Kasar Kano Jiya Da Yau

Kasar Kano Jiya Da Yau KASAR KANO JIYA DA YAU: Sanin Tarihinmu da Magabatanmu

Labaran Yammacin Lahadi 16/02/1447AH - 10/08/2025CE Ga Takaitattun Labaran.Hukumar NDLEA ta k**a Fasto da take nema ruwa...
10/08/2025

Labaran Yammacin Lahadi 16/02/1447AH - 10/08/2025CE Ga Takaitattun Labaran.

Hukumar NDLEA ta k**a Fasto da take nema ruwa a jallo kan safarar miyagun kwayoyi a Legas.

Gwamna Abba na jihar Kano ya bai wa dalibai 1,130 kayan aikin sana’o’in hannu.

Hukumar NDLEA ta cafke masu baburan da ke kai saƙon muggan kwayoyi a Abuja.

Kungiyar kare hakkin jama’a da tattalin arzikin kasa da kuma kungiyar Editocin Najeriya (NGE) sun maka Gwamnan Jihar Neja Umar Bago da Hukumar Yada Labarai ta Kasa a kotu kan rufe gidan rediyon Badeggi FM.

Wasu mahara sun hallaka mutum 2 tare da ƙona gidaje da kuma coci-coci a karamar hukumar Bokkos na jihar Filato.

Jami’an Hukumar EFCC, sun kai samame a dakin Karatun Obasanjo da ke Abeokuta, a Jihar Ogun, inda s**a k**a wasu matasa da ake zargin ’yan damfara ne.

Gwamnonin arewa na alhinin mutuwar tsohon ministan noma Cif Audu Ogbeh.

Gwamnan Kano ya karɓi daruruwan ƴan APC da s**a sauya sheka zuwa NNPP.

Kamfanin Oxfam ya fitar da rahotan cewa ƴan Najeriya miliyan 83 ke cikin talauci yayin da kaso 10 cikin 100 ne kacal ke facaka da arziƙin ƙasar.

Ƴan bindiga sun kashe ƴan sanda da jami'an sa kai 13 a jihar Zamfara.

Jihar Kogi ta kafa kotuna 9 don hukunta masu cin zarafin Mata.

An sake shiga tashin hankali a Jihar Sakkwato bayan wani sabon mummunan hari da ƴan bindiga s**a kai a wasu kauyuka, lamarin da ke ƙara tsananta matsalar tsaro a faɗin jihar.

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa Isra'ila ba ta "zaɓi" illa "karasa aikin" da ta fara wajen ƙarya lagon Hamas.

Kotu ta ɗaure tsohon Firaministan Chadi shekara 20 a gidan yari.

Ana zanga-zanga a Isra’ila kan shirin Netanyahu na mamaye Gaza.

Birtaniya za ta fara tisa ƙeyar bakin da s**a aikata laifi zuwa gida.

Ƙawayen Ukraine sun ce dole ne a sa ƙasar a tattaunawar zaman lafiya.

Barau FC dake Kano ta ɗauki 'yanwasa 10 kafin fara firimiyar Najeriya ta bana.

Mohamed Salah ya soki hukumar kwallon kafa ta Turai, UEFA, kan wallafa sakon alhinin mutuwar ɗan wasan Falasɗinawa ba tare da cikakken bayani kan abin da ya yi sanadin rasuwarsa ba.

Community Shield: Crystal Palace tayi nasara akan Liverpool daci 3 : 2 a bugun Fanareti bayan tashi 2 : 2 a wasan share fagen kakar 2025/2026 wadda za a fara Juma a mai zuwa.

Newcastle United na gab da kammala ɗaukar ɗanwasan baya Malick Thiaw daga AC Milan.

Sunderland ta ɗauki ɗanwasa na 10 kafin fara kakar wasa ta bana.

Tafiyar Martinez za ta taimaka wajen rage nauyin biyan albashin ’yan wasa a Barcelona, ƙungiyar da a bayan nan ke fama da matsalar rashin kuɗi.

Labaran Safiyar Alhamis 13/02/1447AH - 07/08/2025CE Ga Takaitattun Labaran.Shugaba Tinubu ya jajanta wa al'ummar Ghana k...
07/08/2025

Labaran Safiyar Alhamis 13/02/1447AH - 07/08/2025CE Ga Takaitattun Labaran.

Shugaba Tinubu ya jajanta wa al'ummar Ghana kan mutuwar ministoci.

Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin samar da tsarin kula da lafiya kyauta ga masu ƙaramin ƙarfi da s**a yi ritaya a ƙarƙashin shirin fansho na karo-karo.

Shugaba Tinubu ya taya Nafisa, Rukayya, Hadiza murnar samun nasarar zama gwanaye a gasar turanci ta Duniya.

Shugaban EFCC, Olukoyede ya ce galibin rukunin gidajen da aka fara amma aka yi watsi da su a Abuja na ma’aikatan gwamnati ne da s**a mallaka da kudaden sata.

Gwamnatin Kano ta ce za ta bai wa iyalan ƴan wasan nan 22 kuɗaɗe da filaye a matsayin gudummawa bayan rasuwarsu a kan hanyar komawa gida daga jihar Ogun.

Wani soja wanda ba a daɗe da yaye su ba, Dauda Dedan, ya yi layar zana bayan zargin sa da kashe wani ɗansanda, Aaron John, ta hanyar caka masa wuƙa a Jalingon jihar Taraba.

Sojoji sun K**a mai yi wa Boko Haram safarar Man Fetur a jihar Borno.

Mataimakin Gwamnan Jihar Taraba, Alhaji Aminu Alkali, ya yi ɓatan dabo inda ya shafe tsawon watanni takwas ba tare da an gan shi ba.

Rundunar ƴan sandan Kano ta shawarci al'umma su kai mata rahoton duk wani ɗan sanda da suke zargin yana karɓar cin hanci don haɗa baki ko rufa asirin wasu ɓata-gari ko masu aikata laifi a yankunansu.

Hukumar Kwastam ta k**a Tankar mai dauke da buhunan shinkafa a Kaduna.

Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi II ya zargi ƴan siyasar Najeriya da aikata cin hanci da rashawa sabida "rashin tarbiyya tun daga tasowarsu".

Mahukuntan Abuja sun fatattaki mabarata 273, sun k**a ababen hawa 670 a cikin watanni hudu

Jami'an 'yan sanda, sun k**a fitattacen dan fafutuka, kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Omoyele Sowore.

Hukumar WAEC ta rufe shafin duba jarabawar WASSCE 2025.

Faransa na fama da bala'in gobarar daji 'mafi muni a tarihi'.

Ƙasar Italiya za ta gina gada mafi tsawo a duniya.

Manchester United ta tuntuɓi Brighton kan ɗanwasan ta Carlos Baleba.

Rasha ta ce ana samun ci gaba a tattaunawar tsagaita wuta a yaƙin Ukraine.

Ɗan wasa Alexander Isak an faɗa masa ya yi atisaye shi kaɗai a Newcastle United saboda farautarsa da Liverpool ke ci gaba da yi.

Inter Milan na duba yiyuwar ɗauko ɗan wasan Manchester United Sancho, idan ta kasa samun ɗan wasa Ademola Lookman, daga Atalanta.

Labaran Safiyar Talata 10/02/1447AH - 05/08/2025CE Ga Takaitattun Labaran.Mataimakin Gwamnan Zamfara yace ruwan wuta ne ...
05/08/2025

Labaran Safiyar Talata 10/02/1447AH - 05/08/2025CE Ga Takaitattun Labaran.

Mataimakin Gwamnan Zamfara yace ruwan wuta ne kawai maganin ‘Yan Ta’adda ba sasanci ba.

’Yar shekara 17 daga Jihar Yobe, Nasifa Abdullah ta lashe Gasar Harshen Turanci ta duniya inda ta doke mutum 20,000 da s**a fafata a gasar da aka gudanar a birnin Landan na ƙasar Birtaniya.

Jam'iyyar ADC tace kashe N712bn kan gyaran filin jiragen saman Legas rashin sanin ya k**ata ne.

Ƴan sanda sun k**a ƴan Jamhuriyar Benin kan zargin safarar mutane.

Sanatan Bauchi ta Kudu, Shehu Buba Umar ya ƙaddamar rabon takin zamani da kuma allurar rigakafin dabbobi kyauta ga al'ummar mazaɓarsa.

Pantami ya ce ya k**ata Tinubu ya ba wa ɗalibar nan ’yar shekara 17 daga Jihar Yobe da ta lashe Gasar Turanci ta Duniya, Nafisa Abdullah Aminu, kyautar $100,000 da gida da kuma lambar OON, k**ar yadda aka ba wa ’yan kwallon da s**a lashe Gasar Afirka.

Hukumar wayar da kan ƴan ƙasa tace Gwamnatin tarayya ta kwato ₦21bn, ta kashe yan ta’adda 78

Kamfanin BUA Siminti ya kaddamar da shirin horas da matasan Sakkwato.

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa.

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana.

An yi garkuwa da mutum 9 a gidan marayu a Haiti.

Trump ya yi barazanar ƙara wa Indiya haraji saboda hulɗa da Rasha.

Ukraine ta ce jiragenta sun kai hari sansanin sojin Rasha a Crimea.

Tsofaffin jami'an tsaro sun buƙaci Trump ya kawo ƙarshen yaƙin Gaza.

Iyalan waɗanda Hamas ke garkuwa da su sun zargi Netanyahu da jefa Isra'ila cikin bala'i.

RSF ta miƙa sansanin gudun hijirar Zamzam ga sojojin hayar Columbia.

Gwamnatin Ghana ta ƙara farashin Koko da take saya daga hannun manoma.

Newcastle da Manchester United na hamayya kan Benjamin Sesko, mai shekara 22.

Kocin Everton David Moyes na son ƙara shiga kasuwa domin ƙara cefanen ƴanwasa shida da s**a ƙunshi ƴanwasan tsakiya guda biyu.

Rodrygo, na son ci gaba da taka leda a Real Madrid duk da ribibinsa da Tottenham da Arsenal da Liverpool ke yi.

Labaran Safiyar Litinin 09/02/1447AH - 04/08/2025CE Ga Takaitattun Labaran.Rikici ya Ɓarke a zaɓen Ribas, ƴan PDP sun fi...
04/08/2025

Labaran Safiyar Litinin 09/02/1447AH - 04/08/2025CE Ga Takaitattun Labaran.

Rikici ya Ɓarke a zaɓen Ribas, ƴan PDP sun fito a matsayin yan takarar APC.

ADC ta yi Allah-wadai fa rufe gidan Rediyon Badeggi FM a Neja.

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare.

Serap ta ba wa gwamnan Neja wa'adin janye umarnin rufe rediyon Badeggi FM.

Mai Martaba Sarkin Gombe, Alhaji Dakta Abubakar Shehu Abubakar III, ya naɗa Dakta Ibrahim Jalo Daudu sarautar Tafarkin Gombe.

Dangote ya dauki nauyin bikin baje kolin gidajen Afrika da mahalarta Ƙasashe 21.

A cikin Babban Barikin Sojoji na Jaji da ke Jihar Kaduna aka k**a dillalan miyagun ƙwayoyi 28, cikinsu har da mata 11.

Saudiya ta kashe mutane 8 da aka samu da laifin safarar miyagun ƙwayoyi.

Ƙasashen Larabawa sun yi tir da ziyarar ministan Isra'ila a Masallacin Ƙudus.

Ana Gaggauta ayyukan gyara tituna da gadojin da ambaliya ta lalata a Arewacin Kasar Sin.

Iran da Pakistan za su ƙarfafa alaƙar kasuwanci da dala biliyan 10.

Shugabar Tanzania ya kaddamar fa cibiyar cinikayya da Jigila da Sin ta hina a Kasar.

Tottenham na son sayen Rodrygo, domin maye gurbin ɗan wasanta, Son Heung-min.

Manchester United ta bi sahun Newcastle a neman daidaitawa da ɗan wasan RB Leipzig, Benjamin Sesko.

Mai tsaron ragar PSG, Donnarumma, na son tafiya Manchester United.

Labaran Yammacin Lahadi 08/02/1447AH - 03/08/2025CE Ga Takaitattun Labaran.Rundunar Soji tare da haɗin gwiwar jami’an DS...
03/08/2025

Labaran Yammacin Lahadi 08/02/1447AH - 03/08/2025CE Ga Takaitattun Labaran.

Rundunar Soji tare da haɗin gwiwar jami’an DSS sun ceto Injiniya Joshua Saleh, wani malami a Jami’ar Taraba, wanda ’yan bindiga s**a sace.

Peter Obi ya ce idan ya samu nasarar zama shugaban ƙasar wa'adi ɗaya na shekara huɗu kawai zai yi k**ar yadda ya yi alƙawari.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ƙaddamar da babban shirin dashen bishiyoyi miliyan biyar a shekarar 2025.

Gini mai hawa uku ya rufta kan mutum biyu a Abuja.

Wani masanin tsaro Sani Shinkafi yace gwamnatin tarayya ce ta kawo cikas wajen kashe Bello Turji a lokacin da aka yi masa ƙawanya a jihar Zamfara.

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya ce idan Shugaba Tinubu ya sake lashe zaɓe a 2027, hakan zai lalata makomar ’yan Najeriya.

Gwamnan Zulum na jihar Borno ya ce gwamnatinsa ta fara yunƙurin gyara tsarin Maiduguri domin kiyaye jihar daga ambaliya.

Ƴan bindiga sun sace mutane fiye da 50 a harin da s**a kai a karamar hukumar Bakura dake jihar Zamfara.

Gwamnan Yobe, Mai Mala Buni, ya amince da naɗa Ismaila Ahmed Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi, bayan rasuwar Alhaji Isa Bunuwa Madugu Ibn Kaji.

IPI ta yi kira da a buɗe rediyon Badegi, ta yi barazanar sanya sunan gwamna Bago a jerin mutanen da ke Tauye Ƴancin Jarida

Wani dutse a gabashin Rasha ya k**a da wuta karon farko cikin sama da shekara 500.

Ana binciken jami'in da ya shigar da Trump ƙara kafin zaɓe.

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinawa a Birnin Sydney dake Australia.

Rasha ta zargi Ukraine da kai hari a cibiyar dakon fetur a ƙasarta.

Yau Jamhuriyyar Nijar ke gudanar da bikin zagayowar ranar samun ƴanci.

Ɗan wasan Najeriya, Ademola Lookman ya ce ya mika batun neman izinin barin Atalanta, bayan da ya zargi ƙungiyar da saɓa alkawari.

Labaran Safiyar Lahadi 08/02/1447AH - 03/08/2025CE Ga Takaitattun Labaran.Gwamnatin ta aika tawaga ƙasar Ghana don yayya...
03/08/2025

Labaran Safiyar Lahadi 08/02/1447AH -
03/08/2025CE Ga Takaitattun Labaran.

Gwamnatin ta aika tawaga ƙasar Ghana don yayyafa wa wutar zanga-zangar ƙin jinin 'yan Najeriya ruwa.

Gwamnatin Tarayya za ta aiwatar da shirin daƙile sulalewar kuɗaɗen haraji.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Najeriya (NEMA) ta ce aƙalla mutane 165 ne s**a rasu, sannan 82 s**a ɓace sak**akon ambaliya a bana.

KIRA GA TINUBU: Samar da kotun shari'ar Muslunci a jihohi 36 ne adalci inji kungiyar MURIC.

Ma'aikatan jinya sun janye yajin aiki bayan cimma matsaya da gwamnati.

Salihu Tanko Yakasai ya soki Shugaba Tinubu kan yadda yake fifita jihar Legas fiye da sauran jihohin Najeriya.

Ana zargin Kwamishinan Sufuri na Kano, Ibrahim Namadi, da karɓar kuɗin toshiyar baki har Dala 30,000 daga wani ƙasurgumin dilan ƙwaya, Sulaiman Danwawu domin yin belinsa a kotu k**ar yadda rahoton da Hukumar Tsaro ta Ƙasa (SSS), ta fitar.

Gwamnatin tarayya za ta kashe Naira biliyan 68.7 wajen samar wa jami'o'i wutar lantarki.

Bayan ƙaddamar da filin jirgin saman Nasarawa na naira biliyan 15 da Buhari ya yi, shima ya shiga cikin jerin ayyukan baban giwa.

Gwamnatin tarayya za ta kashe Naira biliyan 987 wajen gyaran filayen jirgin saman Najeriya.

'Yansiyasar Rasha sun yi watsi da barazanar Trump ta tura mak**an nukiliya kusa da ƙasar.

Kotu ta yi wa fitaccen ɗansiyasar Indiya ɗaurin rai da rai kan laifin fyaɗe.

Newcastle United ta gabatar da tayin fam miliyan 65.3 kan Benjamin Sesko.

Liverpool za ta sake gabatar da tayi kan Isak ma, idan Newcastle ta samu mai maye gurbinsa.

Ɗan wasan Son-Heung Min ya amince ya koma LAFC bayan yanke hukuncin barin Tottenham.

An kammala duba lafiyar Jorrel Hato a Chelsea kan cimma yarjejeniyar fam miliyan 35.5 a kansa.

01/08/2025

Assalamu alaikum!
Barkamu da safiya dafatan mun tashi lafiya.
Daga wani gari kuke bibiyarmu?
Me kuka wayi gari dashi a yankunanku?
Ƙasar Kani Jiya da yau TV/Radio

Labaran Yammacin Alhamis 06/02/1447AH - 31/07/2025CE Ga Takaitattun Labaran.Shugaba Bola Tinubu ya ƙara wa Bashir Adeniy...
31/07/2025

Labaran Yammacin Alhamis 06/02/1447AH - 31/07/2025CE Ga Takaitattun Labaran.

Shugaba Bola Tinubu ya ƙara wa Bashir Adeniyi, Shugaban Hukumar Kwastam ta Ƙasa, karin shekara ɗaya a kan wa'adin da ya k**ata ya yi na shugabancin hukumar.

Aƙalla mutum tara ne s**a rasu, yayin da wani kwale-kwale ɗauke da fasinjoji 17 ya kife a Jihar Jigawa.

Ɗaya daga cikin jigo a PDP, Farfesa Jerry Gana ya yi iƙirarin cewa Peter Obi zai kayar da duk wani ɗan takara a jihohin Arewacin Najeriya idan ya tsaya takara a PDP.

Gwamnatin taraya ta ce za ta fara yi wa ɗaliban jami'o'in ƙasar gwajin shan ƙwayoyi a wani mataki da daƙile yaɗuwar ta'ammalai da ƙwayoyin.

'Yan majalisar Katsina sun gabatar da kuɗirin gaggawa kan matsalar tsaro a jihar.

Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) ya sanar da sake haka sabbin rijiyoyin man fetur guda hudu yankin Kolmani na jihar Bauchi, k**ar yadda Darakta a kamfanin, Yusuf Usman ya tabbatar.

Dino Melaye ya koma jam'iyyar ADC bayan ficewarsa daga PDP.

Hukumar NEMA ta ce mamakon ruwan sama da yin gine gine kan magunan ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri.

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya reshen Jihar Benuwe, a ranar Alhamis, ta bayyana cewa aƙalla shanu 340 na mambobinta ne aka sace a cikin watan Yuli.

Aƙalla mutum 13 sun mutu a Ukraine bayan luguden wuta da Rasha ta yi a Kyiv.

Gwamnatin sojin Myanmar ta kawo ƙarshen dokar ta-ɓaci da ta sanya bayan kifar da gwamnatin San Suu Kyi.

Iran ta ce ba za ta sake komawa teburin sulhu da Amurka kan shirin nukiliyarta ba, har sai Amurkan ta yarda za ta biya ta diyya kan ɓarnar da aka yi mata a yaƙin watan da ya gabata.

Fiye da mutum 30 sun mutu a gidan gajiyayyun China saboda ambaliya.

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas.

Tanzania ta haramta wa baƙi gudanar da kasuwanci a faɗin ƙasar.

Labaran Safiyar Alhamis 06/02/1447AH - 31/07/2025CE Ga Takaitattun Labaran.Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya karɓi baƙuncin ɗ...
31/07/2025

Labaran Safiyar Alhamis 06/02/1447AH - 31/07/2025CE Ga Takaitattun Labaran.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya karɓi baƙuncin ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Kiru da Bebeji na Jihar Kano, Abdulmumin Jibrin Kofa.

Kwana ɗaya da miƙa tallafin, bilyan 1 daga matar shugaba Tinubu ƴan gudun hijirar sun fantsama tituna suna zanga-zangar yunwa, amma hukumar bayar da agaji ta jihar ta ce kuɗin ba na sayen abinci a raba musu ba ne.

Gwamnatin Tarayya ta sanar da cewa za ta kammala aikin shimfiɗa layin dogo wanda ya taso daga Kaduna zuwa Kano a cikin shekarar 2026 mai zuwa.

Sama da mutum 5,000 ne s**a tsere daga gidajensu a Jihar Katsina, sak**akon sabbin hare-haren da ’yan bindiga s**a kai a Ƙananan Hukumomin Bakori da Faskari.

Sojoji sun ce sun kashe 'yan Boko Haram tara a jihar Borno.

Bayo Onanuga, Mai Bai Wa Shugaba Bola Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai, ya ce wasu ’yan siyasa na s**ar Tinubu ne kawai saboda ya fito daga Kudancin Najeriya.

Ƙasashen Larabawa sun nemi Hamas ta zubar da mak**anta.

AU ta watsi da gwamnatin da RSF ta kafa a Sudan.

Trump ya ƙaƙaba wa Brazil harajin kashi 50.

Wasu ƙasashen da ke yankin arewacin Pacific sun janye gargaɗin da s**a aika bayan aukuwar mummunar girgizar ƙasa a gabashin Rasha.

Manchester United ta soma tattaunawa da PSG kan golan su Donnarumma, amma Chelsea da Manchester City na cikin masu sha'awar golan.

Chelsea na ci gaba da matsi kan Garnacho amma Manchester United na son a biya ta fam miliyan 40 kan ɗan wasan.

Labaran Yammacin Laraba  05/02/1447AH - 30/07/2025CE Ga Takaitattun Labaran.Shugaba Tinubu ya amince da naɗin Olumode Sa...
30/07/2025

Labaran Yammacin Laraba 05/02/1447AH - 30/07/2025CE Ga Takaitattun Labaran.

Shugaba Tinubu ya amince da naɗin Olumode Samuel Adeyemi a matsayin sabon Shugaban Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa.

Gwamnatin taraya ta ce za a kammala aikin titin jirgin ƙasa daga Kaduna zuwa Kano a shekarar 2026, k**ar yadda Ministan Sufuri Sa'idu Ahmed Alkali ya bayyana.

Ruwan sama mai ƙarfi da ya sauka da safiyar ranar Laraba a Maiduguri, Babban Birnin Jihar Borno, ya haddasa ambaliya.

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta jihar Bauchi (BASIEC), Ahmed Mak**a Hardawa, ya rasu.

Gwamnatin taraya tace ta samu kuɗin gudanar da aikin gina layin dogo daga Maiduguri zuwa garin Aba na jihar Abiya.

Gwamnatin Tarayya ta fara daukar ma’aikata a mataki na biyu na shirin Renewed Hope ta karƙashin hukumar NDE

Gwamnatin tarayya ta kaddamar da shirin YouthCred don tallafawa matasa 400,000 da rancen Kudi

Hare-haren ta'addanci sun ragu matuka a karkashin mulkin Tinubu - In Ji Wazirin Katsina, Idah.

Sanatocin arewacin Najeriya sun yi allah wadai da kisan mutane a Zamfara.

Taron Jiga-Jigan Arewa da jami’an gwamnatin Tinubu ya soma da yin kira ga Tinubu da ya daina shigo da abinci daga waje.

Mazauna gidan haya a Kaduna sun koka kan lafta musu ƙarin kuɗin haya a dare ɗaya, sun roki Uba Sani ya sa baki.

Gwamnatin Jigawa ta haramta wa ɗaliban sakandare yin al'adar 'sign out'.

Yara 13 sun mutu a Sudan saboda rashin abinci.

Amurka za ta haramta wa masu zuwa ƙasar haihuwa don samar wa jariransu katin ɗan ƙasa daga Najeriya.

Sojojin Sudan ta Kudu da Uganda sun kashe juna a kan iyaka.

Trump zai sanya harajin kashi 25 kan kayayyaki daga Indiya.

An ji amon harbe-harbe a babban birnin Angola, yayin da aka shiga rana ta 3 da farfasa shaguna da sace kayayyaki da ake yi, bayan kashe mutum 4 da k**a mutane masu yawa lokacin da hatsaniya ta kaure sak**akon ƙarin farashin fetur da ya hadddasa yajin aiki.

Labaran Laraba 05/02/1446AH - 30/07/2025CE Ga Takaitattun Labaran.Mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan Harkokin tsaro Rib...
30/07/2025

Labaran Laraba 05/02/1446AH - 30/07/2025CE Ga Takaitattun Labaran.

Mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan Harkokin tsaro Ribado yace an samu raguwar hare-haren Boko Haram da na ƴan bindiga.

Duk da yadda mukarraban gwamatin Tinubu s**a yi bajekolin ayyukan da s**a ce yana yi a Arewa, Kungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF), ta yi korafin cewa gwamnatin ta mayar da yankin saniyar ware.

Remi Tinubu ta bai wa iyalan da rikicin Benue ya ɗaiɗaita tallafin biliyan ɗaya.

Gwamnan Gombe ya ce arewa za ta mara wa Tinubu baya a zaɓen 2027.

Gwamnatin Kaduna ta raba gidaje ga waɗanda matsalar tsaro ta jefa cikin ƙunci.

Gwamna Mutfwang na Filato yace babu wata Karamar Hukumar da ke karƙashin ikon ƴan ta’adda a jihar.

Gwamnan Darfur ya soki sojoji kan rashin kawo karshen ƙawanyar da aka yi wa yankin.

An kashe mutum huɗu tare da k**a ɗaruruwan masu zanga-zanga a Angola.

Birtaniya ta sanar da shirin amincewa da Falasɗinu a matsayin halastacciyar ƙasa.

Golan Newcastle Nick Pope zai iya komawa Man. United idan Newcastle ta yi nasarar ɗauko golan Southampton, Aaron Ramsdale.

Arsenal na ci gaba da zawarcin Eberechi Eze, amma ba ta shirya biyan £60m kan ɗanwasan ba domin haka tana jira har sai Crystal Palace ta karya farashinsa.

29/07/2025

Labaran Yammacin Talata 04/02/1447AH - 29/07/2025CE Ga Takaitattun Labaran.

Uwargidan Shugaba Tinubu ta bayar da tallafin naira biliyan daya ga wadanda harin nan ya rutsa da su a yankin Yelwata na Ƙaramar Hukumar Guma a Jihar Benuwe.

Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello a matsayin sabon Sarkin Katsinan Gusau.

Wani mutum ya rasu yayin da yake ƙoƙarin raba wani mutum da matarsa da fada a yankin Babban Birnin Tarayya.

Kungiyar malaman jami'ar jihar Yobe ta janye yajin aiki.

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta maka kamfanin NNPCL a kotu.

Gwamnan jihar Kaduna ya sauke kwamishinan yada labarai na jihar.

Gwamnan Zamfara ya bayyana kashe sama da mutum 30 da ƴanbindiga s**a yi daga cikin waɗanda s**a yi garkuwa da su a matsayin dabbanci da rashin sanin darajar ɗan'adam.

Mahara sun kashe akalla mutane biyar a Dajin Madam da ke tsakankin jihohin Bauchi da Taraba.

Ƴanbindiga da s**ayi garkuwa da ɗaliban Law School da aka sace a jihar Benue sun ce idan ba a biya kuɗin fansa ba, za ku kashe su, k**ar yadda kafar The Punch ta ruwaito.

A yanzu haka ana hasashen samun saukar mamakon ruwan sama har zuwa gobe Laraba a wasu yankuna sama da 10 na China.

Jami'ar Jihar Gombe (GSU) za ta fara daukar dalibai domin samun digiri a wasu sabbin kwasa-kwasai shida da za ta fara a fannin noma.

Rasha na son fara haƙar mak**ashin Uranium a Nijar.

Ɗan sanda da wasu uku sun mutu a harbin bindiga a birnin New York.

Ukraine ta ce Rasha ta kai hari a wani gidan yari da ke kudancin Zaporizhzhia tare da kashe aƙalla mutum 16 da raunata wasu da dama.

Ɗaruruwan 'yan Sudan da yaƙi ya ɗaiɗaita na komawa ƙasarsu daga Masar.

Wata gobarar daji mai munin gaske ta tashi a Birnin Bursa na Turkiyya, inda take ci gaba da mamaye wasu unguwanni, wanda hakan ya tilasta wa hukumomi kwashe dubban mazauna yankunan.

Shugaban ƙasar Ivory Coast Alassane Ouattara mai shekara 83, ya sanar da aniyarsa ta sake tsayawa takarar zaɓen shugaban ƙasa karo na huɗu - wanda za

Address

Airport Road
Fagge
2355

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kasar Kano Jiya Da Yau posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Kasar Kano Jiya Da Yau:

Share

Category