02/06/2026
Hukumar tsaron farin kaya DSS, ta k**a mutane biyar, ciki har da ‘yan ƙasar Nijar biyu, bisa zargin samar da mak**ai ga ‘yan bindigar da s**a sace ɗaliban.
Ma’aikatan Makarantar Katolika ta St. Mary’s da ke garin Papiri a Jihar Neja.
Hukumar ta kuma kwato bindigogi kirar AK-103 guda 15, mujallu 15 da harsasai sama da dubu daya a yayin samamen.
Majiyoyin tsaro sun ce an k**a Yusuf Mohammed, wanda aka fi sani da Bature, da Mubarak Ibrahim a kan hanyar Zariya zuwa Kaduna yayin da suke kan hanyarsu ta karɓo mak**ai.
Bincike ya kai ga k**a Goni Ibrahim, wani dillalin mak**ai daga yankin Diffa na Jamhuriyar Nijar, da abokinsa Tukur Sani.
Daga baya kuma an k**a Alhaji Adamu, wanda aka fi sani da Gado Banufe, a Yauri ta Jihar Kebbi.
Jami’an tsaro sun ce bincike ya nuna cewa mutanen biyar ɗin na cikin masu kai wa ‘yan bindigar da s**a kai hari makarantar mak**an da suke amfani da su.