Kanawa Radio

Kanawa Radio News, Media and Broadcasting Station.

Biyo bayan korafi da mazauna unguwar Dukawuya s**a gabatarwa da Ma'aikatar Kasa da tsara birane, Gwamnatin jihar Kano ta...
04/08/2026

Biyo bayan korafi da mazauna unguwar Dukawuya s**a gabatarwa da Ma'aikatar Kasa da tsara birane, Gwamnatin jihar Kano ta rushe wani gini da aka yi ba bisa ka'ida ba akan hanyar ruwa a unguwar.

Gwamnatin Tarayya ta buɗe ƙofa ga 'yan Najeriya domin su gabatar da shawarwari da bayanai kan sabon Kudirin Dokar Tsaron...
04/08/2026

Gwamnatin Tarayya ta buɗe ƙofa ga 'yan Najeriya domin su gabatar da shawarwari da bayanai kan sabon Kudirin Dokar Tsaron Ƙasa, a wani mataki na samar da cikakken tsarin doka na kafa rundunar 'yan sandan jihohi.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Aiki na Shugaban Ƙasa kan Sauye-sauyen Tsaro, Femi Gbajabiamila, ya fitar bayan taron kwamitin da aka gudanar a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

Gbajabiamila ya bayyana cewa manufar shirin ita ce samar da tsarin aikin 'yan sanda na zamani wanda zai daidaita nauyin da ke tsakanin Gwamnatin Tarayya da gwamnatocin jihohi.

Ya ce kwamitin na duba Dokar 'Yan Sanda ta shekarar 2020, tsarin Hukumar Kula da Ayyukan 'Yan Sanda da sauran dokokin da s**a shafi tsaro domin samar da cikakken tsarin aikin 'yan sanda.

04/08/2026

Labaran Kanawa

‎Tsohon kocin ƙungiyar kwallon kafa ta kasa Super Eagle, Johannes Bonfrère  Jo, ya bayyana takaicinsa kan yadda har yanz...
04/08/2026

‎Tsohon kocin ƙungiyar kwallon kafa ta kasa Super Eagle, Johannes Bonfrère Jo, ya bayyana takaicinsa kan yadda har yanzu gwamnatin Najeriya ba ta karrama shi ko ba shi lada ba.

‎Duk da cika shekaru 30 da jagorantar ƙasar zuwa lashe lambar zinare ta farko kuma tilo a gasar ƙwallon ƙafa ta wasannin Olympics.

‎Bonfrère ya jagoranci wata ƙwararriyar tawaga da ta ƙunshi fitattun 'yan wasa irin su Kanu, Austin Okocha, Daniel Amokachi, Taribo West, Celestine Babayaro, Garba Lawal da Emmanuel Amuneke zuwa rubuta tarihin da ba za a manta da shi ba a gasar Olympics.

‎Super Eagle ta doke Brazil da ci 4-3 bayan ƙarin lokaci a wasan kusa da na ƙarshe, kafin daga bisani ta yi nasarar doke Argentina da ci 3-2 a wasan ƙarshe.

‎Yayin da ta zama ƙasa ta farko a Afirka da ta lashe zinari a gasar ƙwallon ƙafa ta Olympics.

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta amince da ƙudirin dokar gyaran Hukumar Kula da Makarantu Masu Zaman Kansu da na Ƙungiyoy...
04/08/2026

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta amince da ƙudirin dokar gyaran Hukumar Kula da Makarantu Masu Zaman Kansu da na Ƙungiyoyi ta Jihar Kano na shekarar 2026 wanda ya tanadi sabbin sauye-sauye domin ƙarfafa tsarin sa ido da gudanar da harkokin makarantu masu zaman kansu da na ƙungiyoyi a faɗin jihar.

An amince da kudirin ne a zaman majalisar bayan da Kwamitin Ilimi na Majalisar ya gabatar da rahotonsa, wanda aka tsara bayan gudanar da sauraron ra’ayoyin jama’a da kuma tattaunawa da masu ruwa da tsaki.

Da yake jawabi bayan amincewa da kudirin, Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano ya yaba wa ‘yan majalisar bisa gudunmawar da s**a bayar wajen tantance kudirin.

Ya ce gyaran dokar zai taimaka wajen inganta yadda ake gudanar da hukumar tare da kare muradun iyaye da ɗalibai.

Har ila yau, sabuwar dokar ta tanadi cewa duk wata makaranta mai zaman kanta ko ta ƙungiya ba za ta ƙara kuɗin makaranta ko wasu kuɗaɗen karatu ba sai ta fara samun amincewar hukumomin da abin ya shafa.

Mazauna garin Mubi sun nemi ayi adalci bayan zargin soja da harbe dan kasuwa a jihar Adamawa.Mazauna garin Mubi da ke Ji...
04/08/2026

Mazauna garin Mubi sun nemi ayi adalci bayan zargin soja da harbe dan kasuwa a jihar Adamawa.

Mazauna garin Mubi da ke Jihar Adamawa sun nuna matuƙar damuwa tare da neman a yi adalci, bayan zargin wani soja da harbe wani ɗan kasuwa mai suna Suleiman Abu a yankin Ƙaramar Hukumar Mubi ta Arewa.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 8:40 na daren Lahadi, lokacin da marigayin ke tuka babur mai amfani da wutar lantarki, inda ya hango wasu sojoji suna sintiri.

Majiyoyi sun ce, saboda fargabar k**a shi sak**akon dokar hana zirga-zirgar babura daga ƙarfe 9:00 na dare zuwa 6:00 na safe, ya juya ya nufi gidansa kafin lokacin dokar ya fara aiki.

Shaidu sun yi zargin cewa bayan da Suleiman Abu ya isa gidansa, ya ajiye baburinsa kuma yana ƙoƙarin rufe ƙofar gidan, wani soja da ake zargin ya bi sawunsa ya buɗe masa wuta.

Ƙoƙarin jin ta bakin Kwamandan Sashe na 4 na Operation Hadin Kai, Birgediya Janar Amechi Agwu, bai yi nasara ba, domin an ce yana halartar wani taro a lokacin da aka nemi jin

‎‎Majalisar dokin jihar Kano ta dakatar da shugabannin kananan hukumomi 3 da s**a hada Shugaban karamar hukumar Rogo da ...
04/08/2026


‎Majalisar dokin jihar Kano ta dakatar da shugabannin kananan hukumomi 3 da s**a hada Shugaban karamar hukumar Rogo da na Bagwai da Bebeji a yau.

‎Majalisar ta dakatar da su ne bisa tuhumar su kan laifuka da s**a shafi ofisoshin kan gudanarwar ba bisa ka'ida ba.

‎Shugabannin ƙananan hukumomin da abin ya shafa sun haɗa da Alhaji Bello Abdullahi Gadanya na Bagwai, Dr. Alhassan Salisu na Bebeji da Alhaji Abubakar Mustapha Rogo na Rogo.

‎Majalisar ta dakatar da su na tsahon watanni uku domin bawa kwamatin dake kula da kananan hukumomin da harkokin masarautu damar gudanar da cikakken bincike.

04/08/2026
Iyalan Alkalin babbar kotun a jihar Kebbi  Justice Faruk Hassan Bunza, wanda akayi garkuwa dashi sun bayyana cewar sai d...
04/08/2026

Iyalan Alkalin babbar kotun a jihar Kebbi Justice Faruk Hassan Bunza, wanda akayi garkuwa dashi sun bayyana cewar sai da s**a biya kudin fansa naira miliyan 50 kafin sakin sa.

‎Mai shari'a Bunza anyi garkuwa dashi a ranar Lahadi 26, ga watan yuli a karamar hukumar Bunza ta jihar Kebbi.

‎Alkali Bunza ya samu yanci ne, bayan shafe kwanaki takwas a hannun yan' bindigar ..

Wata tawaga daga Gwamnatin Jihar Kano ta kai ziyarar ta’aziyya zuwa Jihar Sokoto bisa rasuwar Sardaunan Sokoto, Alhaji A...
04/08/2026

Wata tawaga daga Gwamnatin Jihar Kano ta kai ziyarar ta’aziyya zuwa Jihar Sokoto bisa rasuwar Sardaunan Sokoto, Alhaji Abubakar Alhaji, a madadin Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf.

Tawagar, wadda Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Alh. Murtala Sule Garo, ya jagoranta, ta kunshi Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Umar Farouk Ibrahim, Sarkin Rano, Mai Martaba Muhammad Isa Umar; Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar, Hon. Umar Haruna Doguwa; da Kwamishinar Al’adu da Yawon Buɗe Ido, Hajiya Aisha Lawan Saji, tare da wasu manyan jami’an gwamnatin jihar.

Tawagar ta kai ziyara gidan marigayi Sardaunan Sokoto, inda ta isar da sakon ta’aziyyar Gwamna Yusuf ga iyalan marigayin.

Haka kuma, tawagar ta ziyarci Fadar Mai Alfarma Sarkin Musulmi, domin isar da sakon ta’aziyyar Gwamna Yusuf ga Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar III inda s**ayi addu'ar Allah ya jikan sa da rahama.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kanawa Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category