Kanawa Radio

Kanawa Radio News, Media and Broadcasting Station.
(1)

Gwamnan jihar Yobe Mai mala Buni ya sanar da rage farashin hayar tarakta domin samun saukin gudanar da noman banaGwamnat...
03/06/2026

Gwamnan jihar Yobe Mai mala Buni ya sanar da rage farashin hayar tarakta domin samun saukin gudanar da noman bana

Gwamnatin ta bayyana cewar daga yanzu manoma zasu rika biyan Naira dubu hamsin ne a maimakon Naira dubu dari.

buni

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, yace majalisar na kokarin ganin an samar wa wasu sanatocin da s**a ...
03/06/2026

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, yace majalisar na kokarin ganin an samar wa wasu sanatocin da s**a kasa samun tikitin tsayawa takara a zabukan fidda gwani damar komawa takara a shekarar 2027.

Hakan na zuwa ne bayan korafe-korafe sun yawaita a jam'iyyar APC kan faduwa zaben fitar da gwani da kuma zargin magudi a zaben.

Akallah sanatoci 40 daga jam’iyyu daban-daban da s**a hada da APC, PDP da NDC, da sauransu, sun sha kaye a zabukan fitar da gwani.

TSARO/KOGI                      BBC HAUSARundunar sojin kasarnan ta kuɓutar da fasinjoji 23 da wasu da ake zargin ƴanbin...
03/06/2026

TSARO/KOGI BBC HAUSA

Rundunar sojin kasarnan ta kuɓutar da fasinjoji 23 da wasu da ake zargin ƴanbindiga ne s**a sace a kan hanyar Ayegunle zuwa Bunu a ƙaramar hukumar Kabba-Bunu da ke jihar Kogi.

Cikin wata sanarwa a shafin X, rundunar sojin ta ce an kai samamen ne sak**akon kiran gaggawa da s**a samu da sanyin safiya lamarin da ya sa sojoji s**a gaggauta kai ɗauki yankin.

A cewar sanarwar, maharan sun toshe babbar hanyar tare da garkuwa da matafiya da dama kafin jami'an tsaro su isa wajen.
Sojojin sun ce samamen ya sa sun gano motocin bas da motar dakon kaya da aka yasar kan t**i.

Sanarwar ta ƙara da cewa akwai mutum biyu da s**a mutu sai kuma wasu biyar da s**a ji rauni inda aka gaggauta kai su asibitin St Joseph da ke Kabba kuma a nan ake kula da su.

NAHCON/NIGERIA                        SOLACEBASEHukumar Alhazai ta Ƙasa NAHCON ta sanar cewa za a fara jigilar maniyyata...
03/06/2026

NAHCON/NIGERIA SOLACEBASE

Hukumar Alhazai ta Ƙasa NAHCON ta sanar cewa za a fara jigilar maniyyatan kasarnan daga Saudi Arabia zuwa gida Nigeria a gobe Laraba.

Hukumar ta kuma buƙaci maniyyatan da ke shirin dawowa da su bi ka’idojin diban kaya da takardun tafiya domin kauce wa jinkiri yayin komawa gida.

Shugaban Sashen Sufurin Jiragen Sama na Hukumar, Habib Bello, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a birnin Makkah.

Bello ya ce kamfanonin jiragen sama ne ke tsara jadawalin tashi da saukar jirage, yayin da hukumar dake kula da jirage ta kasa ke amincewa da jadawalin tare da ware lokutan aiki ga dukkan kamfanonin da ke gudanar da zirga-zirgar jirage.
A cewarsa, jirgin Max Air zai fara jigilar maniyyata masu dawowa a ranar 3 ga Yuni tare da maniyyatan jihar Nasarawa, yayin da jirgin Flynas da na Air Peace za su fara jigilar maniyyatan daga ranar 4 ga Yuni tare da maniyyatan jihohin Ogun State da Oyo State.

Ya kuma shawarci maniyyatan da su kiyaye ƙa’idar adadin kayan da aka amince da su, wato jakunkuna biyu masu nauyin kilo 23 kowacce, tare da jakar hannu guda ɗaya mai nauyin kilo 8.

Cutar kwalara ta yi ajalin akalla mutane 40 a yayin da wasu sama da mutane dubu uku suke fama da ita a cikin wata guda a...
02/06/2026

Cutar kwalara ta yi ajalin akalla mutane 40 a yayin da wasu sama da mutane dubu uku suke fama da ita a cikin wata guda a wasu kananan hukumomi bakwai a Jihar Borno.

‎Rahotanni sun bayyana cewar al’ummomi 139 ne aka samu bullar cutar a kananan hukumomin Borno, Jere, Mafa, Konduga, Monguno, Ngala da Magumeri.

Gwamnatin Jihar Borno ta sanar cewa cutar kwalara ta kashe mutum 37, a yayin da wasu dubu uku, ke cigaba da fama da ita.

‎Sabbin alkaluman sun nuna an samu karuwar mace-mace 10 da sabbin wadanda s**a kamu da mutum 285 cikin kwana uku kacal.

‎Shugaban marasa rinjaye na majalisar wakilai ta tarayya, Kingsley Chinda, ya yi murabus daga mukaminsa tare da ficewars...
02/06/2026

‎Shugaban marasa rinjaye na majalisar wakilai ta tarayya, Kingsley Chinda, ya yi murabus daga mukaminsa tare da ficewarsa daga jam’iyyar PDP zuwa APC.

Shugaban majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, ne ya sanar da murabus da sauya shekar Chinda a zaman majalisar bayan dawowa daga hutun makonni hudu.

Wasu yan majalisar wakila ta  kasar nan 13 sun sanar da ficewarsu daga jamiyyu daban daban sak**akon rice rikicen cikin ...
02/06/2026

Wasu yan majalisar wakila ta kasar nan 13 sun sanar da ficewarsu daga jamiyyu daban daban sak**akon rice rikicen cikin gida da ya dami jamiyyunsu a zaman majalisar nay au.

Shugaban majalisar wakilan Tajudeen Abbas, ya karanta wasikar ficewar tasu a zaman majalisar domin sanar da duka mambobin majalisar halin da ake ciki na sauya shekar.

Daga cikin wadanda s**a sauya shekar, akwai Alex Ehnona wanda ya sanar da ficewarsa daga jamiyyar APC zuwa PDP, da Esosa Iyawo wanda ya bar jamiyyar APC zuwa jamiyyar NDC.

Haka zalika majalisar ta sanar da ficewar mambobi 6 wadanda s**a bar jamiyyar PDP zuwa jamiyyar APM dfaga jihar Oyo.

‎Hukumar tsaron farin kaya DSS, ta k**a mutane biyar, ciki har da ‘yan ƙasar Nijar biyu, bisa zargin samar da mak**ai ga...
02/06/2026

‎Hukumar tsaron farin kaya DSS, ta k**a mutane biyar, ciki har da ‘yan ƙasar Nijar biyu, bisa zargin samar da mak**ai ga ‘yan bindigar da s**a sace ɗaliban.

‎Ma’aikatan Makarantar Katolika ta St. Mary’s da ke garin Papiri a Jihar Neja.

‎Hukumar ta kuma kwato bindigogi kirar AK-103 guda 15, mujallu 15 da harsasai sama da dubu daya a yayin samamen.

‎Majiyoyin tsaro sun ce an k**a Yusuf Mohammed, wanda aka fi sani da Bature, da Mubarak Ibrahim a kan hanyar Zariya zuwa Kaduna yayin da suke kan hanyarsu ta karɓo mak**ai.

‎Bincike ya kai ga k**a Goni Ibrahim, wani dillalin mak**ai daga yankin Diffa na Jamhuriyar Nijar, da abokinsa Tukur Sani.

‎Daga baya kuma an k**a Alhaji Adamu, wanda aka fi sani da Gado Banufe, a Yauri ta Jihar Kebbi.

‎Jami’an tsaro sun ce bincike ya nuna cewa mutanen biyar ɗin na cikin masu kai wa ‘yan bindigar da s**a kai hari makarantar mak**an da suke amfani da su.

‎Wasu yan' bindiga sun kaiwa tawagar shugaban ma'aikatan fadar gwamnatin jihar Anambra,Chief Ben Nwankwo wanda yayi sana...
02/06/2026

‎Wasu yan' bindiga sun kaiwa tawagar shugaban ma'aikatan fadar gwamnatin jihar Anambra,Chief Ben Nwankwo wanda yayi sanadiyar mutuwar jam'in yan' sanda biyu.

‎Yan bindigar sun kaiwa tawagar harin ne, yayin da suke kan hanyar zuwa Amansea–Awa a karamar hukumar Orumba.

‎Shugaban ma'aikatan fadar gwamnatin Chief Ben Nwankwo, yana wakiltar gwamnan Chukwuma Soludo, a wani taro a Awka.

Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya Babachir Lawal, ya yi hasashen cewa Shugaba Bola Tinubu zai lashe zaɓen shugaban ƙasa...
02/06/2026

Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya Babachir Lawal, ya yi hasashen cewa Shugaba Bola Tinubu zai lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2027 cikin sauƙi.

Lawal ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels, jim kaɗan bayan ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar ADC.

Ya ce ya yanke shawarar barin harkokin siyasa ne saboda rashin gamsuwa da yadda ake tafiyar da siyasa a Najeriya.

A cewarsa, yanzu zai mayar da hankali kan harkokin noma da kuma ayyukan addini.

Lawal, wanda ya yi haɗaka da ‘yan adawa ya amince da ADC a matsayin jam’iyyarsa, ya ce Tinubu zai yi wahalar kayarwa a zaɓe mai zuwa.

Ya kuma yi iƙirarin cewa idan maganar yin maguɗi ne ke ƙayyade nasara a zaɓe, babu wani ɗan siyasa da zai iya yin takara da Tinubu.

Haka kuma ya ce tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar zai yi wahala ya yi takara da Tinubu a zaɓen 2027.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kanawa Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category