
23/05/2025
Labaran Juma'a 25/11/1446AH - 23/05/2025CE Ga Takaitattun Labaran.
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya caccaki masu cewa gwamnatinsa na ingiza ’yan Najeriya wajen bin tsarin jam’iyya ɗaya.
Damagun ya bugi ƙirji da cewa duk waɗanda s**a sauya sheƙa daga PDP, babu wanda zai iya fitowa ya ce jam’iyyar ta yi masa wani laifi: “Sai dai ma ta yi musu riga ta yi musu wando.”
Gwamnatin tarayya tayi karar Sanata Natasha kan laifin ‘ɓata suna’ da yin ƙazafi ga Akpabio da Yahaya Bello.
Shugaban babbar jam'iyyar, PDP, Ambasada Umar Iliya Damagun, ya musanta zargin da wasu ke yi masa cewa yana yi wa jam'iyyar, APC aiki ne shi ya sa rikicin PDP din ya ki ci ya ki cinyewa.
Ana tuhumar mutumin ake zargi da kashe ma'aikatan ofishin jakadancin Isra'ila a Amurka da laifin kisa.
An rattaba hannu kan yarjejeniyar damka wa Mauritius ikon tsibirin Chagos.
Hukumar samar da abinci ta Majalisar ɗinkin ɗuniya (WFP) ta ce fiye da ƴan gudun hijira dubu 700 a Kenya za su sami kashi 1 ne kawai bisa huɗu na abincin da suke buƙata daga wata mai zuwa saboda katse tallafi.
Gwamnatin Trump ta haramta wa jami'ar Harvard ɗaukar ɗalibai ƴan ƙasashen waje.
Manchester United ta ba da himma don ganin ta sayar da 'yan wasan ta Rashford, Jadon Sancho, da kuma Antony, a matsayin wani bangare na sake fasalin kungiyar.
Duk da rashin buga gasar cin kofin zakarun Turai, Manchester United za ta yi watsi da duk wani yunkuri na son daukar kyaftin dinta Bruno Fernandes.
Dan wasan Real Madrid Modric zai bar kungiyar a karshen kaka.
Tsohon kocin Manchester United Ten Hag zai karbi koyar da Bayern Liverkusen.