba 2023 da aka fara rikicin, ta hanyar bayanan tauraron dan adam na UNOSAT.

> “Muna nan muna sake kira ga gwamnatin Isra’ila da ta daina rusa Gaza. Muna kuma sake jaddada buƙatar tsagaita wuta,” in ji Haq.

Tun farkon rikicin, rundunar sojan Isra’ila na ci gaba da hare-haren da s**a yi sanadin mutuwar sama da Palasdinawa 58,600 — yawancinsu mata da yara.

A watan Nuwamba, Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC) ta fitar da sammacin k**a Firayim Ministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu da tsohon Ministan Tsaronsa, Yoav Gallant, bisa zargin aikata laifukan yaki da laifukan cin zarafin ɗan Adam a Gaza.

Isra’ila na fuskantar shari’a a Kotun Ƙoli ta Duniya (ICJ) bisa zargin aikata kisan kare dangi a yakin Gaza.

Kungiyar NMA Gombe Ta Yi Fatali da Sabon Tsarin Alawus na Gwamnatin TarayyaƘungiyar Likitoci ta Najeriya reshen Jihar Go...
18/07/2025

Kungiyar NMA Gombe Ta Yi Fatali da Sabon Tsarin Alawus na Gwamnatin Tarayya

Ƙungiyar Likitoci ta Najeriya reshen Jihar Gombe (NMA-Gombe) ta yi watsi da sabuwar takardar sanarwa daga Hukumar Albashi da Albarkatun Kuɗi ta Ƙasa wadda ta yi nazari kan alawus na likitoci da likitocin haƙori a ma’aikatar Gwamnatin Tarayya.

A cewar ƙungiyar, sabon tsarin “bai da adalci, yana karya gwiwa, kuma ya ci karo da yarjejeniyar da aka cimma a baya.”

An yanke wannan hukunci ne a wani taron gaggawa da ƙungiyar ta gudanar ta yanar gizo a ranar Litinin, 14 ga Yuli, 2025, domin nazarin sak**akon takardar sanarwar ranar 27 ga Yuni mai lamba: SWC/S/04/S.218/111/648.

📌 Ƙungiyar ta ce ba za ta lamunci cigaba da wulakanta ma’aikatan lafiya ba, kuma za ta bi duk wata hanya da ta dace don kare martabar likitoci a jihar da ma ƙasa baki ɗaya.

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗa Muhammad Babangida, ɗan tsohon shugaban mulkin soja Janar Ibrahim Bada...
18/07/2025

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗa Muhammad Babangida, ɗan tsohon shugaban mulkin soja Janar Ibrahim Badamasi Babangida, a matsayin Shugaban Bankin Raya Noma (Bank of Agriculture) da aka sake fasalta.

Wannan naɗi na zuwa ne a wani bangare na ƙoƙarin da gwamnatin Tinubu ke yi na gyara harkokin noma da bunƙasa habakar tattalin arzikin ƙasa ta hanyar bayar da fifiko ga bankunan raya masana'antu.

Address


Telephone

+2347045989882

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Aminchi Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Aminchi Tv:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share